Sashe 98
Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dadi gun mami kamar ta goyesu haka ta dinga ji,cooler uku ta yiwa mamin na duk abinda ta dafa wa abdallan,kusan awa daya suna hirarau tare daga baya ta tasgi don basu guri su gana su biyu,don tsakanin da da uwa akwai sirri(qalubalenmu mata,sai kuje gaida uwar miji keda mai gida ki musu qifi qifi a tsakiya idan kika san uwar miji mai kawaici wadda ba zata iya ce miki ki matsa ki basu guri su gana ba,ke kuma ba hankali,na minti goma ba zaki iya matsawa ki basu guri ba,ta yiwuwu akwai maganar da alokacin takeso suyi da danta,don Allah mata mu gyara,koke ya yiwa haka keda mahaifiyarki ai bazakiji dadi ba)
mamin ce ta tambayeta ina zuwa
''zanje mu gaisa da mero ne''
''to...to,bata kuwa dade da barin nan din ba,sai da na korata ma tukun''tana murmushi ta sulale ta fice
Fes ta taras da meron da bangarenta,bisa dukkan alamu training na mami ne,tayi kyau da ita ta fara gogewa,haka nan fatarta ta qara kyau,kallo ta tarar da su sunayi ita da labaran din,suka gaisa sai ya miqe ya fice ya basu guri,murna mero ta dinga yi sosai ta dauko wannan ta kawowa maryam,ta rakito wancan ta bata har sai data ce ya isa,sun dan jima suna hira tana sake wayar mata da kai kan wasu abubuwan da tasan ta fita waye wa akansu,sai da ta kusa awa guda sannan labaran ya shigo yace mai gida na magana zasu wuce,kamar kada ta tafi haka mero taji tace amma zata zo itama taga gidan takwaranta,dariya tayi tace shikenan sai tazo din
A waiting parlour ta taddasu tsaye da mami,sai data rakasu har bakin mota,abdallah ya dubi mamin
''badai wata matsala ko mami zamanku da su labaran''murmushi tayi
''wallahi ko kadan,basu da matsala kam,ina jin dadin zama da alhamdulillahi''ya gyada kansa yace
''masha Allahu,mami sai da safe,muna ta missing dinki mami''murmushi tayi
''gwara ai kusan gurma ya kamaku da haka zaku saba ai''ta dube maryam da kanta ke qasa tace
''diyata ku gaida gida tinda qarfi da yaji sai kinyi surukuta da ni bayan nace ni bana surukutar,ki kula da kanki,kaima ka kulamin da ita,Allah yayi muku albarka''ameen suka amsa baki daya
Sai daya tsaya da ita a hanya ya mata siyayyar kayan maqulashe,qememe yace tayi zamanta a motar basai ta fito ba
''zan iya hadiyar zuciya fa idan kika fito wani ya kalleki,ke Allah zan iya mutuwa maryam a kanki,kishi ne da ni sosai,qaunarki ce tamin yawa,ba qaramin kamu ta yimin ba fa''dariya ta qyalqyale da ita''anya my kishin nan naka bai yawa ba''
ido ya zaro
''waya gaya miki?,bakisan yadda sahabbai keda kishi bane?,duk kishin nan nawa baikai nasu ba,kuma ma ai dole na kasance mai kishi saboda annabi muhammad S,A,W,yace maras kishin iyalinsa (addayyus)bazai shiga aljanna ba''kai ta gyada ta saka tafin hannunta a nasa tace
''gaskiya ne,sadaqa rasulul kareem,zan taya ka kaucewa duk wani abun da zai sanya kishinka motsawa RUHINA''
''na gode RAYUWATA''ya bata amsa cike da shauqinta
Sai kusan sha daya da rabi na dare suka koma gidan,da wani kasalallen tuqi ya dinga yi suka dinga hirar soyayya abinsu cikin motar kafin sukai gida
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶6⃣7⃣
