Sashe 95
Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Allah ya rufa asiri yana shiga bayi baaba uwani ta shigo,nan ta zauna tana yiwa maryam sannu da jiki,cike da kunya take amsa mata,lokacin da ya fito sannu da zuwa kawai ya yiwa baaba uwanin ya fice bayan ya jefi sahibar tasa da wani kallo mai cike da qauna da bege,baifi minti goma da fitar tasa ba siga wata nurse ta shigo,tace baaba uwani ta taso a nuna mata dakinta inda zata kwana,nan din akwai mai kwana da madam maryam din,bata musa ba ta bita don ba sanin tsarin asibitin tayi ba batasan duk plan din abdallah bane,sai data fice kana ya dawo dakin harda maida key kana ya shigo ya fidda kayan jikinsa ya bar singlet da three quater ya qarasa gaban plasma din dake jkkin bangovya dauki remote na reciever din,kansa tsaye ya dale gadon da maryam din ke kai a kwance bayan ya bata magungunanta ta sha,jikinsa ya janyota ya rungumeta tsam bayan ya sauya musu tasha zuwa mbc bollywood cikin sa'a suna film din geet,lumshe idonta tayi ta sake narkewa cikin jikinsa,don tana bala'in son film din,hakan ya qara mata shauqi ya kuma hanata cewa abdallah komai tana jinsa yana ta rage zafinsa a zafafe kamar zai hadiyeta,saidai data fuskanci zai sauya akala zata dakatar da shi,shikam ko hakan ma ya masa,ya fi masa ace baya kusa da ita
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
qarfe goma mami ta iso ta sallamesu bayan ta sake dubawa ta tabbatar da komai normal,gargadi kam abdallah yasha shi,har ya kasa daurewa ya dafe kansa qasa qasa ''abdallah ka shiga uku,Allah ne kadai gatanka''
''baka shiga uku ba sai ka sake ganganci na dauketa gaba daya lokacin zaka tabbatar ka shiga tara ma ba uku ba''bai zaton zata ji ba din haka ya fece ya bar musu dakin
Da wannan dama abdallah yayi amfani ya shirya tafiye tafiyensa don gyara duk wata harka ta kasuwancinsa da ta samu baraka kamar kamfanoninsa da sauransu,wadda su nene da ahalinta suka so yin tsallen badake a kanta,kwana goma ya tsara zaiyi,din baijin zai iya zama guri guda da maryam bai tsallake sharadin mami ba,ya tabbata kafin dawowarsa aidai ra warke,idaan yaso yaci duniyarsa da tsinke son ranshi,don da baaba uwani ra hadosu saboda ta kula da maryam din ta warke sarai kamar wata me jego inji abdallah
Ana jibi zai tafi yayi niyyar gaya mata,ita ke kawo masa abinci har sashensa,kamar ko wanne lokaci taci kwalliyarta tsaf cikin atamfa fitted gown,babu wata sura tata da bata bayyana ba,qamshin ta kawai ya isa ya daga maka hankali,yana cin abincin ne kawai amma duka hankalinsa na gareta,daga qarshe ma fita yayi daga kansa abinci ya tureshi ya miqa mata hannu,take ta taso cikin taku na daukar hankali ta qaraso gareshi,kan cinyarsa yayi mata masauki kana ya mannata da jikinsa ya saba aikin nasa na rage zafi,luf tayi tana karbar saqonnin da duk yake aika mata,cikin salo na jan magana yace
''ke kanki kina karbar saqonni na,amma yanzu da zance zamu fara lacture saikiyi tawaye''
aikam tuni ta zaro ido don har yanzu bata manta wuyar baya ba,narkewa tayi ta marairaice masa,cikin wata shishshiqa ta kissa tace masa
''amma ka sani fa my ban warke ba''
''i know,shi yasa nace gwara na danyi nesa duk da zuciya bafa so''sai tayi hanzarin juyowa ta dubeshi
''kayi nesa kuma,kamar yaya?''
girarsa ya dage mata ya kashe mata ido daya
''zanyi tafiya inje in gyara kamfanoni na da aka so durqusarwa,kwana goma in sha Allahu na kammala,kafin na dawo nasan kin warke kinga sai shiga aji da daukar lacture ko?''
