Sashe 29
Ahalinmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fuskar nan ta Sulaim ɗaure tamau tamkar shine Yariman tun kafin su ƙarasa aka sanar wa da sarki zuwan Yarima Sultan magajin karaga,
Sanda suka isa har anfito zaman fada duk wani mai ruƙe da muƙami yana zaune aciki kama daga kan Waziri, Galadima, Hakimi, Liman, da sauran masu karaga,
Kai tsaye suka nufi wajan da mai martaba yake zaune kan karagar sa ta mulki fadawan yarima Sultan ne suka farayi mishi kirare da kambamawa ahankali suka rage tsaye tare da russunawa cikin tsananin Girmamawa,
Sarki yayi murmushi yana amsa gaisuwar da suke yi mishi tare da miƙawa Sulaim hannu alamar suyi musabaha,
Sosai Sulaim ya ƙara yin ƙasa da kanshi cikin girmamawa batare da yamiƙa hannun ba fadawa ne suka amsa da cewa Sarki ya gaishe da ɓaƙon masarautar Gabas kuma amini ga sarkin gobe Yarima sultan ZAKI Dan sarki jikan sarki,
Miƙawa Yarima sultan hannu sarki yayi alamar su gaisa,
Take Yarima sultan ya cire hular kanshi don ne man albarkar mai martaba kamar yadda suka saba duk sanda yazo haka ce take faruwa,
Fadawan sarki ne suka ƙara fadin sarki ya gaishe da sarkin wata rana a masarautar GABAS, Sarki ya amshi gaisuwar Yarima Sultan,
Mai martaba ya kalli muskar Sulaim tare da jin daɗin yadda yaga tsananin girmamawa daga yaron hakan ya burgeshi duk da ba yau yasan Sulaim din ba amma shi komai yaron yayi yana masa daɗi a rai duk da mulki baya bari ya bayyana,
Duka hannuwan sa biyun yasa tare da ɗago da su daga duƙushan da suke tare da yi musu alamar su zauna zama sukai sosai sai a lokacin yarima ya maida hular kanshi tare da daidai ta zaman ta akan nashi,
Saida suka zauna sosai sannan Sulaim yafara magana,
Baffa yana gaishe ka, yace a miƙo sakon bangirma ga zakin sarki da samun kamar sa sai an tona,
Kamar yadda baffan yabashi sakon haka yakawo shi bai rage komai ba aciki,
Murmushin girma sarki yayi dayake yasan baffa sosai abokin shine duk da baffan ya girmeshi, kasancewar babu wanda yaji abunda Sulaim yace hakan yasa babu ba Fadan da ya tofa albarkacin bakin shi bare su ari bakin sarki suci masa albasa,
Nagode sosai Aminin Sultan, kafaɗawa alhaji Imran Arab sarki ya amsa kuma yana miƙo gaisuwa ga dattijon arziƙi,
Take sarki ya basu umarnin Gaisawa da sauran mutanan fada
Gaisawa yarima Sultan yayi da su cikin girma mawa saboda duk manyane akan shi,
Shima Sulaim haka amma duka sauran ƴaƴan sarkin miƙa musu hannu yayi suka gaisa hakan baƙaramin ɓata musu rai yayi ba bama kamar Yarima Safwan yaji baƙin cikin ganin mai martaba ya sakar wa Sulaim fuska har suka yi magana,
Sannan shi Indai kai ba ɗan mulki bane baka isa yamiƙa maka hannu ba amma gashi yau yayi da Sulaim cikin ƙunar rai ya tashi ya bar Fada batare da mai maitaba ya kula ba,
Bayan sungama Gaisawa da kowa Yarima Sultan ya matsa kuwa da sarki sosai tare da fadin
Allah yaqara Maka yawan nasara muza mukoma
Allah ya albarkaci rayuwar ku zaku iya tafiya,
Munbarku lafiya baba cewar Sulaim tunkafin ya tashi ,
