Sashe 21
Ahalinmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi kawai Imran Arab yayi batare dayace komai ba Amma Kuma tabbas Shima ya dade Yana wannan tunanin acikin Aransa, Kuma sannan kobanza burin sa natara iyalai dayawa zai cika idan har allah yakawo rabo,
Take mahaifin da yafado masa a Rai, cikin zuciyar sa yafara tunanin da ace mahaifin da ya Tara mata da yawa ai Shima yanzu dabai rasa Dan uwa ba, take yabawa kansa amsa ta hanyar cewa aikomai na Allah ne sannan ya qaddara komai,
Da wannan tunani yakoma gida *Niger republic*
Baiyi Wani tunanin ya sanar wa matar sa Amina maganar auran da yakeso zaiqara saboda baya boye mata komai Koda kuwa Hakan bazai Yi mata Dadi ba,
Taji Babu Dadi sosai Amma sai ta shanye a lokacin Dan su hameed Bai wuce shekara 2 ba,
Cikin qanqanin lokaci alhaji Imran Arab yafara shirin aure da wata Wadda suka hado, a Wani gidan cin Abinci *restaurant* a jahar katsina, Mai suna bilkisu, yarinyar Mai gidan abincin ce dama ta dade tana nuna masa tana sonshi a duk lokacin da suka zo Amma Bai taba Bata dama ba,
Wannan batu baqaramin Dadi yayiwa bilki da mahaifiyar taba, bayan an daura auran sa da bilki,
Sai ya ajiye ta a Wani gidan sa da ya dade da siya a Nasarawa, cikin garin Kano,
Bilki maca ce Mai son zuciya, son abun duniya, zata iya yin komai saboda ta samu abunda takeso,
Akusan lokaci ɗaya bilki da Amina suka haihu, wanda duk suka haifi ƴaƴa maza, bilki haihuwa fari wanda ɗan yaci suna Hasheem,
Itakuma Amina haihu ta biyu ne tayi wanda aka sawa ɗan suna Bello,
Ahaka alhaji imran Arab ya cigaba da gudanar da harkokin sa cikin tarin nasarori da cigaba, iyali suka cigaba da haɗuwa da ta kowane ɓangare daga matan nasa, baya wani samun tashin hankali daga gare su saboda ko wacce ƙasar da take zaune daban,
Ko wacce cikin su ya kai ta *UMRA* da aikin *HAJJI* hada ƴaƴan sa a lokacin kasuwancin sa har ƙasa shan waje sosai yake fitar dasu, komai tare yake yi da babban ɗan sa hameed
tun hameed ɗin baya so amma ya hakura saboda shi yafison aikin gomnati akan kasuwanci sam baya burgeshi,
Amma da haka har ya hakura ba yadda ya iya,
A lokacin ne alhaji hameed ARAB yafara tunanin haɗe iyalinsa guri ɗaya, yafara tunanin a wace ƙasa zai zauna tsakanin NIGERIA da NIGER,
Duba da yanayin komai nasa yafi ƙarfi a Nigeria hakan yasa shi zarɓar haɗe su acan ɗin, take aka fara dan ƙara ginin babban ESTATE unguwa guda saboda alhaji imran yana da burin hatta jikokin sa idan suka tashi aure anan zasu zauna,
Yaɗora babban ɗan nasa hameed akan ginin estate ɗin da akeyi, komai daza abuƙata na ginin daga ƙasar waje aka kawo sa,
Ko engineer ɗin daya zana ginin ba a ƙasar nan yake ba shima kansa saida abun yabirgeshi saboda Tunda yake zane bai taɓa mai girman wannan ba kuma yabirgeshi haka ba,
Ya jinjinawa alhaji imran sosai saboda komai bada naira aka biya ba anci kuɗi sannan kuma an ɗan ɗauki lokaci anayi, hameed ne ki tsaye kan komai duk da yana fama da school matakin Masters,
Lokacin da Alhaji imran yajewa da uwar gidan sa wadda suke kira da Hajiya umma, batun koma warsu NIGERIA gaba ɗaya ƙin yadda tayi saboda tana ganin ga dan ginta da ƴan uwan ta zata tafi tabar su, daƙar dai alhaji imran ya samu ya shawo kanta ta amince badan tana soba,