Duk da ya bata kunya amma sai da ta sa masa kukan shagwaba''amma daga yin sati daya sai kace zakayi tafiya?kasan bazan juri rashin ganinka ba har kwana gona?.....nidai gaskiya.....gaskiya.....''ido ya lumshe shagwabarta na sake rudashi ne sosai
''nima haka my dear na,nasan halina,indai naci gaba da zama din bazan iya jurewa ba,idan kuma kin amince muci gaba da darasi to''sai kuma tayi luf bayan ta noqe kafada,dariya yasa mata yana fadin
''you see''
hannunta ya kama ya dora a qirjinsa daidai zuciyarsa yace
''kada diya na ta ta damu,kin manta zuciyarmu guda daya ce,nisan dake tsakaninmu ne kadai zai raba mu amma muna tare ne,koda mutuwa dayan yayi to muna tare,after all ma gwara nayi tafiyan tun yanzu,saboda idan aka wuce yanzu gaskiya bazan iya yinta ba,kinsan ni ba ragon malami bane,dali barce dai na samu raguwa''kai abdallah na kasheta da salonsa,sai ta kasa ce masa komai,ranar bara baro bangaren ba sai kusan sha daya
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Washegari sai ganin lubabatu tayi yasa andauko mata ita,tayi murna kam qwarai duk da cike take da kewar tafiyar tasa,mami ma da ya gaya mata cewa tayi idan maryam ta yarje masa yaje shikenan,don ta riga da ta sani tafiyar tasa ce kawai zata sa yabar mata maryam din ta warke yadda ya kamata
Kuka take sosai sai taji zuciyarta tayi matuqar quntata batason tafiyar tashi,bata taba sanin rabuwa da masoyi haka yake da daci ba sai yai,ashe haka matan da mazansu ke tafiye tafiye suje ji,tun hisham na matsa masa horn har ya gaji ya daina don ya bararraje a gabanta yanata faman aikin lallashi,so yaje yaga ba hawaye ko daya cikin idanunta amma hakan ya gagara,daga qarshe ya dubeta cikin karaya
''anya dear na ba haqura zanyi da tafiyar nan ba''da sauri ta girgiza kai
''nikam gwara kaje,sai gaba kuma mun sake watanni kace zaka je?,tab,aikam,nazan yarda ba''dariya taso bashi,sai ya hade hannayensu
''is ok,indai kina son na tafi to ki share hawayen kinji''da kai ta amsa masa ta fara sharewar yana tayata,sai da yaga fuskar tata tayi fes sanann ya ciro mata hijabi ya saka mata,ya kama hannunta suka sauko,ya dubi fuskarta yadda tasha kuka sai yayi sha'awar tsokanarata
''ashe maryama ta abdallah ce,ashe maryama na mutuwar son abdallah,ashe rabuwa da masoyi da daci''yayi maganar cikin salo na waqa,sai ta fara diddira qafafunta cikin shagwaba,baya yadan ja kana ya kama baki
''iyeeee,naga fa alamar yammata kin warke,irin wannan tsalle haka,kodai na fasa tafiyar nan na zauna aci gaba da daukan darasi mu tsinki fure sosai''ba qaramar dariya ya bata ba,abdallah badai iya tsoka na ba idan yaso,sai ta fada jikinsa cikin dariya,shima baiyi qasa a gwiwa ba ya tarbeta ya rungume abarsa tsam yana jin duminta da qamshin azababben turarenta,sai da ya gama bata hot kisses sannan suka fito
Tana kan kafadarsa daya kafadar tata rataye da briefcase dinshi haka suka jero har harabar gidan,bai damu da securities dinshi ko hisham dake tsaye agun ba ya sake qwaqume abarshi,duk da kunyar da take ji amma ya hanata motsawa a haka har suka isa motar da zasu tafi din,ko kallo hisham dake waje a tsaye shida lubabatu yana zabga masa harara bai isheshi ba,sake janyita yayi ta mata kiss a kumatu da goshinta,yasa dan yatsansa yana dauke mata hawayen da ya fara silalo mata
''no baby,no,hawayenki karyamin duk wani qwarin gwiwa yake,ki bar kukan nan haka,bari na gaya miki abunda zaki min qwaya dayq da zaisa na kuma gamsuwa lallai kina sona kuma kinyi kewata bayan tafiyata''bakinsa ya sanya a kunnenta cikin kashe murya da iya salon sace zuciya da tada tsohon miki yace
''kimin wani kyakkyawan tanadi yadda zamu bargaje amarcinmu sosai bayan dawowata,idan so samu ne ma mami taga alama,ki mata guzurin jika''wayyo kunya kashe maryam,sai ta maida kanta kafadarsa tana dariya qasa qasa
''zan baka mamaki kuwa,kasha kuruminka''itama ta maida masa cikin nata salon
'ido ya dan zaro yana murmushi
''Allah tawan,kai wlh ke ta musamman ce dear na''dariya suka saki tare a hankali
''kaga malam,idan an fasa tafiyar nan ne ka gaya min,don me zaka shanya mutane kuzo ku bude wa mutane filin soyayya''kunu abdallah ya dan sha
''kaga malam,ya zaka shiga haqqin masoya,miji da mata fa sai Allah,musamman ma ni da maryam kafi kowa sanin cewa mu na musamman ne,don haka ka shafa mana lafiya tsohon gauro kawai''dariya hisham ya fashe da ita
''dududu yaushe Allah ya 'yantaka,naga tare muke fama da gaurancinmu,har gwara ni na fika qarfin zuciya ma.....''
