Sashe 3
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayani akayi sosai tareda gabatar musu da mutumin da ya jajurce wurin basu gudun mawa akoda yaushe, har akayi aka gama baice ko uffan ba, shugaban gidan marayun ne yayi jawabin godiya a madadin marayun tareda mika wasu tarin bukatunsu wadanda suke son gwamnati tayi musu ko kuma masu hannu da shuni,
Take awurin matashin saurayin Wanda suka sanya masa suna da baya goya marayu yabada gudun mawar naira biliyan goma, yana gama saka hannu ajikin cheque din da yabada yabude motarshi yashiga batare da yatsaya yaji karshen jawabin godiyar da jama'ar wurin keyi masa ba,
Shiru Hafsat da amina sukayi acikin zuciyoyinsu suna tambayar kansu to shi wannan wanne irin mutum ne mai alheri wanda baya bukatar godiya?.
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*6*
***Suna tsaye suna kallonshi motar tashi ta lula tabar wurin yayinda yan rakiyarsa suka yi hanzarin shiga nasu motocin suka mara masa baya,
"Mutumin nan Allah yasaka masa da alkhairi, dan haduwa ya hadu amma kuma nidai banji dadin yanda ya karbemu ba lokacin da ana gabatar masa damu.." Amina tace da Hafsat tana girgiza kanta,
"To in banda abinki amina mudai ina ruwanmu da yanda ya karbemu,mudai dama taimakonmu kawai muke so yayi kuma yana yi iya daidai gwargwadonsa sannan dama kin san masu kudi ance wulakanci garesu"
"Hakane Hafsat amma kuma ai daraja mutum ma wani abune mai muhimmanci.."
"Kedai amina korafinki kullum baya karewa, dadina dake kenan"
"To shikenan Hafsat nayi shiru.."
Amina tafada tana kokarin jan hannunta.
***
Tunda yashiga cikin lafiyayyen gidan nasa yaja burki acikin kasaitaccen falonsa na alfarma wanda za a iya kira da aljannar duniya,
Kasa zama yayi dan haka ya mike yafara yin sintiri yana kaiwa da kawowa acikin falon nasa,
Yau kwata kwata baya jin barci sannan yasan barcin ma dama bazai zo gareshi ba saboda halin da yake ciki,
Maganar mami ce ta fado masa nacewa zata kaishi domin a binciki kwakwalwarshi,
Shi dai a iya saninsa yasan lafiyarshi kalau bashida wata lalura wacce keda alaka da tabin hankali,
Haka yaci gaba da ire iren wadannan tunane tunanen har dare ya raba, saida yayi sallar asubah sannan yasamu bacci yayi awon gaba dashi,
Misalin karfe 10 daidai nasafe yatashi, wanka yayi ya shirya yafito cikin bakaken suit wadanda sukayi mutukar karbarshi domin rigar da yasaka aciki ja ce shikuma red colour tana mutukar amsarshi,
Fita yayi zuwa wurinda aka tanada musamman domin adana motoci, motocine gasu nan ajere kala daban daban tamkar wurin saida motoci,
Wata dark blue ya bude yashiga yayi mata key yafita daga gidan, kamar ya biya ta gidan mami yayi breakfast sai kawai yawuce batare da yabiya ba domin yasan idan yaje ma fadan dai da take ta yi zata dora daga inda ta tsaya,
Kamfaninshi na sarrafa takalma da jaka ya nufa domin yana da meeting da ma'aikatan company din nan yabata lokaci mai tsawo bashi ya tashi ba sai 5 na yamma dan haka agajiye ya tasamma gidan mami,
Yana tafe yana kokarin cire necktie din dake wuyanshi daf da zai shiga falo su surayya suka fito itada kawarta wacce ta Kawo mata ziyara,
"Barka da zuwa yaya.." Surayya tace dashi lokacin da saka zo daf dashi, ko kallonta baiyi ba bare ya amsa mata sannun da take yimasa,
Dayake tasan halinshi sai ko damuwa batayi ba maimakon hakama sai murmushi da tadanyi ta waiwaya lokacin har yashige cikin babban falon,
"Sury wannan kuma waye?"
