← Book details Ahalinmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 37

Sashe 27

Ahalinmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Room din farko Sulaim ya shiga yayi wanka yana fitowa ya ga kaya gefan saman make kyan bed ɗin baiyi mamaki ba saboda yasan Sultan ne yasa aka kawo su saboda idan yazo harya koma kaya iri daya suke sawa saidai wani lokacin kawai kala ce zata ban banta shima ba ko yaushe ba,

Cikin ƙanƙanin lokaci ya shirya cikin kayan da Yarima Sulaim ya aiko dasu don jin daɗin sa,

Wani ɗanyan yadi ne launin ruwan madara mai turuwa wanda ake kira da butter milk bashida nauyi rigar taɗan haura gwaiwa kadan mai gajeran hannu iya gwaiwa yayi kyau sosai,

Sanda yafito a parlourn ya tadda Yarima Sultan shima cikin shigar sa sak irin ta Sulaim komai da komai ban bancin daya ne Yarima Sultan yaɗora alkyabba bisan kayan nashi,

Barka da fitowa Amini na cewar Sultan,

Allah yasa Yarima baiyi Fushi ba Sulaim ya faɗa cikin sigar wasa,

Murmushi Sultan yayi kafin yace hukunci ya tabbata akan wanda ya ɓatawa Sultan rai,

Shima murmushin Sulaim yayi batare da yace komai ba,

Naga lokacin sallah ya gabato mu fara muje masallaci bayan mun gabatar da salla sai munufi *FADA* gurin mai martaba,

Sulaim yace hakan yayi

Kallon Sulaim yayi kafin yace Wato kana nan da halinka wai Meyasa baka son alkyabba ne? naga acikin kayan da na aiko maka hadda ita,

Zata dame ni ne abunda sulaim yace kenan

Murmushi Sultan yasakyayi akaro na biyu idan kaine a matsayi na yazakayi kenan?

Sulaim yace Yadda nayi yanzu,

Batare da Yarima Sultan ya ƙara cewa komai ba haka ya tashi suka fita,

Baƙaramin kyau suka yi ba tamkar ƴan biyu sai haske suke tamkar wata daran goma sha biyu,

*YARIMA SULTAN* kyakkyan wane ajin farko ga kyau ga mulki ga izza ga kwarjini ga ilimi dukiya kwa ba a magana ɗan gayu yana da miskilan ci amma bai kai Sulaim ba gashi fari ne tas amma farin nasa irin jannan ne launin mutanan Koria dogon hancin sa har wani dan lankwasawa yayi ga dara daran ido farare tasss kwayar ciki kuma baƙa siɗik tana yawo saman farin idon da har wani farin ruwa ne aciki tamkar yawaye amma ba hawaye bane halittar sa ce ahaka, lips din da red colour tamkar yasamusu Kala,
Yana da bayyanan nan kyau ga tsayi kamar Sulaim komai nashi mai jan hankali ne,

Bayan sun fito daga babban masallacin cikin masarautar Yarima Sultan ya samu labari mai martaba sarki yayi baƙi,

Sai suka fasa zuwa fadar suka wuce Layin UMMUL BAIT Sufara gaisa wa da ita suka barshi zuwa gobe sai gana da mai martaba,

Zaune take tana fuskan tar qofar shigowa parlourn qafafuwan ta saman kushin gaban ta Wani babban tire ne na kayan marmari nau'i kala kala kama daga kan, tuffa, zaitun, ayaba, lemo, inibi, da dai sauran su,

Ta Dora alkyabba saman Wani hadaddan lace Wanda Bai sai antsaya gaya Maka kudin saba, wuyan ta da hannun ta sun Sha kayan a do na zinare sai kalli suke,

Matar fara ce sosai da kaganta zaka iya cewa balarabiya ce ko Kuma help CAS gata doguwa duk da a zaune take Amma yanayin ta yanuna Hakan Daka ganta kasan Ita ta haifi Yarima Sultan duk da shi farin sa irin na mutanan yankin qasar koria ne, ta Dan manyan ta Amma dayake akwai hutu baza kataba gane Hakan ba bugu da qari yar gayu ce sosai don ta Dan girmi ummeethar mahaifiyar Sulaim,

