← Book details Ahalinmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 37

Sashe 15

Ahalinmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hhmm kawai suhaima tace don, gani take tsanar datakeyiwa hajiya fanteka ko kwatanta khaltum batayi mata ita da bata san komai akan fanteka ɗin ba,

Da sallama aka turo ɗakin da suke ciki, amsawa suka yi tare da kai kallon su bakin ƙofar, wata nurse ɗin ce hannun ta riƙe da wani tire ɗin magunguna ne aciki, ƙarasuwa tayi tare da yiwa khaltum ɗin sannu,
Sannan ta bata magungunan da zata sha,

Ta kalli suhaima tace ki kuma kibiyo ni

Tashi suhaima tayi khaltum ta ruƙe mata hannu gam, kallon ta suhaima tayi girgiza mata kai khaltum ɗin tayi alamun kada ta tafi,

Janye wa tayi, tace yanzun zandawo kada kidamu,

Tabi bayan nurse ɗin suka fice, kamar khaltum tabi bayan su haka take ji to amma bata jin ma zata iya tashi ji take kamar ankashe mata jiki, ga ciwo datakeji asaitin zuciyar ta,

_______________________
_________________
____________
*Back to Arab Estate*
Sannu yaro na da alama yau kagaji sosai, cewar uncle Bello dake zaune yana kallon sulaim a parlon baffa, to ya aikin? ya tambayi sulaim ɗin,

Alhamdulillahi daddy sulaim Wanda ke zaune kusa da baffa ya amsa gabansa kuma laptop ce saman wani ɗan ƙaramin kushin mai tudu an rubuta _Hp_ a bayan computer ɗin, da alama aiki yake yi,

Kallon daddyn Canada baffa yayi kafin yace wai Bello baza ka bamu guri bane,

Ƴar dariya uncle Bello yayi kafin yace to baffa ai mu mundawo nan koro mu fa suka yi,

A a Bello koro shi dai kuka yi ai hadda kai Tunda kana kallo agaban ka suka kore shi, daga Part ɗin su, yanzu kuma shine zaka biyo shi, ai bazai koma ba ya dawo kenan dama anan ɗin yake tun farko, cikin wasa baffa yake maganar don dama shi mutum ne mai wasa da ƴan ƴan shi da kuma jikokin sa, idan suna hira da yaransa sai ka rantse ma abokai ne, amma shi mutum ne mai magana ɗaya ga dattaku, bai kuma yadda ƙarami ya raina na sama dashiba, acikin iyalan sa,

To shikenan baffa yanzu dai zantafi ɗin Tunda kora ta kukeyi amma ataya mu bawa ɗan nawa hak'uri ya dawo,

A sauka lafiya cewar baffa dayake kallon sulaim ɗin don ganin abunda zai yi,

Tashi sulaim yayi ya ɗan matsa kusa da dadin, baffa yayi tunanin binsa zai yi sai kuma yaji yace,
" Allah yabamu alkhairi daddy" nayi missing mommy sosai, zanzo mu gaisa anjima,
Kamar mai ciwon baki yayi maganar,

Murmushi daddyn yayi aransa yana mamakin hali irin na sulaim tabbas idan da lalura to akwai hali, ma wato da gaske sulaim fushi yayi kenan sai sunzo biko,

Ɗan rungume shi daddyn yayi ta gefe sannan yace to yaron kirki sai kazo idan ma bakazo ba muza muzo ai,

Komawa sulaim yayi ya zauna inda ya tashi batare da yace komai ba, shima daddyn kusa da baffa ya matsa yaɗan russuna sannan yace, a huta lafiya baffa,

Jinjina kai kawai baffan yayi sannan shikuma ya fita,

Shiko sulaim wani daɗi yake ji, aransa bayan lokaci mai tsayi, da cire tsammani, amma gashi a yau yayi wa wata aiki kuma cikin nasara da iKon Allah ta tashi ta farfaɗo, ahankali ya furta alhamdulillahi,

Baffa yace sulaim naga kamar kana murmushi,
kallon baffa sulaim yayi, sannan yace, "eh amma Bakomai" ya so faɗawa baffa abun da ya faru sai kuma yaji bakin sa yayi nauyi ya kasa, amma tabbas yasan da ya faɗa masa da baƙaramar murna baffa zaiyiba,