Tunda hasheem yazo ganin ginin estate ɗin da mahaifin nasu keyi, yaga komai ɗan uwansa hameed ne akayi, yaje yabawa mahaifiyar su labari wadda suke kira da mama bilki shikenan hankalin ta yaƙara tashi ainun,
Ta ƙara ɗaura ɗamara gurin bin bokayen ta kala kala, duk wata hanyar banza ta sani ita ke ɗora ƴaƴan ta a kai bama kamar babban ɗan nata wanda take ganin alhaji imran ɗin baya saka shi cikin kasuwancin sa,
shikuma yana ƙin ɗora shine saboda yafison yaga ya nutsu sannan, saboda hasheem irin mutanan nan ne masu san sharholiya da son duniya, ga shaye shaye ga son zuwa club kullum shine zuwa mashaya (BAR),
Shiyasa alhaji imran baya saka shi acikin komai nashi saboda yafa himci bashi da nutsuwa,
Duk tunanin mama bilkisu Yakoma kan duk yadda zatai zata yi saboda kada Hajiya umma ta dawo cikin estate ɗin da zasu koma, tafi son yazama daga ita sai ƴaƴan ta,
Tabi boka ye kala kala suna bata asiri saboda duk dan kada su haɗe a guri ɗaya amma ina, duk sanda zata yi abun babu nasara,
Naƙar she ne ta samu a wajan wani bokan ta mai suna ZARSHIMA yabata wani ruwan magani yace ta tabbata ta dafa wa alhaji imran abinci dashi wannan ruwan, a ranar da zai koma ƙasar Niger, Idan har ya haɗu da matar sa Hajiya umma a wannan ranar to ko ƙasar Nigeria bazai taɓa barin ta tazo ba bare ma su zauna guri ɗaya,
Haka kuwa akayi ranar da ta tabbatar zai tafi da wuri ta tashi ta shiga kichin da kanta don yi masa breakfast dakan ta saboda tasamu ta sarrafa shi da wannan ruwan da boka ZARSHIMA ya bata,
Aiko cikin sa'a alhaji imran yaci abincin sosai sannan yayi mata sallama da niyar ya tafi, baƙaramin daɗi ne ya rufe mama bilki ba don tasan komai ya tafi yadda ta tsara kuma takeso,
Alhaji imran da yanu airport domin komai a tsare yake jirgin safe zai hau zuwa *Niger republic*
Akan hanyar sa ne abokin sa alhaji idris yakirashi kan duk abunda yake yazo zasu yi zaman gaggawa yau ɗin nan a garin Katsina,
Alhaji imran ya faɗa masa Niger yanufa amma Tunda a Katsina nane bari yazo gidan nashi kawai sai su tafi idan suka gama meeting ɗin sai ya wuce Niger,
Dahaka suka yi salla alhaji imran yabawa driver ɗin nasa umarnin su nufi gidan alhaji idris ɗin tsaye,
Babu musu ya ɗauki hanyar unguwar gadon Ƙaya, zuwa gidan alhaji idris ɗin Tunda dama ya sani,
Babu ɓata lokaci suna zuwa, alhaji idris yaga shirya musu komai, kawai hanyar Katsina State su ɗauka,
A ranar meeting sukayi sosai da wasu mutanan da suke kasuwanci dasu mazauna ƙasar Australia 🇦🇺kan wani sabon company da suke so su kafa a ƙasar ta Australia, take alhaji imran ya wakilta babban ɗansa HAMEED ARAB kan wanda zai wakilcesa zuwa ƙasar Australia 🇦🇺
Sanda suka gama meeting ɗin around 6:44pm magrib tayi,
Kabari mana zuwa gobe sai ka wuce Niger ɗin nima saina koma gida, Tunda dare ya ƙara to kuma dama inaso mu tattauna akan wasu batutuwa cewar alhaji idris, wanda ke kallon alhaji imran ɗin,
Dan Jimm alhaji imran yayi kafin yace to Allah ya kaimu lafiya, ba don taso ba ya so ganin uwar gidan sa kuma farin cikin sa a ranar to amma ai duk ɗaya ne a gurin Allah da haka ya kau da tunanin nasa,
A wani guest house ɗin alhaji imran suka sauka wanda ke acikin garin Katsina dama yakan sauka anan ɗin idan dare yayi masa a hanya,
Sosai alhaji idris yabawa alhaji imran shawara kan ya rage tunanin dayake yawanyi,
saboda doctor ya faɗamin wancan lokacin da ya duba ka jinin ka ya hau sosai, duk nameye wannan ɗin?