*Daga abu zarril ghifari R.A yace:Manzan Allah S A W yace da ni:((ka ka wulaqanta wani abu daga cikin kyakkyawan aiki komai qanqantarsa,koda haduwa da dan uwanka ka sakar masa fuska ne(kayi masa murmushi)*
*Daga barraa,dan Aaazib R.A yace:Manzan Allah S A W yace:((babu musulmai biyu da zasu hadu suyi MUSABAHA face sai Allah ya gafarta musu zunubansu kafin su rabu))*
Gida ne suka taru suka ginashin mai cike da ni'ima qauna soyayya da kwanciyar hankali,wanda tsabar kula da haqqin juna wanda Allah ya dorawa kowannensu shine sila,kowa na qoqarin sauke haqqin dan uwanshi a kansa ua kuma qara da kyautatawa jin qai qauna da rahama irin wadda Allah ke sanyata tsakanin ma'aurata,kamar yadda abdallah ya sake tabbatarwa kanshi yahi dace da *macen qwarai* wadda har *ABADAN* bazai iya rabuwa da ita ba haka itama maryam anata bangaren,tabbas babu shakka *abdallah kyautar Allah ne*,hikimar ubangiji mai yawace,wato alkhairi ke tafe da ita,jinkirin auren da ya mata ashe shi kadai yasan manufarsa ta yin hakan,ba shakka shine sarki gagara misali,komai da yayi kan bawansa akwai manufarsa a ciki,saidai kai ajizanci da son zuciya irin taka ya hanaka gani
*************
_BAYAN WATA SHIDDA_
Haka rayuwa taci gaba da jujjuya musu cikin hikima ta ubangiji,rayuwa ce suke yinta mai cike farinciki da qaruwar arziqi,tsantsar qauna da fahimtar juna a tsakaninsu,hakanan ci gaba kala kala suna ganinshi,albarkacin tsaftatacciyar zuciya taimako da qaunar jama'a da suke da ahi wanda raino ne irin na *MAMI* kusan a gurinta suka nashi wanann aqidar
Tuni abdallah yayi gini gini mai kyau da tsari mai dauke da part biyu,cikin tsarinsa da halinsa maryam sam batasan ginon waye,ba sai bayan da ya kammala taji ana gayyatarta tariya,gida ne da ya mallakawa mahaifin maryam wato malam ahmadu wanda aka fara kira da alhj amadu dalilin kaishi umara da yayi shida mama,godiya tazo ta masa ya rufe bakinta da zafafan kises yace bai buqatar kowacce godiya daga bakinta,shi a rayuwa sun gama masa komai mama da baaba da suka haifa masa ita
Maama da baaba huwaila ne kawai suka tare a ciki don a taohon gidan aka bar inna hadiza da jamila da bintu,don tuni malam amadu ya tsawatar wa dukka wacce take jin zata ci gaba da wasa da aurenta tana jeka ka dawo,matuqar kuwa ta kashe auren nata to saidai ta nemi gidan zama ba gidansa ba,yabi kowacce da jari daidai qarfinsa,suntsota kuwa don bai taba musu bore irin wanan ba don haka kowacce tayi luf a gidanta,abun dama akwai raahin kwaba da hantara tunda sunsan idan sun dawo din ana maraba da su,musamman yaran inna huwaila wanda itama bayan babansu yayi nashi jan kunnen itama ta dora da nata
Hisham kuwa da lubabatu tuni zance yayi nisa,don tuni ma har manya sun shiga maganar an kai kudin aurensu,hakan,na qaramin dadi ya yiwa baaba huwaila ba,girma da qimar maryam da mama suka dadu cikin idanunta,babu shakka sanin masoyi sai Allah,wanda ka tsana kake ganin bai sonka wani lokaco baka gane cewa ashe masoyinka ne sai tafiya tayi tafiya
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