Murmushi kawai baffa yayi, batare da shima yace komai ba,

______________________
Mama bilki ce zaune aka tafaran perlon ta, ta ɗora ƙafa ɗaya bisa ɗaya, lace ne a jikin ta mai tsadar gaske launin sky blue anyi masa kwalliyar stone, sai ɗaukar ido yake, sai babbar ƴar ta mace wato jamila, dake zaune a kujerar kusa da ita, sai uncle Mansur dake fuskantar su, cikin fusata tafara magana,
"Haba Haba na gaji da wannan al'amarin da yaƙici yaƙi cinye wa, Tunda na shigo gidan alhaji imran arab, nake fama da uwar gidan sa, da ƴa ƴan ta ace kullum sune agaba acikin gidan nan, yanzu gashi jinkan tama yana nema yazamar min ciwon ido,
To wlh da sake da sake fa bazaiyiwu ba, dole asan abunyi, yanzu nayi waya da, boka zarshima, yana sanar min wai yaron nan da muka daɗe muna aiki akan sa ace, yau yayi wa wata aiki, kunga kenan akwai alamun aiki yafara war ware wa, kuma sannan ya tabbatar min da cewa ya samu kwarin gwaiwa da nasara ne daga ƴar uwar wadda yayi wa aikin, sannan Yace min tabbas yarinyar tananan kuma zata tun karo gidan nan, idan kuma har hakan ta faru to babu ko shakka komai namu zaizo ƙarshe, to nikuma bazan taɓa barin hakan ya faru ba koda ace zanyi yawo tsirara ne to bazan bari iyalai na su wulaƙan taba,

Ai wlh mama lefin kine nace miki akwai wani boka da nasani, aikin shi kamar yankan wuƙa haka yake, kamata yayi mu maida aikin komai gurin shi, da tuni yanzu wata maganar ake bawannan ba aƙasar India yake , cewar jamila wadda tazo gidan a daran jiya saboda, taji labarin saleem ya mari ɗiyar ɗan uwan ta, he excellency Sambo, tana jin labari ya biyo jirgin dare daga Abuja, don zuwa ɗaukar mataki,

Kallon su uncle mansur yayi cikin, matsanancin ɓacin rai ya soma magana wanda saboda tsabar masifa, har shaƙe wa yake wajan cewa, kowa ce wannan yarinyar daza tazamar mana barazana dole ne mudakatar da shigowar cikin ahalin mu,

Kallon shi mama bilki tayi, abunda ya kamata mu fara yi kenan, tun kafin wankin hula yakaimu mu dare,

____________________
Yauwa mommyn yara dama inaso muyi magana, ne cewar ummeetha dake zaune kan super,

To inajinki cewar mommyn,

Dama sonake kafin saleem ya wuce Lagos mu shirya zuwa *MASARAUTAR GABAS*.

*Share and like fisabilillah*🙏

https://whatsapp.com/channel/0029Van1Keq59Pwb6CDnwe0V

*AHALIN MU DAYA*

*CREATED AND WRITTEN*
*BY*
*Fatima Y zakariyya*
_😍Oum Ameerah_😍

*NAZARI WRITER'S ASSOCIATION*📚
_Sarauniyar👸Nazari writer's association_

______Dedicated to aunty salma💎

*Page* 2️⃣5⃣▶️2️⃣6⃣📖
Dama so nake kafin saleem ya wuce Lagos mu shirya zuwa *MASARAUTAR GABAS*

Eh gaskiya kam ya kamata saboda tun wancan zuwan namu Nigeria🇳🇬 ba wanda ya wuce ba Bamu ƙara zuwa ba, kuma ya kama ta aje a gaida baba Waziri, cewar mommy tana ɗan murmushi,
Sai afaɗawa yaran su fara shiri ko, koya zamuyi da sulaim gashi da yayi mana yaji da gaske,

Murmushi ummeetha tayi, to kuma dai kunga halin ɗan naku ko, dama fa can yana da tsarin komawa Part ɗin baffa, to shine yanzu kawai Yakoma, kuma ko da yana wannan Part ɗin ai ba ganin shi aikeba sai Anne meshi, Sannan DUK sanda ya bushi iska saidai muji labarin yana MASARAUTAR GABAS Din,