Ka ƙara hak'uri sosai idan har ƴar uwar ka da mahaifan ka naraye zaku gana kuma zamu cigaba da bibiyar garin da harzuwa sanda Allah zai sa a dace,
Sosai alhaji imran yaji daɗin maganganun abokin nasa kuma aminin sa duk da ya sosa masa inda yake yi masa ƙaiƙayi gashi dama a ɗan tsakanin nan yana yawan mafarkin ƙanwar tasa wato BAHIJJAH Sai dai kawai yayi addu'ar Allah yasa duk inda suke suna cikin ƙoshin lafiya,
Sannan alhaji idris ɗin ya ƙara da cewa, kuma baka ganin kana ɗan matsawa HAMEED da harkokin nan kuma na fahimci kamar yafison karatun sa,
Alhaji idris kenan ai HAMEED dole shi zai tsaya akan komai kaga kuwa dole yafara sabawa da su tun yanzu,
Jinjina kai alhali idris yayi alamar gamsuwa, da haka dai suka cigaba da tattaunawa da kuma bawa juna shawar wari game da rayuwar su,
Bayar da wuwar alhaji imran ARAB Nigeria aka fara zuba kaya acikin estate ɗin wanda tsayawa faɗar tsarin sa ma ɓata lokaci ne komai na amfanin gida kama daga furnitures, daga ƙasashe daban daban aka kawo su,
Mama bilki kullum farin cikinta zata mallaki estate mai girman gari guda, daga ita sai ƴaƴan ta,
Aranar da suka dawo nan bata san Hajiya umma kwanan su na biyu kenan aciki, tana ta haukan ta,
Saida alhaji imran yace zai shirya zama da dukan su sannan tasani baƙaramin tashin hankali ta shiga ba tama rasa tunanin Meye zata yi, to aikin bokan tane bai yiba koko ita tayi kuskure wajan aikin, ta tambayi kanta,
Tare da masifar ai alhaji imran yaci amanar ta bai faɗa mata ya ɗakko matar shiba, gashi boka ZARSHIMA yace mata duk wadda tafara shiga cikin estate ɗin acikin su to ita zata mallaki komai sannan ƴaƴan ta zasu jagoran ci komai na ARAB family,
Tuna wannan maganganun bokan ne yasa ta ƙara jin kamar tayi hauka, amma bazata haƙuraba dole tasan abunda zata yi,
Da yake gogaggiyar ƴar duniya ce bata taɓa nuna mugun halinta a fili ko hassadar ta akan Hajiya umma da ƴaƴan ta,
Rayuwa mai daɗi suke gabatar wa acikin estate Ɗin amm banda mama bilki wadda kullum tunanin ta da lissafin ta taya zata kai Hajiya umma ƙasa,
Bayan wani lokaci hasheem yazo da maganar aure, alhaji imran bai hana shiba saboda yana ganin kamar hakan zai sa ya gara halayen sa,
Fatan alkhaeri alhaji imran yayi masa tare da bashi mukullin house guda ɗaya acikin estate ɗin,
Hasheem baiyi wani farin ciki ba saboda shi kuɗi yake so kawai a sakar masa, shikuma alhaji imran yace bazai bashi ba amma shi zai yi koma ya zaɓi ko Meye yakeso afaɗin Kasar Nigeria da ƙetare zai yi masa shi,
Amma ina hasheem yaƙi yadda daga ƙarshema sai yayi zuciya yace bazai zauna acikin estate ɗin ba shida matar tasa,
Take mahaifin da yafado masa a Rai, cikin zuciyar sa yafara tunanin da ace mahaifin da ya Tara mata da yawa ai Shima yanzu dabai rasa Dan uwa ba, take yabawa kansa amsa ta hanyar cewa aikomai na Allah ne sannan ya qaddara komai,
Da wannan tunani yakoma gida *Niger republic*
Baiyi Wani tunanin ya sanar wa matar sa Amina maganar auran da yakeso zaiqara saboda baya boye mata komai Koda kuwa Hakan bazai Yi mata Dadi ba,