Kawar tata ta tambayeta tana dafa kafadarta,
"Wallahi billy brother nane.."
"Au wai dama kinada wani brother din bayan Abdul da khalifa?"
Murmushi surayya tayi,
"Wannan shine first born namu ai sunanshi yusleem"
Kada kai billy tayi tana dan murmusawa,
"Masha Allah, amma duk yafiku kyau, inama ace zaki bani shi.."
"A'a billy bazanyi Fatan ki auri yaya yusleem ba domin daga karshe kawancenmu dake sunanshi kararre"
"Meyasa kikace haka?" Billy ta tambayeta,
"Kedai kawai mubar maganar, idan mun koma school zamu karasa, nidai bazan samu komawa next week ba sai dai upper week"
"To shikenan Allah yakaimu"
Sallama sukayi billy tatafi ita kuma surayya tashiga cikin gida, akan dining ta iske yusleem yana cin abinci,
"Yaya wallahi kayi kasuwa.."
Banza yayi mata yaci gaba da cin abincinsa, bedroom din Mami ta shiga ta fara tsegunta mata maganar kawarta billy, ahaka yusleem yasamesu,
Agefen gadon mami yazauna yadan kishingida,
"Mami maganar visa dinnan inaga kawai kufara shiri domin nanda kwana 4 zata iya zama ready.."
"Allah yakaimu, Allah yayi maka albarka yusleem.."
"Amin mami".
Cikin kwanaki hudu visa tafito suka shirya suka tafi kasar chairo, bincike sosai mami tasa ayi mata a kwakwalwar yusleem dan agano mata abinda ke damunsa, cikin kwanaki 2 likitocin suka kammala sakamako yafito...
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*7*
aishaummi.blogspot.com
***Mamaki ne ya kama mami saboda ganin sakamakon dake jikin takardar, wurin surayya taje ta mika mata bayan ta zauna agefenta,
Itama surayyan mamaki ne ya bayyana akan fuskarta ganin wai yusleem lafiyarsa kalau bashida matsalar komai,
"To yanzu mami menene mafita kuma?"
Surayya tayi tambayar tana kallon mamin,
"Surayya mujira tukunna mu koma gida sai asamo mafita"
"To Allah ya kaimu".
Satinsu biyu suka koma gida nigeria, bayan sun hutane mami tasake sakashi agaba ta koro masa jawabi kamar haka,
"Tunda munje asibiti sun tabbatar mana da cewar kwakwalwarka lafiya lau take tofa akwai sauran bincike domin yanzu kuma malamin rukiyya zan samo yazo yayi maka rukiyya ya rabaka da wannan aljanar data aureka.."
Ware ido yayi ya kalli mami,
"Rukiyya kuma mami? Ni me ya hadani da rukiyya kuma?"
"Kai kuwa keda hadi da rukiyya yusleem domin dukkan alamu sun nuna cewar kana tareda aljana..."
"Wallahi mami ni banida wata aljana, lafiyata lau.."
"Ai bazan yarda dakai ba har sai masu bincike sun bincika sun tabbatar"
Mikewa yayi yafita, tun daga nan bai sake komawa gidan ba sai ranar da surayya zata koma makaranta,
Acikin kitchen ya iske mami itada kukunta suna soya dambun kifi da nama wanda surayya zata tafi dashi makaranta,
"Mami barka da aiki.."
Kallonsa mami tayi ta dauke idonta taci gaba da aikinta,
"Sai yau zaka zo gidan? Akan ina nemamaka lafiya shine kuma zaka daina zuwa gidan nan? Yayi kyau"
Shiru yayi baice komai ba dama kuma tasan ba komai din zaice ba,
Wucewa yayi zuwa cikin falo inda surayya take zaune tanata harhada kayanta wadanda zata wuce school dasu,
"Yawwa yaya dama kai nake jira, pls ka bani kudi zan sai phone wallahi kaga wannan din ta fashe jiya ina..."