Fadawan Sultan ne suka rufa musu baya Suka nufi Layi Sashen UMMUL BAIT tare da sheda mata isowar su ummeethar,
Bayan sun gaisa Yarima Sultan yasanar mata da isowar tasu tare da sheda mata har antafi airport dakko su,
Sosai taji Dadi tasan ko badon da wowar Dan ta suka zoba Amma dai sun zo din Hakan baqaramin Dadi yayi mata ba,
Umarnin zuwa gaida Fulanin sarki UMMUL BAIT taba su Dan tasan Indai bahakan tayiba Sultan bazai taba cewa suje can din ba,
Aiko Hakan ce takasan ce badon Yarima yaso ba haka ya amsa mata da to cike da tsantsar girmamawa saboda Basu San meye musu da gardama ba biyayya kawai su tashi sukaga anayi ga na gaba dakai,
Suntashi da niyar tafiya saga qannan Yarima Sultan Nan su uku da fuskokin su dauke da kyayataccan murmushu su qarasu ganin su yasa Yarima Sultan komawa saman kujera ya zauna Shima Sulaim din haka,
Saida suka fara gaida UMMUL BAIT kana suka juya gurin su Sulaim,
Har lokacin murmushi ne bisa fuskokin su Hakan ya faru ne sana diyar ganin Sulaim da sukai duk da Basu Wani saba dashi sosai ba Amma dai suna son ganin shi yazo,
HAISAM, Shine kebin Yarima Sultan sai Kuma TASLEEM, da TASLEEMA, Yan biyu ne *(twins)* sune mata suke bin HAISAM Kuma sune auta A gurin UMMUL BAIT
Hannu Haisam yami qawa Sulaim tare da fadin Yaya Sulaim barka da zuwa masarautar GABAS,
Murmushi Sulaim yayi tare da miqamasa hannu suka gaisa tare da furta fatan kana lafiya,
Alhamdulillah yafada Yana janye hannuna sa,
Kusan atare Tasleem da Tasleema suka furta barka da zuwa Yaya Sulaim Allah yasa ka iso cikin ameenci,
Alhamdulillah Allah yasa Kuma Kuna cikin ameencin,
Tasleema ta furta mungode ma allah,
Kallon su Sulaim yayi yace Am kice sai Kuma yayi shiru,
Da sauri Tasleem tace eh nice Tasleem Ita Kuma Tasleema,
Wani kyataccan murmushi Sulaim yayi ba tare da yace komai ba yadda Tasleem din tayi ne yabashi dariya
Shi baya hira da kowa baima iya ba idan kaga yayi doguwar magana to da Yarima Sultan ne da baffa sai Kuma Saleem sai aunty raziqa itama Kuma takuramasa take,
Aransa yace ko Tayaya suke iya Gane yaran Nan komai nasu iri daya tamkar RAFIQ da TAUFIQ Yan uwansa kenan Suma twins ne,
Salma sukayi da su da sannan suka qarayiwa UMMUL BAIT sallama suka fita,
Fulani na zaune aka sanar mata da shigowar Yarima Sultan Layin sashanta Gaisawa sukai Babu yabo ba fallasa suna cikin Gaisawa Siyama tashigo sai Wani faman iyayi take da Yan ga daga bangaran da Yarima yake anan ta zauna tagaishe su batare da daya daga cikin su ya kalli ko inda take ba haka dahaka suka bar parlourn,
Wannan abun baqara min ciwo yayiwa Siyama ba Fulani ko ba a magana daga Kai kawai tayi tare da yin kwafa dama tana Jin haushin tunda yadawo sau daya yaje gaida ta,
🦋🦋🦋
Manya manyan motocine guda 4 launin baƙi kowacce da tambarin masarautar GABAS ajiki wato ZAKI *(SHAREEF EMIRATE)* agaban motocin aga rubuta,
Yarima Sultan ne ya turo a dakko su ummeethar yahado hadda sarkin mota saboda abasu tsaro sosai su iso cikin iKon Allah da aminci,