Taji Babu Dadi sosai Amma sai ta shanye a lokacin Dan su hameed Bai wuce shekara 2 ba,
Cikin qanqanin lokaci alhaji Imran Arab yafara shirin aure da wata Wadda suka hado, a Wani gidan cin Abinci *restaurant* a jahar katsina, Mai suna bilkisu, yarinyar Mai gidan abincin ce dama ta dade tana nuna masa tana sonshi a duk lokacin da suka zo Amma Bai taba Bata dama ba,
Wannan batu baqaramin Dadi yayiwa bilki da mahaifiyar taba, bayan an daura auran sa da bilki,
Sai ya ajiye ta a Wani gidan sa da ya dade da siya a Nasarawa, cikin garin Kano,
Bilki maca ce Mai son zuciya, son abun duniya, zata iya yin komai saboda ta samu abunda takeso,
Akusan lokaci ɗaya bilki da Amina suka haihu, wanda duk suka haifi ƴaƴa maza, bilki haihuwa fari wanda ɗan yaci suna Hasheem,
Itakuma Amina haihu ta biyu ne tayi wanda aka sawa ɗan suna Bello,
Ahaka alhaji imran Arab ya cigaba da gudanar da harkokin sa cikin tarin nasarori da cigaba, iyali suka cigaba da haɗuwa da ta kowane ɓangare daga matan nasa, baya wani samun tashin hankali daga gare su saboda ko wacce ƙasar da take zaune daban,
Ko wacce cikin su ya kai ta *UMRA* da aikin *HAJJI* hada ƴaƴan sa a lokacin kasuwancin sa har ƙasa shan waje sosai yake fitar dasu, komai tare yake yi da babban ɗan sa hameed
tun hameed ɗin baya so amma ya hakura saboda shi yafison aikin gomnati akan kasuwanci sam baya burgeshi,
Amma da haka har ya hakura ba yadda ya iya,
A lokacin ne alhaji hameed ARAB yafara tunanin haɗe iyalinsa guri ɗaya, yafara tunanin a wace ƙasa zai zauna tsakanin NIGERIA da NIGER,
Duba da yanayin komai nasa yafi ƙarfi a Nigeria hakan yasa shi zarɓar haɗe su acan ɗin, take aka fara dan ƙara ginin babban ESTATE unguwa guda saboda alhaji imran yana da burin hatta jikokin sa idan suka tashi aure anan zasu zauna,
Yaɗora babban ɗan nasa hameed akan ginin estate ɗin da akeyi, komai daza abuƙata na ginin daga ƙasar waje aka kawo sa,
Ko engineer ɗin daya zana ginin ba a ƙasar nan yake ba shima kansa saida abun yabirgeshi saboda Tunda yake zane bai taɓa mai girman wannan ba kuma yabirgeshi haka ba,
Ya jinjinawa alhaji imran sosai saboda komai bada naira aka biya ba anci kuɗi sannan kuma an ɗan ɗauki lokaci anayi, hameed ne ki tsaye kan komai duk da yana fama da school matakin Masters,
Lokacin da Alhaji imran yajewa da uwar gidan sa wadda suke kira da Hajiya umma, batun koma warsu NIGERIA gaba ɗaya ƙin yadda tayi saboda tana ganin ga dan ginta da ƴan uwan ta zata tafi tabar su, daƙar dai alhaji imran ya samu ya shawo kanta ta amince badan tana soba,
Tunda hasheem yazo ganin ginin estate ɗin da mahaifin nasu keyi, yaga komai ɗan uwansa hameed ne akayi, yaje yabawa mahaifiyar su labari wadda suke kira da mama bilki shikenan hankalin ta yaƙara tashi ainun,
Ta ƙara ɗaura ɗamara gurin bin bokayen ta kala kala, duk wata hanyar banza ta sani ita ke ɗora ƴaƴan ta a kai bama kamar babban ɗan nata wanda take ganin alhaji imran ɗin baya saka shi cikin kasuwancin sa,