Bai bari ta karasa ba yayi saurin katseta,
"Nawa kikeso?"
"Yaya duk abinda nasamu"
"Kijira zan turo miki anjima harda kudin karatunki, inyaso idan kikaje can sai kisiya"
"Nagode yaya, Allah yabaka mata tagari"
Wata uwar tsawa ya daka mata,
"Ke....."
Saurin rufe bakinta tayi tai shiru, mami ce ta shigo tana rikeda dambun nama akan flate, yusleem ta ajiyewa agabanshi ta samu wuri ta zauna tana kallonshi,
"Gobe idan Allah yakaimu malamin da zai yimaka rukiyya zaizo zaku fara"
Baiyi maganaba illa idanuwansa da ya tsayar akan tv din dake kafe abangon falon tana aiki,
"Ko bakaji ne? Ina yimaka magana"
"Inaji.."
"Yawwa dan haka gobe da safe inganka agidan nan"
Dambun naman yaja yafara tsakura yana ci har surayya ta kammala shiryawa nan ya daukesu a motarshi itada mami ya kaisu airport, saida sukaga tashin jirginsu sannan suka dawo gida, bai shiga gidan ba ya juya ya nufi gidansa.
Washe gari kamar yadda mami tace haka ya nufi gidan, lokacin har mai yin rukiyyar yazo, tun aranar aka fara amma shiru babu alamun aljanu atare dashi,
Tsawon kwana 7 aka dauka ana gudanar da rukiyyar amma babu abinda ya canja dan haka malamin yacewa mami daga ranar angama kuma lafiyar yusleem kalau,amma bai saniba ko aljanar kin bayyana tayi,
Shiru mami tayi tai tagumi tarasa abin fada amma har lokacin zuciyarta bata amince mata da cewar yusleem baya tareda aljana ba.
Sallamar malamin mami tayi ta zubawa yusleem ido,
"Yusleem ka fada min abinda ke damunka saboda ni har yanzu jikina yana bani da akwai wani abu"
"Mami babu abinda yake damuna"
"Da akwai yusleem, akwai abinda yake damunka, kafada min gaskiya idan baka da lafiya a matsayinka na d'a namiji?"
Dan sunkuyar da kai yayi yasoma shafa sumar kanshi saboda nauyin da maganar ta mami tayi mishi,
"Mami nifa banida kowacce irin matsala wallahi lafiyata lau"
"To shikenan tunda kafadi haka amma ina son daga yau dinnan kafara duba matar aure domin agaskiya bazan juri ganinka ahaka babu mata ba"
Kallonta yayi amma sai yayi shiru baiyi magana ba domin shi ba kasafai ya fiya son yayita magana ba, nasiha mami tashiga yimasa sai da tayi tagama sannan yatashi ya fita,
Tun daga ranar mami tashiga nemar masa matar aure domin acewarta bata son ganinshi haka babu aure,shikuma tasan ba samowa zaiyi dakanshi ba ko tabashi dama tunda abaya tasha gwada irin hakan amma abun ya faskara.
Cikin sa'a aka samo mata wata yarinya mai hankali Nusaiba yarinyar bazata wuce shekaru 20 ba domin ko jami'a bata shiga ba, duk da iyayenta sunji labarin irin auri sakin da yusleem yakeyi hakan bai sasu yunkurin hanashi aurenta ba domin suna ganin kamar wannan wata damace da suka samu wadda zasu dandani zakin arziki.
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*8*
aishaummi.blogspot.com
***Tamkar zaiyi kuka yasa mami agaba yana rokonta akan ta janye maganar auren nan domin bashida burin sake yin aure nan kusa,
"Mami tunda dai sakin nan da nakeyi bakya so, shi yafi komai daga miki hankali to kiyi hakuri kibar maganar auren nan domin bana bukatarsa.."
"Kai ka isama? Ai ko bakaso sai nayi maka wannan auren domin cikar kimarka shine aganka da iyali, haba yusleem wacce irin rayuwa kake son yi ne? Haka kake so inzuba maka ido ka zauna babu mata atare dakai? Ina abinda bazai yuyu ba kenan.."