Au ashe ma yana zuwa? Mommy ta tambaya

Eh yana zuwa sosai don mayanzu yaɗan rage zuwa Tunda wani couse ya kai *YARIMAN GABAS* Korea 🇰🇷 kusan 1year kenan, to ya ɗan rage zuwa,

Hhm to shekenan, naji ansanar da taron gaggawa anjima idan muka je nidai zanyo bikon kalbiy na,

Suhailat ce ta sakko daga upstairs, cikin shiga mai kyau ta alfarma, material yard ne ajikin ta ɗan uban su wadda ko na faɗa maka ba kasan ba irin nayaku bayi bane, coffee colour anyi masa ɗinkin A shape mai kwala a wuya, abunka da dogon mutum gata fara, sai yadin material ɗin ya haska ta sosai, tayi yafa mayafi brown color Mai haske, ƙafar ta na sanye da plate shoe shima brown colour, tayin kyau sosai,

Ƙarasa wa tayi gurin da su mommy da ummeetha suke a zaune, tace mommy barkan ku da gida,

Barka dai daughter har kunshirya kenan,! "eh mommy"

Ummeetha tace to ina saleema? "nayi zaton ta tafi ai, cewar Suhailat,

Kafin ummeetha tace wani abu saiga, saleema itama tana sakkowa cikin salo da yanga, riga da wando ne ajikin ta irin American dress ɗin nan, rigar tata har gwaiwa red colour sai Wasu manya yanyan bottle golden colour da akayi adon rigar da su guda uku, wandon ma golden ne, ta ɗan buɗe daga ƙasa kamar flazo, hannun ta riƙe da jaka irin pos ɗin nan itama black taji stone, GA wani uban glass data saka yacin ye rabin fuskar ta, mayafin tana ɗa akan ta kamar rawani ahaka ta fito, sai tashin ƙamshi takeyi dama bikin ɗiyar uncle ɗin su saleema akeyi yayan mommy uncle tahir to yau suka fara bikin shine zasu yi gaba kafin zuwan su mommyn ita kuma suhailat amaryar friend ɗin tace tare suka yi North West kano , tsaya wa tayi itama a gurin su mommy sannan tace, ummeetha mommy na wuce,

Saikin a dawo lafiya, ummeetha tace mata tare da ɗaga mata hannu alamar bye bye,

Har tafara tafiya mommy ta kalle Suhailat tace to Tunda kunfito tare, driver yakaiku mana,

"No mommy zantafi nida yaya sulaim ne zanje part ɗin grandad ɗin Yanzu sai mutafi tare, kallon Suhailat tayi kafin ta ce," _u can go if you want_"

Mai makon abun yabawa Suhailat haushi sai ma tayi murmushi sannan tace _Don't worry about it saleema till we meet there_ aranta Kuma tace Allah sarki ashe babu rabon yau kije bikin nan Indai yaya sulaim ne zai kai ki,

Atare suka yi hanyar fita daga perlon, ummeetha aranta tana addu'ar Allah ya shirya musu zuri'a atako, mommy da alama hakan ko a jikin ta, don su agurin su hakan Bakomai bane,

Parking space suka nufa tunkafin suƙarasa, saleem dake zaune acikin mota yana jiran futuwar suhailat, tada motar yayi sannan yayi parking a dai dai gaban Suhailat, aiko ta tsaya kafin tayi wani motsi har yafito yabuɗe mata ɗayan ɓangaran, kallon shi Suhailat ɗin tayi da murmushi a kan fuskar ta tace,
"wlh yaya saleem idan kanamin irin wannan abun duk sai narin ƙajin kunya, so kake ace kazama driver ɗina ko," to wlh babu ruwa idan budurwar ka taji labari, takai ƙarshen maganar tare da shige wa cikin motar,

Shima dariya yayi kawai yaza gaya Yakoma driver site, yazauna suka fice daga house din ya hau titin hameed Arab way,

Saleema ma mota ta shiga ta nufi Part ɗin kakan nunsu gurin sulaim,
Chapter 15 · 0% Book details