''ko yanzu Allah ya 'yantani dai na fika''yayi sautin katseshi don kada ya masa tonon silili yana yafito lubabatu dake can gefe tana kallonsu tana murmushi
''amana zan danqa miki,ki kularmin davrayuwata,idan har kika bata kulawa yadda ya dace ni kadai nasan tukuicin da zan miki,zan baki wannan tsohon gauron ki taimaki rayuwarshi''dukkansu sai da abdallahn ya basu dariya,itakam lubabatu hannu tasa ta rufe fuskarta
Wani dogon hot kiss ya bata wanda sai da yasa hisham da lubabatu dauke kan don kunya kana ya kama hannunta yana fadin
''ki kula min da kanki,zanyi kewarki fiye da kike tsammni ko hasashe,kana ki cikamin alqawari na idan na dawo''kai take daga masa kafin daga bisani itama ta juya tafin hannunshi ta sumbata,ita da lubabatun na tsaye har motocin suka kammala ficewa daga gidan security ya maida get din ya rufe.
. By
*mrs muhammad ce*👑 BH
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶6⃣6⃣
*An karbo daga abu hurairah,R.A yace: Manzan Allah S A W yace:((MUSULMI DAN UWAN MUSULMI NE,KADA YA HA'INCESHI,KADA YA MASA QARYA,KADA YA TABAR DA SHI,KADA YA WULAQANTASHI,KADA YA ZALUNCESHI,KADA YA TOZARTASHI,KOWANNE MUSULMI A KAN DAN UWANSA HARAMUN NE(YA TABA)MUTUNCINSA,DA DUKIYARSA,DA JININSA,TSORON ALLAH ANAN YAKE,(SAI ANNABIN RAHAMA YAYI NUNI DA QIRJINSA SAU UKU)YA ISHI MUTUM SHARRI YA WULAQANTA DAN UWANSA MUSULMI*
_Allah ka tsaremu,Allah ka tsaremu,Allah ka tsaremu 🙏🏽_
_qarin haske_
_ANTY SIS ta janyo hankali na game da wani abu cikin page din baya,wato da yawa makaranta sun dauka ina nufin sixs hours abdallah yayi a first night dinsu,ba haka nake nufi ba,ina nufin after sixs hours ya fahimci barnar da yayi,abinda nake nufi kenan,don bazaiyiwu mutum yayi sixs hours din yana abu daya ba kamar yadda anty sis kika ce,hakan yake,GODIYA NAKE_
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
qarfe goma mami ta iso ta sallamesu bayan ta sake dubawa ta tabbatar da komai normal,gargadi kam abdallah yasha shi,har ya kasa daurewa ya dafe kansa qasa qasa ''abdallah ka shiga uku,Allah ne kadai gatanka''
''baka shiga uku ba sai ka sake ganganci na dauketa gaba daya lokacin zaka tabbatar ka shiga tara ma ba uku ba''bai zaton zata ji ba din haka ya fece ya bar musu dakin
Da wannan dama abdallah yayi amfani ya shirya tafiye tafiyensa don gyara duk wata harka ta kasuwancinsa da ta samu baraka kamar kamfanoninsa da sauransu,wadda su nene da ahalinta suka so yin tsallen badake a kanta,kwana goma ya tsara zaiyi,din baijin zai iya zama guri guda da maryam bai tsallake sharadin mami ba,ya tabbata kafin dawowarsa aidai ra warke,idaan yaso yaci duniyarsa da tsinke son ranshi,don da baaba uwani ra hadosu saboda ta kula da maryam din ta warke sarai kamar wata me jego inji abdallah
Ana jibi zai tafi yayi niyyar gaya mata,ita ke kawo masa abinci har sashensa,kamar ko wanne lokaci taci kwalliyarta tsaf cikin atamfa fitted gown,babu wata sura tata da bata bayyana ba,qamshin ta kawai ya isa ya daga maka hankali,yana cin abincin ne kawai amma duka hankalinsa na gareta,daga qarshe ma fita yayi daga kansa abinci ya tureshi ya miqa mata hannu,take ta taso cikin taku na daukar hankali ta qaraso gareshi,kan cinyarsa yayi mata masauki kana ya mannata da jikinsa ya saba aikin nasa na rage zafi,luf tayi tana karbar saqonnin da duk yake aika mata,cikin salo na jan magana yace
''ke kanki kina karbar saqonni na,amma yanzu da zance zamu fara lacture saikiyi tawaye''
aikam tuni ta zaro ido don har yanzu bata manta wuyar baya ba,narkewa tayi ta marairaice masa,cikin wata shishshiqa ta kissa tace masa
''amma ka sani fa my ban warke ba''
''i know,shi yasa nace gwara na danyi nesa duk da zuciya bafa so''sai tayi hanzarin juyowa ta dubeshi
''kayi nesa kuma,kamar yaya?''