Bai sake cewa komai ba yaciro wayarshi dake cikin aljihun wandonshi yafara latsawa,
Take awurin matashin saurayin Wanda suka sanya masa suna da baya goya marayu yabada gudun mawar naira biliyan goma, yana gama saka hannu ajikin cheque din da yabada yabude motarshi yashiga batare da yatsaya yaji karshen jawabin godiyar da jama'ar wurin keyi masa ba,
Shiru Hafsat da amina sukayi acikin zuciyoyinsu suna tambayar kansu to shi wannan wanne irin mutum ne mai alheri wanda baya bukatar godiya?.
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*6*
***Suna tsaye suna kallonshi motar tashi ta lula tabar wurin yayinda yan rakiyarsa suka yi hanzarin shiga nasu motocin suka mara masa baya,
"Mutumin nan Allah yasaka masa da alkhairi, dan haduwa ya hadu amma kuma nidai banji dadin yanda ya karbemu ba lokacin da ana gabatar masa damu.." Amina tace da Hafsat tana girgiza kanta,
"To in banda abinki amina mudai ina ruwanmu da yanda ya karbemu,mudai dama taimakonmu kawai muke so yayi kuma yana yi iya daidai gwargwadonsa sannan dama kin san masu kudi ance wulakanci garesu"
"Hakane Hafsat amma kuma ai daraja mutum ma wani abune mai muhimmanci.."
"Kedai amina korafinki kullum baya karewa, dadina dake kenan"
"To shikenan Hafsat nayi shiru.."
Amina tafada tana kokarin jan hannunta.
***
Tunda yashiga cikin lafiyayyen gidan nasa yaja burki acikin kasaitaccen falonsa na alfarma wanda za a iya kira da aljannar duniya,
Kasa zama yayi dan haka ya mike yafara yin sintiri yana kaiwa da kawowa acikin falon nasa,
Yau kwata kwata baya jin barci sannan yasan barcin ma dama bazai zo gareshi ba saboda halin da yake ciki,
Maganar mami ce ta fado masa nacewa zata kaishi domin a binciki kwakwalwarshi,
Shi dai a iya saninsa yasan lafiyarshi kalau bashida wata lalura wacce keda alaka da tabin hankali,
Haka yaci gaba da ire iren wadannan tunane tunanen har dare ya raba, saida yayi sallar asubah sannan yasamu bacci yayi awon gaba dashi,
Misalin karfe 10 daidai nasafe yatashi, wanka yayi ya shirya yafito cikin bakaken suit wadanda sukayi mutukar karbarshi domin rigar da yasaka aciki ja ce shikuma red colour tana mutukar amsarshi,
Fita yayi zuwa wurinda aka tanada musamman domin adana motoci, motocine gasu nan ajere kala daban daban tamkar wurin saida motoci,
Wata dark blue ya bude yashiga yayi mata key yafita daga gidan, kamar ya biya ta gidan mami yayi breakfast sai kawai yawuce batare da yabiya ba domin yasan idan yaje ma fadan dai da take ta yi zata dora daga inda ta tsaya,
Kamfaninshi na sarrafa takalma da jaka ya nufa domin yana da meeting da ma'aikatan company din nan yabata lokaci mai tsawo bashi ya tashi ba sai 5 na yamma dan haka agajiye ya tasamma gidan mami,
Yana tafe yana kokarin cire necktie din dake wuyanshi daf da zai shiga falo su surayya suka fito itada kawarta wacce ta Kawo mata ziyara,
"Barka da zuwa yaya.." Surayya tace dashi lokacin da saka zo daf dashi, ko kallonta baiyi ba bare ya amsa mata sannun da take yimasa,
Dayake tasan halinshi sai ko damuwa batayi ba maimakon hakama sai murmushi da tadanyi ta waiwaya lokacin har yashige cikin babban falon,
"Sury wannan kuma waye?"
Kawar tata ta tambayeta tana dafa kafadarta,
"Wallahi billy brother nane.."