Wasu kuyangu ne guda hudu a gefe da gefan ta suna zaune daga qasa,

Ga wasu kuyangin suna ta aiki acikin parlourn wasu na goge goge wasu na aikin turaren wuta suna ta Kai kawo,

Jin sallama ne yasa ta dago ta kalli kofa ganin Yarima Sultan tare da Sulaim yasa ta fadada murmushin ta tare da amsa sallamar tasu cikin sautin da ba aji sosai,

Tunkafin su qara so ciki gaba daya bayin suka tashi suka hau zubewa suna kwasar gaisuwa wajen Yarima Sultan da Sulaim haka sukai tayi duk Wadda ta gaishe su saita bar parlourn saboda Indai Yarima ya shigo to Babu Mai zama aciki sai Wanda aka nawa Umarni,

Ga kujeru kala kala ga kushin ga wasu kujerun Suma kamar gadaje duk a parlourn Amma suka zauna a San carpet dai dai qafafuwan ta duk da Shima carpet din saboda laushi tamkar audiga,

Parlourn yayi kyau sosai idan kagani dole zai burgeka duka kwalliyar sarauta akayi masa sai wasu manya manyan hotuna guda biyu maqale a jikin babban bangon parlourn daya na Yarima Sultan ne yayi kyau sosai cikin shigar sarakai shikuma dayan hoton na wata kyakkyawar jaririya ce Wanda dagani jaririyar batafi wata daya ba akayi mata hoton,

Ko wace ce oho!

Haka suka zauna Sulaim bangaran daman ta shikuma Yarima Sultan bangaran hagu,
Barka da dare UMMUL BAIT Allah yasa Kuna cikin ameenci, Sulaim ne yafadi Hakan kanshi aqasa,

Ameen barka dazuwa *DAULAR SULTAN* Dana Sulaim Allah yasa kana lafiya, tafada cikin kulawa,

Sulaim ya amsa da Lafiya alhamdulillah
Ta tambaye shi su ummeethar yace suna Lafiya Suma suna hanya zuwa gobe da yaddar Allah,

Barka da hutawa fatan mun sameku cikin ameenci, cewar Yarima Sultan Wanda tunda suka shigo sai yanzu yayi magana,
Kallon Inda yake UMMUL BAIT tayi tare da fadin alhamdulillah fatan Dana Sulaim yasamu kyakkyawar tarba daga Sultan,

Dan murmushin Yarima Sultan yayi kafin yace Anyi duk abunda yadace,

Dakyau tafada ataqaice,

Dakaga yadda suke magana kasan mulki yagama zama a wannan gurin suna yin komai cikin girmamawa ga riqo da al'adun su kala kala,

Tashi sukayi kusan atare suka Dan russuna kafin Sultan yace,

MUN barku Lafiya Shima abunda Sulaim yace kenan,

Daga Kai kawai tayi sukuma suka fita
Murmushi UMMUL BAIT tayi harcikin ranta takeson Sulaim sosai jitake tamkar Ita ta haifeshi tana so taga yazo Hakan baqaramin Dadi yakeyi mata ba,

Suna tafe suna Dan hira jefi jefi sai wasu fadawan Yarima Sultan din guda uku 3 da suke take musu baya, kowa ba gwanin magana bane acikin su shi Sultan hadda mulki shikuma Sulaim haka take dama,
Gidan BABA WAZIRI suka nufa kakan Sulaim mahaifin ummeethar kenan Wanda gidan sa Akwai yar tafiya tsakanin bangaran dasuka baro na UMMUL BAIT

Badann Yarima Sultan yaso ba haka yake tafiyar qasan dama Indai ba Sulaim ne yazoba baya taba zuwa gidan baba WAZIRI aqafa sai dai a mota ki doki saboda Yana son tafiya doki,

danshi baiyason wahala Bai nasan taba shikuma Sulaim Yana son yaga Yana tattaki shiyasa mafi akasarin lokuta yake zuwa house din baffa aqasa daga house din su duk nisan dake tsaka nin su baya Jin komai,
Ko Ina haske gaba daya cikin masarautar tamkar da rana don ko allura ce yafadi zaka iya ganin ta,