Saleem yaso ace mota daya suka shiga da Suhailat Amma Ina Hakan Bai samuba sai mommy tace yashiga motar da su Rafiq da taufiq suka shiga baji dadin Hakan ba,
Yaso ko a gidan gaba ne ya zauna aqalla ko Babu komai zagan ta tacinkin glass din motar tunda daga Ita sai Saleema ne a motar,
Haka suka dauki hanya Amma yasa aransa duk yadda za ai sai ya ga Suhailat kodan suyi magana saboda a jirgi yaga ko kyakkyawan motsi batayi saboda kada su hada ido duk ya lura da ita a takure take,
Kaitsaye suka sauka a gidan baba waziri sun samu tarba Mai kyau tare da abinci kala kala abinci na musamman UMMUL BAIT ta aiko musu dashi daga ban garan ta tare da aiko Jakadiyar ta da sakon barka da isowa zuwa ga su ummeethar,
Bayan sun ci sunsha daga nau'in abinci kala kala da abin Sha kowa ya kama masaukin sa sun huta sosai wasu daga cikin su har sunyi wanka,
Suhailat kuwa ko fitowa batayi daga masaukin suba da aka Basu Ita da Saleema tunda suka gama cin abinci tashiga tayi wanka Bata fito ba
Princess kuwa jira kawai take sufita tafara yawo acikin masarautar don tana qaunar tsarin masarauta,
mommy tace wai nikam banga kalbiy na ba haryan zu Wani irin Dadi Saleema taji Wanda dama gabtake da tambayar Sulaim din sai mommyn su tariga ta,
Saleem Wanda hankalin sa nakan hanyar idan da Suhailat tabi Yana jiran ganin fitowar ta,
Yace mommy gashinan zuwa nayi magana dashi yanzu,
Saleema jitayi tamkar ta daka tsalle don murnar jin Sulaim yana hanyar zuwa don ita ba don shiba da bazata zoba,
Hattara dai ga zaki dan dan zaki dan gado yafi dan na koya Allah ya temaki Yarima Sultan sarkin gobe A masarautar Gabas da yadda Allah gafarai Yarima zai shigo,
Muryar jakadiya ce takara ɗe kunnuwan su ummeetha kafin kowa yayi wani kwakwaran motsi Yarima Sultan da Sulaim sun shiga Parlourn cikin wata sabuwar shigar wadda tafi ta ɗazun kyau,
Fadawansa dake biye dasu suka ja suka tsaya a ƙofar shiga babban parlourn baba waziri na saukar baƙi,
Kai tsaye Yarima Sultan ya wuce inda ummeethar ke zaune tana murmushin ganin su,
Russuna wa yayi sosai agaban ta cikin girmamawa ya furta inayiwa Mahaifiya ta barka da zuwa Masarautar Gabas Allah yasa Ummeethar ta iso cikin aminci Allah yasa Mahaifiya ta ta samu kyakkyawar tarba acikin wannan masarauta cikin nutsuwa Yarima sultan ya faɗi waɗan nan kalaman,
Sosai ummeethar taji daɗi cikin fara'a tace ɗana Sultan kuma Yariman Masarautar mu barka da Warhaka ina fatan Yarima yana lafiya,
Alhamdulillah ya furta hakan batare da ya ɗagoba,
Zauna sosai kaji ɗaya
Babu musu yarima sultan Ya zauna shi ko Sulaim gurin mommy yafara zuwa ta rungume shi suka gaisa sosai,
Sannan ya rungume Saleem tare da Faɗin soja mazan fama barka da isowa,
Murmushi Saleem yayi tare da fadin mun sameku lafiya
Alhamdulillah"
Komawa gefe Saleem yayi dan baya cikin hayyacin sa hayaniyar tana kara dagula masa lissafi,
Lallai idan har haka so yake to ya shammace ni ya shigeni lokacin da banshirya ɗaukar matsalolin sa ba but why Suhailat?