kamar kowanne lokaci kafin dawowar abdallahn da awa daya ta kammala komai,haka ma yauma take ga maryam,bayan ta kammala ayyukanta ta fada wanka,lokaci ta bata mai uawa gaban madubi tana tsara kwalliya kana ta fidda wata iriyar riga mai bazar,tafe take da breast,cup daga sama hakanan hannun shimi gareta,bayan rigar kusan rabinsa a wawake yake,dududu rigar iya karta gwiwa,kusan kullum shigar maryam kenan don qa'idar abdallah ce,bata sanya manya kaya sai idan zasuyi baqi koda rana idan baya nan,amma ko dawowar rana yayi tofa sai anmasa kwalliya da shigarsa ya gani kana zai koma,saidai ko idan zasu fita unguwa,wannan kam harda hijabinta don baya taba barinta ta fita da mayafi koda wasa
Alarm da taji shi ya tabbatar mata ya dawo,ta sake duban kanta ta tabbatar komai yayi daidao,ita kanta tayaba irin kyawun da tayi,ta rasa me yasa take dada wani kyau tare da cika,har wani kumatu ta fara yi,tayi azamar sake fesa turare da gaggawa ta fito,saidai tana zuwa bakin qofar falon ta sauya taku
Zaune yake cikin motaf kamar kowanne lokaci shi daya ne,dama idan taji alarm din ta san cewa security dinsa sun tafi saura shi kadai sai ta fito,a bayan motar yake a zaune da alamu yauma driver ne ya tuqashi,sometimes idan suka taho da securityn nashi yakan karbi driving dinne ya ja suna zaune,wannan na daya daga cikin abinda ke sake burge maryam game da abdallah
Tunda ta taho din ya zuba mata idanu ko qiftawa bayayi,a kullum kwanan duniya sake linka masa qaunarta ake cikin zuciyarshi,har ta qaraso bai sani ba sai data sa bakinta ta hure masa ido,ya saki murmushi ya jawota ta fado cikin motar ya rungumeta
''hala yauma a gajiye kake *shariki hayateey*gaskiya idan basuyi wasa ba kwanan nan zan hana wa kowa ganinka,akan me za'adinga wahalmin da *zuciyata*''ta fada a shagwabe
ajiyar zuciya ya saki yana murmushi
''sosai kuwa baby,amma wai...baby ina da tambaya?''yayi maganar yana bin loko da saqo na jikinta yana shanshanawa saboda irin qamshinta dake gigita shi
''uhmmm,shariky ina jinka''tayi maganar itama tana sake qwaqumeshi
''wai don Allah ya zanyi na ragewa kaina sonki cikin zuciyata ne,yana neman fa ya hallakani''dariya ta qyalqyale da ita tana sake nadewa cikin jikinsa''saidai a qara maka wani son kan wanda kake min my''ido ya dan zaro,cikin wasa yace
''baby.....idan naci gaba da yi miki irin wanann son ai sai ki hanani qara aure''sai ta hade rai ta zame jikinta daga nashi ckkin fushi ta fara qlqarin fitowa a motar,riqeta yayi yana dariyq ciki ciki don yasan ya gama tabota
''ki jirani mana baby mu tafi tare''·
''ka bari ifan ka sake auren sai ta jiraka,tunda ni nayi maka kadan''ta zame da squri ta fice,shima da sauri ya fito yana dariya qasa qasa yadda ba zata ji shi ba,sai ya jingina da motar yana qare mata kallo yadda take tafiya da sauri sauri,abun sai ya burgeshi,'yar figigiyar rigarta ta mata kyau,hakanan yaga ta sake wani cika duk wani hips nata ya fito,sai da ta qaraci saurinta cikin takun da basu gaza biyar ba ya damqota,cak ya dagata tana eutsil wutsil dq qafa tana tureshi ya shige da ita
ya sani a bisa al'adarta kafin ya dawo ta hada masa ruwan wanka don haka ya wuce da ita kanshi tsaye toilet din,tuni ido ya soma raina fata don ta gano qarshen zancan,yau kam kwalliyarta saidai ta sake wata,da sauri tace da shi
''nifa na gane wasa kake min,pls bawan Allah ka saukeni,zan tayaka ma wankan''dariya ta bashi ya dubeta