girarsa ya dage mata ya kashe mata ido daya
''zanyi tafiya inje in gyara kamfanoni na da aka so durqusarwa,kwana goma in sha Allahu na kammala,kafin na dawo nasan kin warke kinga sai shiga aji da daukar lacture ko?''
Duk da ya bata kunya amma sai da ta sa masa kukan shagwaba''amma daga yin sati daya sai kace zakayi tafiya?kasan bazan juri rashin ganinka ba har kwana gona?.....nidai gaskiya.....gaskiya.....''ido ya lumshe shagwabarta na sake rudashi ne sosai
''nima haka my dear na,nasan halina,indai naci gaba da zama din bazan iya jurewa ba,idan kuma kin amince muci gaba da darasi to''sai kuma tayi luf bayan ta noqe kafada,dariya yasa mata yana fadin
''you see''
hannunta ya kama ya dora a qirjinsa daidai zuciyarsa yace
''kada diya na ta ta damu,kin manta zuciyarmu guda daya ce,nisan dake tsakaninmu ne kadai zai raba mu amma muna tare ne,koda mutuwa dayan yayi to muna tare,after all ma gwara nayi tafiyan tun yanzu,saboda idan aka wuce yanzu gaskiya bazan iya yinta ba,kinsan ni ba ragon malami bane,dali barce dai na samu raguwa''kai abdallah na kasheta da salonsa,sai ta kasa ce masa komai,ranar bara baro bangaren ba sai kusan sha daya
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Washegari sai ganin lubabatu tayi yasa andauko mata ita,tayi murna kam qwarai duk da cike take da kewar tafiyar tasa,mami ma da ya gaya mata cewa tayi idan maryam ta yarje masa yaje shikenan,don ta riga da ta sani tafiyar tasa ce kawai zata sa yabar mata maryam din ta warke yadda ya kamata
Kuka take sosai sai taji zuciyarta tayi matuqar quntata batason tafiyar tashi,bata taba sanin rabuwa da masoyi haka yake da daci ba sai yai,ashe haka matan da mazansu ke tafiye tafiye suje ji,tun hisham na matsa masa horn har ya gaji ya daina don ya bararraje a gabanta yanata faman aikin lallashi,so yaje yaga ba hawaye ko daya cikin idanunta amma hakan ya gagara,daga qarshe ya dubeta cikin karaya
''anya dear na ba haqura zanyi da tafiyar nan ba''da sauri ta girgiza kai
''nikam gwara kaje,sai gaba kuma mun sake watanni kace zaka je?,tab,aikam,nazan yarda ba''dariya taso bashi,sai ya hade hannayensu
''is ok,indai kina son na tafi to ki share hawayen kinji''da kai ta amsa masa ta fara sharewar yana tayata,sai da yaga fuskar tata tayi fes sanann ya ciro mata hijabi ya saka mata,ya kama hannunta suka sauko,ya dubi fuskarta yadda tasha kuka sai yayi sha'awar tsokanarata
''ashe maryama ta abdallah ce,ashe maryama na mutuwar son abdallah,ashe rabuwa da masoyi da daci''yayi maganar cikin salo na waqa,sai ta fara diddira qafafunta cikin shagwaba,baya yadan ja kana ya kama baki
''iyeeee,naga fa alamar yammata kin warke,irin wannan tsalle haka,kodai na fasa tafiyar nan na zauna aci gaba da daukan darasi mu tsinki fure sosai''ba qaramar dariya ya bata ba,abdallah badai iya tsoka na ba idan yaso,sai ta fada jikinsa cikin dariya,shima baiyi qasa a gwiwa ba ya tarbeta ya rungume abarsa tsam yana jin duminta da qamshin azababben turarenta,sai da ya gama bata hot kisses sannan suka fito
