← Book details Abadan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 103

Sashe 17

Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

teburin mamin yayi zamanshi yaja laptop dinta yana danne danne ya barta nan a tsaye,a haka mamin ta kammala sallarta ta shafa addu'o'inta
''sannu maryama ya akayi kunama ta sami abdallah?''mamin ta fada cikin kulawa tana linke sallayarta
''tsautsayi ne mami''taji abdallah ya amshe zancan yayin da tayi duru duru tana tsaka da neman amsar da zata bawa mamin
''Allah ya tsare gaba to,amma ya kamata ka daina zuwa gun da ta samekan,don nasan bazai wuce cikin garden ba''ta fada tana hada allurai cikin syringe

maryama tsayawa kawai tayi tana kallon yadda abdallan keta marairaita kamar qanqanin yaro,ita abun ma kunya ya dinga bata,amma shikam ta fuskanci ko ajikinshi wai an tsikari kakkausa
''wannan matarshi zata sha fama da shagwaba,mami duka ta sangartashi''tayi gulmarshi cikin zuciyarta,da sun hada ido sai ya maka mata harara hakan ya sanya ta dauke kanta ta maida kan dan wani qaramin frame me masifar kyau dake kafe kan table din mamin,hoton wani yaro ne wanda bazai haura shekaru takwas ba cikin shigar tazarce da hula da takalmi sawu ciki,ko shakka babu wanna hoton abdallah ne lokacin quruciyarshi,kyawunshi ba loka in girmanshi ne kawai ba kyawu ne na tun usuli

ya lura hoton take kallo don haka ya miqa hannu ya tuntsurar da shi,ya dan bada qara sakamakon haduwarshi da table din har sai da mami ta dago ta dubeshi sannan ta dubi frame din,ta fuskanci abunda yake nufi don haka murmushi kawai tayi can qasan ranta taci gaba da abunda take

bayan mamin ta kammala bashi duka wani taimako na kashe radadi da kuma tsaida dafin sai ta hada mishi da magani,minti goma tsakani mami tace ya taahi su wuce amma sai ya marairaice kan cewa bari ya huta,wayarshi dake gefan system din mami ta dauki kida,kamar bazai daga ba amma yana dubawa yayi hanzarin dagwa
''sir,munga alhj haladu uba mai qusa yanzu cikin asibitin nan''abinda aka fada kenan da ya sanyashi hanzarin miqewa,mami ta dubeshi
''lafiya abdallah?''
''mami ina zuwa,just twenty minute''bai tsaya sauraron komai ba ya fice daga office din,yayin da mamin ta bishi da kallo cikin ranta tana masa addu'a,ita kanta mqryam din binshi tayi da ido cikin mamakin me ya sanya masa kuzari haka lokaci guda,mutumin da anyi anyi ya tashi a tafi gida ya qiya?ya tsaya shagwaba

shudewar kusan sa'a biyu har mami ta soma nuna damuwa sai gashi ya dawo,zufa duka ta wankeshi,cikin kulawa mamin ta dubeshi
''lafiya dai abdallah?''ta sake tambayarshi karo na biyu
''mami na samu nasarar kama alhj haladu,saura alhj hamza naira''ya bata amsa yana tsiyaya ruwa mai sanyi cikin tambulan na glass

ba mami ba,hatta da maryama dake zaune can gefe ba qaramin burgeta yayi ba,tana tsammanin dazun nan taji uana zancan neman mutumin amma har ya sami nasarar cafkeshi cikin abunda bai gaza awa daya da rabi ba,fuskarta qunshe da madaukakin murmushi take fadin
''masha Allah masha Allah,lallai dana daya da daya ne,baka tsinta aqasa ba abdallah,fata na Allah ya tsaremin kai yaci gaba da yi maka jagora,ya baka ikon ci gaba da tsayawa akan gaskiua,ya rabaka da aikinka lafiya''

yana kurbar ruwan sanyin yana ratsa qwaqwalwarsa sannan sanyin dadin addu'ar mahaifiya na sake shigarshi
''ameen ummi na,kullum addu'arki ita ce sirrin nasarata a rayuwa''
cikin mintina gona suka bar asibitin harda ummin don lokacin tashinta yayi

Sashensa ya wuce mami ta haura sama itama don kintsawa yayin da maryam kuma ta koma kitchen don kammala masu abincin dare tunda tuni an fara ahirye shiryen kiran salla,fashin sallar da take ne ya bata damar ci gaba da ayyukanta
shigarta kenan ta kunna gas tana shirin aza tukunya samanshi taga kamar anyi wuf an fice daga kitchen din,da sauri tabi hanyar fitan itama tana dube dube,bata ci nasarar ganin kowa ba sai adnan yayan zubaida dake shigowa cikin waiting room,wanda sairan qiris suyi karo da shi tayi saurin ja baya atsorace

kallo yake qare mata hade da wani shu'umin murmushi wanda hakan ya sanyata ta tsargu,ta tsani namini mai kallo don a aqidarta takan fassara mutum ne kawai da dan iska
''yi a hankali mana baby kada ki jiwa wannan kyakkyawan jikin ciwo ko''babu abunda tace da shi sai juyawa da tayi cikin sassarfa ta koma kitchen shi kuma ya mata rakiyar idanu,sai da ta bace ya wani lashe labba kana ya shige bangaransu

nene tayi saurin damqo wuyan rigarshi don ta fuskanci baima gansu ba a inda suke labe ita da zahariyya suna gano farfajiyar waiting parlour wucesu zaiyi,a razane ya juyo
''banza solobiyo kawai,harka wani tsorata,amma ka iya tsayawa kana qarewa jikin yarinya kallo''
kansa ya shafa yana fadin''to ai nene ba laifi bane''
''kaga ni ba wannan ba,kaga alamun yarinyar nan ta fuskanci an shiga kitchen dinsu ne?''
''eh to,ni dai na ganta a gurguje da alamu wani ta biyo''
''hanyar ina kaga tayi?''
''hanyar valcony''
ajiyar zuciya nene ta saki
''Allah na gode maka bata ga ko waye ba,kuma da alamu bata fuskanci komai ba''

''ya?nene?''adnan ya tambaya yana dagawa uwar gira
''mun aiwatar da aikin mu,saidai mu jira sakamako kuma,indai kuwa sakamako yazo da kyau,to mafarkin kowannen mu ya gama cika,don wannan karon indai aikin mu yaje inda ake buqata to babu makawa burinnu sai ya cika''
tsallen murna yayi
''that's why nake sonki nene,amma....''
ya katse maganar jin takun saukowa daga saman bene,zubaida ce,itama dubansu tayi kamar yadda suka dubeta,ganin yanayin fuskartq bai sauya ba ya tabbatar musu bata ji komai ba,gurin t.v ta nufa ta kunna sanna ta kamo tashar da take da buqatar kalla ba tare da tace da su komai ba,haushinsu duka take ji don dazun sun dqn haura sama kan yadda take son abdallah yana yarfata

_kuyi haquri da wannan sakamakon na wuni gurin mama na da bata jin dadi sosai,muna buqatar addu'o'inku,na gode_

*mrs muhammad ce*👑
Chapter 17 · 0% Book details