''ai kin riga kin makara,kin manta ne babu fushi a zamanmu,you break the rule,and the rule will break you as usual''yana gama fada ya sanyata tsundum cikin bathtube kana ya fidda takalmin qafarsa da safa ya cire suit din jikinsa ya bita ciki,sai da suka gama shan qaunarsu kafin suyi wankan su fito
mamin ce ta tambayeta ina zuwa
''zanje mu gaisa da mero ne''
''to...to,bata kuwa dade da barin nan din ba,sai da na korata ma tukun''tana murmushi ta sulale ta fice
Fes ta taras da meron da bangarenta,bisa dukkan alamu training na mami ne,tayi kyau da ita ta fara gogewa,haka nan fatarta ta qara kyau,kallo ta tarar da su sunayi ita da labaran din,suka gaisa sai ya miqe ya fice ya basu guri,murna mero ta dinga yi sosai ta dauko wannan ta kawowa maryam,ta rakito wancan ta bata har sai data ce ya isa,sun dan jima suna hira tana sake wayar mata da kai kan wasu abubuwan da tasan ta fita waye wa akansu,sai da ta kusa awa guda sannan labaran ya shigo yace mai gida na magana zasu wuce,kamar kada ta tafi haka mero taji tace amma zata zo itama taga gidan takwaranta,dariya tayi tace shikenan sai tazo din
A waiting parlour ta taddasu tsaye da mami,sai data rakasu har bakin mota,abdallah ya dubi mamin
''badai wata matsala ko mami zamanku da su labaran''murmushi tayi
''wallahi ko kadan,basu da matsala kam,ina jin dadin zama da alhamdulillahi''ya gyada kansa yace
''masha Allahu,mami sai da safe,muna ta missing dinki mami''murmushi tayi
''gwara ai kusan gurma ya kamaku da haka zaku saba ai''ta dube maryam da kanta ke qasa tace
''diyata ku gaida gida tinda qarfi da yaji sai kinyi surukuta da ni bayan nace ni bana surukutar,ki kula da kanki,kaima ka kulamin da ita,Allah yayi muku albarka''ameen suka amsa baki daya
Sai daya tsaya da ita a hanya ya mata siyayyar kayan maqulashe,qememe yace tayi zamanta a motar basai ta fito ba
''zan iya hadiyar zuciya fa idan kika fito wani ya kalleki,ke Allah zan iya mutuwa maryam a kanki,kishi ne da ni sosai,qaunarki ce tamin yawa,ba qaramin kamu ta yimin ba fa''dariya ta qyalqyale da ita''anya my kishin nan naka bai yawa ba''
ido ya zaro
''waya gaya miki?,bakisan yadda sahabbai keda kishi bane?,duk kishin nan nawa baikai nasu ba,kuma ma ai dole na kasance mai kishi saboda annabi muhammad S,A,W,yace maras kishin iyalinsa (addayyus)bazai shiga aljanna ba''kai ta gyada ta saka tafin hannunta a nasa tace
''gaskiya ne,sadaqa rasulul kareem,zan taya ka kaucewa duk wani abun da zai sanya kishinka motsawa RUHINA''
''na gode RAYUWATA''ya bata amsa cike da shauqinta
Sai kusan sha daya da rabi na dare suka koma gidan,da wani kasalallen tuqi ya dinga yi suka dinga hirar soyayya abinsu cikin motar kafin sukai gida
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶6⃣7⃣
*Daga abu zarril ghifari R.A yace:Manzan Allah S A W yace da ni:((ka ka wulaqanta wani abu daga cikin kyakkyawan aiki komai qanqantarsa,koda haduwa da dan uwanka ka sakar masa fuska ne(kayi masa murmushi)*
*Daga barraa,dan Aaazib R.A yace:Manzan Allah S A W yace:((babu musulmai biyu da zasu hadu suyi MUSABAHA face sai Allah ya gafarta musu zunubansu kafin su rabu))*