GA kuyangi da bayi suna tafaman zirga zirga wasu da kaya a hannun su wasu babu suna tashi ga kowane Layi da bangarorin cikin ma sarautar tamkar da rana kamar kuma ana wani taro ko biki ko kuma daran sallah,

Duk inda Yarima Sultan yazo wucewa sai shida sulaim sai an buɗa musu sannan kuyangin ko bayin sai sun zube sun kwashi gaisuwa,

Ko ta kansu basa bi kawai tafiya suke cin nutsuwa da ƙasaita,
Fadawan dake bayan su ne suke amsawa da cewa Yarima ya amsa ya kuma gaishe ku,

Sulaim ne yace naga taron Meye akeyi ne?

Sultan yace akwai taron murnar dawowa ta masarauta gobe sannan akwai Hawa wanda za ayi ni zan gabatar da guda ɗaya,

Idan muka koma zanyi maka bayanin yadda taron zai kasance,

Kallon ko ina na masarautar Sulaim ya shiga yi tamkar yau yafara ganin ta shidai yana son irin gine ginan masarauta suna bashi sha'awa,

Dogayen gine gine ne irin nada da kuma soraye irin na masarauta saidai an sabunta wannan ginin ai maida komai na zamani amma batare da an rushe wancan na asalin ba ko wane gini yana da zane irin nasa da kwalliyar sa da kuma irin ginin dutsan nan da akeyi, wani irin ƙaton zaki ne na ƙarfe launin zinare a tsakiyar masarautar idan mutum bai taba zuwa ba idan ya gani sai yabashi tsoro ya zanu sosai zakin,

Sosai gwaggo Murja taji daɗin ganin jikan nata wato Sulaim,

Saida suka gaisa sosai sannan tasa aka gabatar musu da abinci kala kala irin na gargajiya,

Kallon su gwaggo murjan tayi sannan tace kudai ga kunan kunzama tuzurai amma babu mai aure acikin ku sai jajayen kunnuwa kamar ƙosai,

Kai Sultan da ina ganin kamar kaine za kayi sai kasa shi ahanya amma naga duk tafiyar Taku ɗaya,

Idan ma kun rasa masu son nakune to ai akwai ƴan mata kala kala ni sai na samo muku,

Murmushi Yarima Sultan yayi saboda dama sun saba sukan ɗan taɓa wasan jika da kaka duk da ba kakar sa bace da ko ganin shi ba tayi amma sanadiyyar Sulaim suka saba,

shi ko Sulaim ɗaure fuska yayi tamkar an aiko masa da saƙon mutuwa shifa baya son zancan aure kwata kwata idan ma aka fiye yi masa tashi yake fice,

Sultan ne yace to aini nafaɗa miki saidai ki hakura da auran baba waziri ki aure ni don ni idan bakeba to gaskiya saida kisamomin wata kamar ke don ni haryanzu banga matar aure ba kuma bazan iya zama da Yarin yaba,

Dariya sosai gwaggo murja tayi kafin tace to bari kaji nafaɗa maka idan ma aka nemi mata kane ma tun da wuri saboda nida iliyasu waziri mutuwa ce kadai zata rabamu,

Shima dariyar yayi har kyawawan haƙoran sa farare tasss suka bayyana ga wata siririyar wushirya a tsakanin hakuran Yarima Sultan,

To shikenan idan lokaci yayi zamuyi ne nida amini na,

Eemm gwaggo murja tace tare da taɓe baki yo shi wannan aminin naka gashinan wani dunkum dashi kullum rai ahaɗe babu annuri a fuskar sa ba dole ma ya rasa matar aure ba yanzu daga maganar aure ya tashi yawani ƙara haɗe fuska,

Shiru Yarima sultan yayi don shima yakai geji a maganar tasa kuma shi idan zai ji antaɓa masa Sulaim to duk sai yaji babu daɗi,
Chapter 27 · 0% Book details