shikuma yana ƙin ɗora shine saboda yafison yaga ya nutsu sannan, saboda hasheem irin mutanan nan ne masu san sharholiya da son duniya, ga shaye shaye ga son zuwa club kullum shine zuwa mashaya (BAR),
Shiyasa alhaji imran baya saka shi acikin komai nashi saboda yafa himci bashi da nutsuwa,
Duk tunanin mama bilkisu Yakoma kan duk yadda zatai zata yi saboda kada Hajiya umma ta dawo cikin estate ɗin da zasu koma, tafi son yazama daga ita sai ƴaƴan ta,
Tabi boka ye kala kala suna bata asiri saboda duk dan kada su haɗe a guri ɗaya amma ina, duk sanda zata yi abun babu nasara,
Naƙar she ne ta samu a wajan wani bokan ta mai suna ZARSHIMA yabata wani ruwan magani yace ta tabbata ta dafa wa alhaji imran abinci dashi wannan ruwan, a ranar da zai koma ƙasar Niger, Idan har ya haɗu da matar sa Hajiya umma a wannan ranar to ko ƙasar Nigeria bazai taɓa barin ta tazo ba bare ma su zauna guri ɗaya,
Haka kuwa akayi ranar da ta tabbatar zai tafi da wuri ta tashi ta shiga kichin da kanta don yi masa breakfast dakan ta saboda tasamu ta sarrafa shi da wannan ruwan da boka ZARSHIMA ya bata,
Aiko cikin sa'a alhaji imran yaci abincin sosai sannan yayi mata sallama da niyar ya tafi, baƙaramin daɗi ne ya rufe mama bilki ba don tasan komai ya tafi yadda ta tsara kuma takeso,
Alhaji imran da yanu airport domin komai a tsare yake jirgin safe zai hau zuwa *Niger republic*
Akan hanyar sa ne abokin sa alhaji idris yakirashi kan duk abunda yake yazo zasu yi zaman gaggawa yau ɗin nan a garin Katsina,
Alhaji imran ya faɗa masa Niger yanufa amma Tunda a Katsina nane bari yazo gidan nashi kawai sai su tafi idan suka gama meeting ɗin sai ya wuce Niger,
Dahaka suka yi salla alhaji imran yabawa driver ɗin nasa umarnin su nufi gidan alhaji idris ɗin tsaye,
Babu musu ya ɗauki hanyar unguwar gadon Ƙaya, zuwa gidan alhaji idris ɗin Tunda dama ya sani,
Babu ɓata lokaci suna zuwa, alhaji idris yaga shirya musu komai, kawai hanyar Katsina State su ɗauka,
A ranar meeting sukayi sosai da wasu mutanan da suke kasuwanci dasu mazauna ƙasar Australia 🇦🇺kan wani sabon company da suke so su kafa a ƙasar ta Australia, take alhaji imran ya wakilta babban ɗansa HAMEED ARAB kan wanda zai wakilcesa zuwa ƙasar Australia 🇦🇺
Sanda suka gama meeting ɗin around 6:44pm magrib tayi,
Kabari mana zuwa gobe sai ka wuce Niger ɗin nima saina koma gida, Tunda dare ya ƙara to kuma dama inaso mu tattauna akan wasu batutuwa cewar alhaji idris, wanda ke kallon alhaji imran ɗin,
Dan Jimm alhaji imran yayi kafin yace to Allah ya kaimu lafiya, ba don taso ba ya so ganin uwar gidan sa kuma farin cikin sa a ranar to amma ai duk ɗaya ne a gurin Allah da haka ya kau da tunanin nasa,
A wani guest house ɗin alhaji imran suka sauka wanda ke acikin garin Katsina dama yakan sauka anan ɗin idan dare yayi masa a hanya,
Sosai alhaji idris yabawa alhaji imran shawara kan ya rage tunanin dayake yawanyi,
saboda doctor ya faɗamin wancan lokacin da ya duba ka jinin ka ya hau sosai, duk nameye wannan ɗin?