Gida ne suka taru suka ginashin mai cike da ni'ima qauna soyayya da kwanciyar hankali,wanda tsabar kula da haqqin juna wanda Allah ya dorawa kowannensu shine sila,kowa na qoqarin sauke haqqin dan uwanshi a kansa ua kuma qara da kyautatawa jin qai qauna da rahama irin wadda Allah ke sanyata tsakanin ma'aurata,kamar yadda abdallah ya sake tabbatarwa kanshi yahi dace da *macen qwarai* wadda har *ABADAN* bazai iya rabuwa da ita ba haka itama maryam anata bangaren,tabbas babu shakka *abdallah kyautar Allah ne*,hikimar ubangiji mai yawace,wato alkhairi ke tafe da ita,jinkirin auren da ya mata ashe shi kadai yasan manufarsa ta yin hakan,ba shakka shine sarki gagara misali,komai da yayi kan bawansa akwai manufarsa a ciki,saidai kai ajizanci da son zuciya irin taka ya hanaka gani
*************
_BAYAN WATA SHIDDA_
Haka rayuwa taci gaba da jujjuya musu cikin hikima ta ubangiji,rayuwa ce suke yinta mai cike farinciki da qaruwar arziqi,tsantsar qauna da fahimtar juna a tsakaninsu,hakanan ci gaba kala kala suna ganinshi,albarkacin tsaftatacciyar zuciya taimako da qaunar jama'a da suke da ahi wanda raino ne irin na *MAMI* kusan a gurinta suka nashi wanann aqidar
Tuni abdallah yayi gini gini mai kyau da tsari mai dauke da part biyu,cikin tsarinsa da halinsa maryam sam batasan ginon waye,ba sai bayan da ya kammala taji ana gayyatarta tariya,gida ne da ya mallakawa mahaifin maryam wato malam ahmadu wanda aka fara kira da alhj amadu dalilin kaishi umara da yayi shida mama,godiya tazo ta masa ya rufe bakinta da zafafan kises yace bai buqatar kowacce godiya daga bakinta,shi a rayuwa sun gama masa komai mama da baaba da suka haifa masa ita
Maama da baaba huwaila ne kawai suka tare a ciki don a taohon gidan aka bar inna hadiza da jamila da bintu,don tuni malam amadu ya tsawatar wa dukka wacce take jin zata ci gaba da wasa da aurenta tana jeka ka dawo,matuqar kuwa ta kashe auren nata to saidai ta nemi gidan zama ba gidansa ba,yabi kowacce da jari daidai qarfinsa,suntsota kuwa don bai taba musu bore irin wanan ba don haka kowacce tayi luf a gidanta,abun dama akwai raahin kwaba da hantara tunda sunsan idan sun dawo din ana maraba da su,musamman yaran inna huwaila wanda itama bayan babansu yayi nashi jan kunnen itama ta dora da nata
Hisham kuwa da lubabatu tuni zance yayi nisa,don tuni ma har manya sun shiga maganar an kai kudin aurensu,hakan,na qaramin dadi ya yiwa baaba huwaila ba,girma da qimar maryam da mama suka dadu cikin idanunta,babu shakka sanin masoyi sai Allah,wanda ka tsana kake ganin bai sonka wani lokaco baka gane cewa ashe masoyinka ne sai tafiya tayi tafiya
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
kamar kowanne lokaci kafin dawowar abdallahn da awa daya ta kammala komai,haka ma yauma take ga maryam,bayan ta kammala ayyukanta ta fada wanka,lokaci ta bata mai uawa gaban madubi tana tsara kwalliya kana ta fidda wata iriyar riga mai bazar,tafe take da breast,cup daga sama hakanan hannun shimi gareta,bayan rigar kusan rabinsa a wawake yake,dududu rigar iya karta gwiwa,kusan kullum shigar maryam kenan don qa'idar abdallah ce,bata sanya manya kaya sai idan zasuyi baqi koda rana idan baya nan,amma ko dawowar rana yayi tofa sai anmasa kwalliya da shigarsa ya gani kana zai koma,saidai ko idan zasu fita unguwa,wannan kam harda hijabinta don baya taba barinta ta fita da mayafi koda wasa