"Au wai dama kinada wani brother din bayan Abdul da khalifa?"
Murmushi surayya tayi,
"Wannan shine first born namu ai sunanshi yusleem"
Kada kai billy tayi tana dan murmusawa,
"Masha Allah, amma duk yafiku kyau, inama ace zaki bani shi.."
"A'a billy bazanyi Fatan ki auri yaya yusleem ba domin daga karshe kawancenmu dake sunanshi kararre"
"Meyasa kikace haka?" Billy ta tambayeta,
"Kedai kawai mubar maganar, idan mun koma school zamu karasa, nidai bazan samu komawa next week ba sai dai upper week"
"To shikenan Allah yakaimu"
Sallama sukayi billy tatafi ita kuma surayya tashiga cikin gida, akan dining ta iske yusleem yana cin abinci,
"Yaya wallahi kayi kasuwa.."
Banza yayi mata yaci gaba da cin abincinsa, bedroom din Mami ta shiga ta fara tsegunta mata maganar kawarta billy, ahaka yusleem yasamesu,
Agefen gadon mami yazauna yadan kishingida,
"Mami maganar visa dinnan inaga kawai kufara shiri domin nanda kwana 4 zata iya zama ready.."
"Allah yakaimu, Allah yayi maka albarka yusleem.."
"Amin mami".
Cikin kwanaki hudu visa tafito suka shirya suka tafi kasar chairo, bincike sosai mami tasa ayi mata a kwakwalwar yusleem dan agano mata abinda ke damunsa, cikin kwanaki 2 likitocin suka kammala sakamako yafito...
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*7*
aishaummi.blogspot.com
***Mamaki ne ya kama mami saboda ganin sakamakon dake jikin takardar, wurin surayya taje ta mika mata bayan ta zauna agefenta,
Itama surayyan mamaki ne ya bayyana akan fuskarta ganin wai yusleem lafiyarsa kalau bashida matsalar komai,
"To yanzu mami menene mafita kuma?"
Surayya tayi tambayar tana kallon mamin,
"Surayya mujira tukunna mu koma gida sai asamo mafita"
"To Allah ya kaimu".
Satinsu biyu suka koma gida nigeria, bayan sun hutane mami tasake sakashi agaba ta koro masa jawabi kamar haka,
"Tunda munje asibiti sun tabbatar mana da cewar kwakwalwarka lafiya lau take tofa akwai sauran bincike domin yanzu kuma malamin rukiyya zan samo yazo yayi maka rukiyya ya rabaka da wannan aljanar data aureka.."
Ware ido yayi ya kalli mami,
"Rukiyya kuma mami? Ni me ya hadani da rukiyya kuma?"
"Kai kuwa keda hadi da rukiyya yusleem domin dukkan alamu sun nuna cewar kana tareda aljana..."
"Wallahi mami ni banida wata aljana, lafiyata lau.."
"Ai bazan yarda dakai ba har sai masu bincike sun bincika sun tabbatar"
Mikewa yayi yafita, tun daga nan bai sake komawa gidan ba sai ranar da surayya zata koma makaranta,
Acikin kitchen ya iske mami itada kukunta suna soya dambun kifi da nama wanda surayya zata tafi dashi makaranta,
"Mami barka da aiki.."
Kallonsa mami tayi ta dauke idonta taci gaba da aikinta,
"Sai yau zaka zo gidan? Akan ina nemamaka lafiya shine kuma zaka daina zuwa gidan nan? Yayi kyau"
Shiru yayi baice komai ba dama kuma tasan ba komai din zaice ba,
Wucewa yayi zuwa cikin falo inda surayya take zaune tanata harhada kayanta wadanda zata wuce school dasu,
"Yawwa yaya dama kai nake jira, pls ka bani kudi zan sai phone wallahi kaga wannan din ta fashe jiya ina..."
Bai bari ta karasa ba yayi saurin katseta,
"Nawa kikeso?"