Saleem ne ke faman surutan shi a zuciya shikaɗai tare da fito da wayar sa yafara rubuta wa Suhailat saƙo kamar haka
_......Ina son ganin ki yanzu saboda muyi magana ina mai baki hak'uri bisa furta kalmar so agareki hakan ya faru ne batare da nima na shirya ba amma komai ya wuce, still what I know is that I love you Suhailat but for you to love me is not by force, just relax and live your life like everyone oky but one day if you see me with someone else I hope you understood_
Sanda suka isa har anfito zaman fada duk wani mai ruƙe da muƙami yana zaune aciki kama daga kan Waziri, Galadima, Hakimi, Liman, da sauran masu karaga,
Kai tsaye suka nufi wajan da mai martaba yake zaune kan karagar sa ta mulki fadawan yarima Sultan ne suka farayi mishi kirare da kambamawa ahankali suka rage tsaye tare da russunawa cikin tsananin Girmamawa,
Sarki yayi murmushi yana amsa gaisuwar da suke yi mishi tare da miƙawa Sulaim hannu alamar suyi musabaha,
Sosai Sulaim ya ƙara yin ƙasa da kanshi cikin girmamawa batare da yamiƙa hannun ba fadawa ne suka amsa da cewa Sarki ya gaishe da ɓaƙon masarautar Gabas kuma amini ga sarkin gobe Yarima sultan ZAKI Dan sarki jikan sarki,
Miƙawa Yarima sultan hannu sarki yayi alamar su gaisa,
Take Yarima sultan ya cire hular kanshi don ne man albarkar mai martaba kamar yadda suka saba duk sanda yazo haka ce take faruwa,
Fadawan sarki ne suka ƙara fadin sarki ya gaishe da sarkin wata rana a masarautar GABAS, Sarki ya amshi gaisuwar Yarima Sultan,
Mai martaba ya kalli muskar Sulaim tare da jin daɗin yadda yaga tsananin girmamawa daga yaron hakan ya burgeshi duk da ba yau yasan Sulaim din ba amma shi komai yaron yayi yana masa daɗi a rai duk da mulki baya bari ya bayyana,
Duka hannuwan sa biyun yasa tare da ɗago da su daga duƙushan da suke tare da yi musu alamar su zauna zama sukai sosai sai a lokacin yarima ya maida hular kanshi tare da daidai ta zaman ta akan nashi,
Saida suka zauna sosai sannan Sulaim yafara magana,
Baffa yana gaishe ka, yace a miƙo sakon bangirma ga zakin sarki da samun kamar sa sai an tona,
Kamar yadda baffan yabashi sakon haka yakawo shi bai rage komai ba aciki,
Murmushin girma sarki yayi dayake yasan baffa sosai abokin shine duk da baffan ya girmeshi, kasancewar babu wanda yaji abunda Sulaim yace hakan yasa babu ba Fadan da ya tofa albarkacin bakin shi bare su ari bakin sarki suci masa albasa,
Nagode sosai Aminin Sultan, kafaɗawa alhaji Imran Arab sarki ya amsa kuma yana miƙo gaisuwa ga dattijon arziƙi,
Take sarki ya basu umarnin Gaisawa da sauran mutanan fada
Gaisawa yarima Sultan yayi da su cikin girma mawa saboda duk manyane akan shi,
Shima Sulaim haka amma duka sauran ƴaƴan sarkin miƙa musu hannu yayi suka gaisa hakan baƙaramin ɓata musu rai yayi ba bama kamar Yarima Safwan yaji baƙin cikin ganin mai martaba ya sakar wa Sulaim fuska har suka yi magana,
Sannan shi Indai kai ba ɗan mulki bane baka isa yamiƙa maka hannu ba amma gashi yau yayi da Sulaim cikin ƙunar rai ya tashi ya bar Fada batare da mai maitaba ya kula ba,
Bayan sungama Gaisawa da kowa Yarima Sultan ya matsa kuwa da sarki sosai tare da fadin
Allah yaqara Maka yawan nasara muza mukoma
Allah ya albarkaci rayuwar ku zaku iya tafiya,