Alarm da taji shi ya tabbatar mata ya dawo,ta sake duban kanta ta tabbatar komai yayi daidao,ita kanta tayaba irin kyawun da tayi,ta rasa me yasa take dada wani kyau tare da cika,har wani kumatu ta fara yi,tayi azamar sake fesa turare da gaggawa ta fito,saidai tana zuwa bakin qofar falon ta sauya taku
Zaune yake cikin motaf kamar kowanne lokaci shi daya ne,dama idan taji alarm din ta san cewa security dinsa sun tafi saura shi kadai sai ta fito,a bayan motar yake a zaune da alamu yauma driver ne ya tuqashi,sometimes idan suka taho da securityn nashi yakan karbi driving dinne ya ja suna zaune,wannan na daya daga cikin abinda ke sake burge maryam game da abdallah
Tunda ta taho din ya zuba mata idanu ko qiftawa bayayi,a kullum kwanan duniya sake linka masa qaunarta ake cikin zuciyarshi,har ta qaraso bai sani ba sai data sa bakinta ta hure masa ido,ya saki murmushi ya jawota ta fado cikin motar ya rungumeta
''hala yauma a gajiye kake *shariki hayateey*gaskiya idan basuyi wasa ba kwanan nan zan hana wa kowa ganinka,akan me za'adinga wahalmin da *zuciyata*''ta fada a shagwabe
ajiyar zuciya ya saki yana murmushi
''sosai kuwa baby,amma wai...baby ina da tambaya?''yayi maganar yana bin loko da saqo na jikinta yana shanshanawa saboda irin qamshinta dake gigita shi
''uhmmm,shariky ina jinka''tayi maganar itama tana sake qwaqumeshi
''wai don Allah ya zanyi na ragewa kaina sonki cikin zuciyata ne,yana neman fa ya hallakani''dariya ta qyalqyale da ita tana sake nadewa cikin jikinsa''saidai a qara maka wani son kan wanda kake min my''ido ya dan zaro,cikin wasa yace
''baby.....idan naci gaba da yi miki irin wanann son ai sai ki hanani qara aure''sai ta hade rai ta zame jikinta daga nashi ckkin fushi ta fara qlqarin fitowa a motar,riqeta yayi yana dariyq ciki ciki don yasan ya gama tabota
''ki jirani mana baby mu tafi tare''·
''ka bari ifan ka sake auren sai ta jiraka,tunda ni nayi maka kadan''ta zame da squri ta fice,shima da sauri ya fito yana dariya qasa qasa yadda ba zata ji shi ba,sai ya jingina da motar yana qare mata kallo yadda take tafiya da sauri sauri,abun sai ya burgeshi,'yar figigiyar rigarta ta mata kyau,hakanan yaga ta sake wani cika duk wani hips nata ya fito,sai da ta qaraci saurinta cikin takun da basu gaza biyar ba ya damqota,cak ya dagata tana eutsil wutsil dq qafa tana tureshi ya shige da ita
ya sani a bisa al'adarta kafin ya dawo ta hada masa ruwan wanka don haka ya wuce da ita kanshi tsaye toilet din,tuni ido ya soma raina fata don ta gano qarshen zancan,yau kam kwalliyarta saidai ta sake wata,da sauri tace da shi
''nifa na gane wasa kake min,pls bawan Allah ka saukeni,zan tayaka ma wankan''dariya ta bashi ya dubeta
''ai kin riga kin makara,kin manta ne babu fushi a zamanmu,you break the rule,and the rule will break you as usual''yana gama fada ya sanyata tsundum cikin bathtube kana ya fidda takalmin qafarsa da safa ya cire suit din jikinsa ya bita ciki,sai da suka gama shan qaunarsu kafin suyi wankan su fito