Ka ƙara hak'uri sosai idan har ƴar uwar ka da mahaifan ka naraye zaku gana kuma zamu cigaba da bibiyar garin da harzuwa sanda Allah zai sa a dace,
Sosai alhaji imran yaji daɗin maganganun abokin nasa kuma aminin sa duk da ya sosa masa inda yake yi masa ƙaiƙayi gashi dama a ɗan tsakanin nan yana yawan mafarkin ƙanwar tasa wato BAHIJJAH Sai dai kawai yayi addu'ar Allah yasa duk inda suke suna cikin ƙoshin lafiya,
Sannan alhaji idris ɗin ya ƙara da cewa, kuma baka ganin kana ɗan matsawa HAMEED da harkokin nan kuma na fahimci kamar yafison karatun sa,
Alhaji idris kenan ai HAMEED dole shi zai tsaya akan komai kaga kuwa dole yafara sabawa da su tun yanzu,
Jinjina kai alhali idris yayi alamar gamsuwa, da haka dai suka cigaba da tattaunawa da kuma bawa juna shawar wari game da rayuwar su,
Bayar da wuwar alhaji imran ARAB Nigeria aka fara zuba kaya acikin estate ɗin wanda tsayawa faɗar tsarin sa ma ɓata lokaci ne komai na amfanin gida kama daga furnitures, daga ƙasashe daban daban aka kawo su,
Mama bilki kullum farin cikinta zata mallaki estate mai girman gari guda, daga ita sai ƴaƴan ta,
Aranar da suka dawo nan bata san Hajiya umma kwanan su na biyu kenan aciki, tana ta haukan ta,
Saida alhaji imran yace zai shirya zama da dukan su sannan tasani baƙaramin tashin hankali ta shiga ba tama rasa tunanin Meye zata yi, to aikin bokan tane bai yiba koko ita tayi kuskure wajan aikin, ta tambayi kanta,
Tare da masifar ai alhaji imran yaci amanar ta bai faɗa mata ya ɗakko matar shiba, gashi boka ZARSHIMA yace mata duk wadda tafara shiga cikin estate ɗin acikin su to ita zata mallaki komai sannan ƴaƴan ta zasu jagoran ci komai na ARAB family,
Tuna wannan maganganun bokan ne yasa ta ƙara jin kamar tayi hauka, amma bazata haƙuraba dole tasan abunda zata yi,
Da yake gogaggiyar ƴar duniya ce bata taɓa nuna mugun halinta a fili ko hassadar ta akan Hajiya umma da ƴaƴan ta,
Rayuwa mai daɗi suke gabatar wa acikin estate Ɗin amm banda mama bilki wadda kullum tunanin ta da lissafin ta taya zata kai Hajiya umma ƙasa,
Bayan wani lokaci hasheem yazo da maganar aure, alhaji imran bai hana shiba saboda yana ganin kamar hakan zai sa ya gara halayen sa,
Fatan alkhaeri alhaji imran yayi masa tare da bashi mukullin house guda ɗaya acikin estate ɗin,
Hasheem baiyi wani farin ciki ba saboda shi kuɗi yake so kawai a sakar masa, shikuma alhaji imran yace bazai bashi ba amma shi zai yi koma ya zaɓi ko Meye yakeso afaɗin Kasar Nigeria da ƙetare zai yi masa shi,
Amma ina hasheem yaƙi yadda daga ƙarshema sai yayi zuciya yace bazai zauna acikin estate ɗin ba shida matar tasa,