Munbarku lafiya baba cewar Sulaim tunkafin ya tashi ,
Fadawan Sultan ne suka rufa musu baya Suka nufi Layi Sashen UMMUL BAIT tare da sheda mata isowar su ummeethar,
Bayan sun gaisa Yarima Sultan yasanar mata da isowar tasu tare da sheda mata har antafi airport dakko su,
Sosai taji Dadi tasan ko badon da wowar Dan ta suka zoba Amma dai sun zo din Hakan baqaramin Dadi yayi mata ba,
Umarnin zuwa gaida Fulanin sarki UMMUL BAIT taba su Dan tasan Indai bahakan tayiba Sultan bazai taba cewa suje can din ba,
Aiko Hakan ce takasan ce badon Yarima yaso ba haka ya amsa mata da to cike da tsantsar girmamawa saboda Basu San meye musu da gardama ba biyayya kawai su tashi sukaga anayi ga na gaba dakai,
Suntashi da niyar tafiya saga qannan Yarima Sultan Nan su uku da fuskokin su dauke da kyayataccan murmushu su qarasu ganin su yasa Yarima Sultan komawa saman kujera ya zauna Shima Sulaim din haka,
Saida suka fara gaida UMMUL BAIT kana suka juya gurin su Sulaim,
Har lokacin murmushi ne bisa fuskokin su Hakan ya faru ne sana diyar ganin Sulaim da sukai duk da Basu Wani saba dashi sosai ba Amma dai suna son ganin shi yazo,
HAISAM, Shine kebin Yarima Sultan sai Kuma TASLEEM, da TASLEEMA, Yan biyu ne *(twins)* sune mata suke bin HAISAM Kuma sune auta A gurin UMMUL BAIT
Hannu Haisam yami qawa Sulaim tare da fadin Yaya Sulaim barka da zuwa masarautar GABAS,
Murmushi Sulaim yayi tare da miqamasa hannu suka gaisa tare da furta fatan kana lafiya,
Alhamdulillah yafada Yana janye hannuna sa,
Kusan atare Tasleem da Tasleema suka furta barka da zuwa Yaya Sulaim Allah yasa ka iso cikin ameenci,
Alhamdulillah Allah yasa Kuma Kuna cikin ameencin,
Tasleema ta furta mungode ma allah,
Kallon su Sulaim yayi yace Am kice sai Kuma yayi shiru,
Da sauri Tasleem tace eh nice Tasleem Ita Kuma Tasleema,
Wani kyataccan murmushi Sulaim yayi ba tare da yace komai ba yadda Tasleem din tayi ne yabashi dariya
Shi baya hira da kowa baima iya ba idan kaga yayi doguwar magana to da Yarima Sultan ne da baffa sai Kuma Saleem sai aunty raziqa itama Kuma takuramasa take,
Aransa yace ko Tayaya suke iya Gane yaran Nan komai nasu iri daya tamkar RAFIQ da TAUFIQ Yan uwansa kenan Suma twins ne,
Salma sukayi da su da sannan suka qarayiwa UMMUL BAIT sallama suka fita,
Fulani na zaune aka sanar mata da shigowar Yarima Sultan Layin sashanta Gaisawa sukai Babu yabo ba fallasa suna cikin Gaisawa Siyama tashigo sai Wani faman iyayi take da Yan ga daga bangaran da Yarima yake anan ta zauna tagaishe su batare da daya daga cikin su ya kalli ko inda take ba haka dahaka suka bar parlourn,
Wannan abun baqara min ciwo yayiwa Siyama ba Fulani ko ba a magana daga Kai kawai tayi tare da yin kwafa dama tana Jin haushin tunda yadawo sau daya yaje gaida ta,
🦋🦋🦋
Manya manyan motocine guda 4 launin baƙi kowacce da tambarin masarautar GABAS ajiki wato ZAKI *(SHAREEF EMIRATE)* agaban motocin aga rubuta,
Yarima Sultan ne ya turo a dakko su ummeethar yahado hadda sarkin mota saboda abasu tsaro sosai su iso cikin iKon Allah da aminci,
Saleem yaso ace mota daya suka shiga da Suhailat Amma Ina Hakan Bai samuba sai mommy tace yashiga motar da su Rafiq da taufiq suka shiga baji dadin Hakan ba,