"Yaya duk abinda nasamu"
"Kijira zan turo miki anjima harda kudin karatunki, inyaso idan kikaje can sai kisiya"
"Nagode yaya, Allah yabaka mata tagari"
Wata uwar tsawa ya daka mata,
"Ke....."
Saurin rufe bakinta tayi tai shiru, mami ce ta shigo tana rikeda dambun nama akan flate, yusleem ta ajiyewa agabanshi ta samu wuri ta zauna tana kallonshi,
"Gobe idan Allah yakaimu malamin da zai yimaka rukiyya zaizo zaku fara"
Baiyi maganaba illa idanuwansa da ya tsayar akan tv din dake kafe abangon falon tana aiki,
"Ko bakaji ne? Ina yimaka magana"
"Inaji.."
"Yawwa dan haka gobe da safe inganka agidan nan"
Dambun naman yaja yafara tsakura yana ci har surayya ta kammala shiryawa nan ya daukesu a motarshi itada mami ya kaisu airport, saida sukaga tashin jirginsu sannan suka dawo gida, bai shiga gidan ba ya juya ya nufi gidansa.
Washe gari kamar yadda mami tace haka ya nufi gidan, lokacin har mai yin rukiyyar yazo, tun aranar aka fara amma shiru babu alamun aljanu atare dashi,
Tsawon kwana 7 aka dauka ana gudanar da rukiyyar amma babu abinda ya canja dan haka malamin yacewa mami daga ranar angama kuma lafiyar yusleem kalau,amma bai saniba ko aljanar kin bayyana tayi,
Shiru mami tayi tai tagumi tarasa abin fada amma har lokacin zuciyarta bata amince mata da cewar yusleem baya tareda aljana ba.
Sallamar malamin mami tayi ta zubawa yusleem ido,
"Yusleem ka fada min abinda ke damunka saboda ni har yanzu jikina yana bani da akwai wani abu"
"Mami babu abinda yake damuna"
"Da akwai yusleem, akwai abinda yake damunka, kafada min gaskiya idan baka da lafiya a matsayinka na d'a namiji?"
Dan sunkuyar da kai yayi yasoma shafa sumar kanshi saboda nauyin da maganar ta mami tayi mishi,
"Mami nifa banida kowacce irin matsala wallahi lafiyata lau"
"To shikenan tunda kafadi haka amma ina son daga yau dinnan kafara duba matar aure domin agaskiya bazan juri ganinka ahaka babu mata ba"
Kallonta yayi amma sai yayi shiru baiyi magana ba domin shi ba kasafai ya fiya son yayita magana ba, nasiha mami tashiga yimasa sai da tayi tagama sannan yatashi ya fita,
Tun daga ranar mami tashiga nemar masa matar aure domin acewarta bata son ganinshi haka babu aure,shikuma tasan ba samowa zaiyi dakanshi ba ko tabashi dama tunda abaya tasha gwada irin hakan amma abun ya faskara.
Cikin sa'a aka samo mata wata yarinya mai hankali Nusaiba yarinyar bazata wuce shekaru 20 ba domin ko jami'a bata shiga ba, duk da iyayenta sunji labarin irin auri sakin da yusleem yakeyi hakan bai sasu yunkurin hanashi aurenta ba domin suna ganin kamar wannan wata damace da suka samu wadda zasu dandani zakin arziki.
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*8*
aishaummi.blogspot.com
***Tamkar zaiyi kuka yasa mami agaba yana rokonta akan ta janye maganar auren nan domin bashida burin sake yin aure nan kusa,
"Mami tunda dai sakin nan da nakeyi bakya so, shi yafi komai daga miki hankali to kiyi hakuri kibar maganar auren nan domin bana bukatarsa.."
"Kai ka isama? Ai ko bakaso sai nayi maka wannan auren domin cikar kimarka shine aganka da iyali, haba yusleem wacce irin rayuwa kake son yi ne? Haka kake so inzuba maka ido ka zauna babu mata atare dakai? Ina abinda bazai yuyu ba kenan.."
Bai sake cewa komai ba yaciro wayarshi dake cikin aljihun wandonshi yafara latsawa,