Tana kan kafadarsa daya kafadar tata rataye da briefcase dinshi haka suka jero har harabar gidan,bai damu da securities dinshi ko hisham dake tsaye agun ba ya sake qwaqume abarshi,duk da kunyar da take ji amma ya hanata motsawa a haka har suka isa motar da zasu tafi din,ko kallo hisham dake waje a tsaye shida lubabatu yana zabga masa harara bai isheshi ba,sake janyita yayi ta mata kiss a kumatu da goshinta,yasa dan yatsansa yana dauke mata hawayen da ya fara silalo mata
''no baby,no,hawayenki karyamin duk wani qwarin gwiwa yake,ki bar kukan nan haka,bari na gaya miki abunda zaki min qwaya dayq da zaisa na kuma gamsuwa lallai kina sona kuma kinyi kewata bayan tafiyata''bakinsa ya sanya a kunnenta cikin kashe murya da iya salon sace zuciya da tada tsohon miki yace
''kimin wani kyakkyawan tanadi yadda zamu bargaje amarcinmu sosai bayan dawowata,idan so samu ne ma mami taga alama,ki mata guzurin jika''wayyo kunya kashe maryam,sai ta maida kanta kafadarsa tana dariya qasa qasa
''zan baka mamaki kuwa,kasha kuruminka''itama ta maida masa cikin nata salon
'ido ya dan zaro yana murmushi
''Allah tawan,kai wlh ke ta musamman ce dear na''dariya suka saki tare a hankali
''kaga malam,idan an fasa tafiyar nan ne ka gaya min,don me zaka shanya mutane kuzo ku bude wa mutane filin soyayya''kunu abdallah ya dan sha
''kaga malam,ya zaka shiga haqqin masoya,miji da mata fa sai Allah,musamman ma ni da maryam kafi kowa sanin cewa mu na musamman ne,don haka ka shafa mana lafiya tsohon gauro kawai''dariya hisham ya fashe da ita
''dududu yaushe Allah ya 'yantaka,naga tare muke fama da gaurancinmu,har gwara ni na fika qarfin zuciya ma.....''
''ko yanzu Allah ya 'yantani dai na fika''yayi sautin katseshi don kada ya masa tonon silili yana yafito lubabatu dake can gefe tana kallonsu tana murmushi
''amana zan danqa miki,ki kularmin davrayuwata,idan har kika bata kulawa yadda ya dace ni kadai nasan tukuicin da zan miki,zan baki wannan tsohon gauron ki taimaki rayuwarshi''dukkansu sai da abdallahn ya basu dariya,itakam lubabatu hannu tasa ta rufe fuskarta
Wani dogon hot kiss ya bata wanda sai da yasa hisham da lubabatu dauke kan don kunya kana ya kama hannunta yana fadin
''ki kula min da kanki,zanyi kewarki fiye da kike tsammni ko hasashe,kana ki cikamin alqawari na idan na dawo''kai take daga masa kafin daga bisani itama ta juya tafin hannunshi ta sumbata,ita da lubabatun na tsaye har motocin suka kammala ficewa daga gidan security ya maida get din ya rufe.
. By
*mrs muhammad ce*👑 BH
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶6⃣6⃣
*An karbo daga abu hurairah,R.A yace: Manzan Allah S A W yace:((MUSULMI DAN UWAN MUSULMI NE,KADA YA HA'INCESHI,KADA YA MASA QARYA,KADA YA TABAR DA SHI,KADA YA WULAQANTASHI,KADA YA ZALUNCESHI,KADA YA TOZARTASHI,KOWANNE MUSULMI A KAN DAN UWANSA HARAMUN NE(YA TABA)MUTUNCINSA,DA DUKIYARSA,DA JININSA,TSORON ALLAH ANAN YAKE,(SAI ANNABIN RAHAMA YAYI NUNI DA QIRJINSA SAU UKU)YA ISHI MUTUM SHARRI YA WULAQANTA DAN UWANSA MUSULMI*
_Allah ka tsaremu,Allah ka tsaremu,Allah ka tsaremu 🙏🏽_
_qarin haske_
_ANTY SIS ta janyo hankali na game da wani abu cikin page din baya,wato da yawa makaranta sun dauka ina nufin sixs hours abdallah yayi a first night dinsu,ba haka nake nufi ba,ina nufin after sixs hours ya fahimci barnar da yayi,abinda nake nufi kenan,don bazaiyiwu mutum yayi sixs hours din yana abu daya ba kamar yadda anty sis kika ce,hakan yake,GODIYA NAKE_