Yaso ko a gidan gaba ne ya zauna aqalla ko Babu komai zagan ta tacinkin glass din motar tunda daga Ita sai Saleema ne a motar,
Haka suka dauki hanya Amma yasa aransa duk yadda za ai sai ya ga Suhailat kodan suyi magana saboda a jirgi yaga ko kyakkyawan motsi batayi saboda kada su hada ido duk ya lura da ita a takure take,
Kaitsaye suka sauka a gidan baba waziri sun samu tarba Mai kyau tare da abinci kala kala abinci na musamman UMMUL BAIT ta aiko musu dashi daga ban garan ta tare da aiko Jakadiyar ta da sakon barka da isowa zuwa ga su ummeethar,
Bayan sun ci sunsha daga nau'in abinci kala kala da abin Sha kowa ya kama masaukin sa sun huta sosai wasu daga cikin su har sunyi wanka,
Suhailat kuwa ko fitowa batayi daga masaukin suba da aka Basu Ita da Saleema tunda suka gama cin abinci tashiga tayi wanka Bata fito ba
Princess kuwa jira kawai take sufita tafara yawo acikin masarautar don tana qaunar tsarin masarauta,
mommy tace wai nikam banga kalbiy na ba haryan zu Wani irin Dadi Saleema taji Wanda dama gabtake da tambayar Sulaim din sai mommyn su tariga ta,
Saleem Wanda hankalin sa nakan hanyar idan da Suhailat tabi Yana jiran ganin fitowar ta,
Yace mommy gashinan zuwa nayi magana dashi yanzu,
Saleema jitayi tamkar ta daka tsalle don murnar jin Sulaim yana hanyar zuwa don ita ba don shiba da bazata zoba,
Hattara dai ga zaki dan dan zaki dan gado yafi dan na koya Allah ya temaki Yarima Sultan sarkin gobe A masarautar Gabas da yadda Allah gafarai Yarima zai shigo,
Muryar jakadiya ce takara ɗe kunnuwan su ummeetha kafin kowa yayi wani kwakwaran motsi Yarima Sultan da Sulaim sun shiga Parlourn cikin wata sabuwar shigar wadda tafi ta ɗazun kyau,
Fadawansa dake biye dasu suka ja suka tsaya a ƙofar shiga babban parlourn baba waziri na saukar baƙi,
Kai tsaye Yarima Sultan ya wuce inda ummeethar ke zaune tana murmushin ganin su,
Russuna wa yayi sosai agaban ta cikin girmamawa ya furta inayiwa Mahaifiya ta barka da zuwa Masarautar Gabas Allah yasa Ummeethar ta iso cikin aminci Allah yasa Mahaifiya ta ta samu kyakkyawar tarba acikin wannan masarauta cikin nutsuwa Yarima sultan ya faɗi waɗan nan kalaman,
Sosai ummeethar taji daɗi cikin fara'a tace ɗana Sultan kuma Yariman Masarautar mu barka da Warhaka ina fatan Yarima yana lafiya,
Alhamdulillah ya furta hakan batare da ya ɗagoba,
Zauna sosai kaji ɗaya
Babu musu yarima sultan Ya zauna shi ko Sulaim gurin mommy yafara zuwa ta rungume shi suka gaisa sosai,
Sannan ya rungume Saleem tare da Faɗin soja mazan fama barka da isowa,
Murmushi Saleem yayi tare da fadin mun sameku lafiya
Alhamdulillah"
Komawa gefe Saleem yayi dan baya cikin hayyacin sa hayaniyar tana kara dagula masa lissafi,
Lallai idan har haka so yake to ya shammace ni ya shigeni lokacin da banshirya ɗaukar matsalolin sa ba but why Suhailat?
Saleem ne ke faman surutan shi a zuciya shikaɗai tare da fito da wayar sa yafara rubuta wa Suhailat saƙo kamar haka
_......Ina son ganin ki yanzu saboda muyi magana ina mai baki hak'uri bisa furta kalmar so agareki hakan ya faru ne batare da nima na shirya ba amma komai ya wuce, still what I know is that I love you Suhailat but for you to love me is not by force, just relax and live your life like everyone oky but one day if you see me with someone else I hope you understood_