Sashe 75
Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cak taji ya dauketa baki daya bai direta ko ina ba sai kan kujerarsa da ya tashi ya ajjiye ta a kai bayab ya dauke alqur'anin dake kai ya maida man window din dakin inna wuro,reshe sai ya juye sa mujiya a maimakon abdallah dake kallonta a sace dazun,yanzun ita ke binshi da kallo baki sake kuma kai tsaye
Gabanta ya dawo ya durqusa baiko damu da rairayin dake gurin kada ya bata masa kaya ba,ya kama kyakkyawar qafarta da yake tunani anan ta gurde din
matsawa wani guri yayi sannan yace
''nan ne?''bata fahimci ma da ita yake ba don ta tafi cikin duniyar mamaki,saida yasa bakinsa ya hure mata brown oily eyes dinta da suka qara sheqi sakamakon sabuwar qwallar dake ciki tana yawo,bata kai ga fitowa ba
''kada ki cinyewa mero ni mana,ina ne gun ciwon?''ya tambayeta yana sake duban qafar tata
''abdallah ka warke?ka fara tafiya fa abdallah ko baka gani ba?''kyakkyawan murmushi ya saki kana ya dago ya dubeta kana ya sake maida kansa ga qafarta
''na sani kuma na gani,tun shekaran jiya na warke maryam,ranar da kika kwana a qijina,ranar da tsoho alhaji ya baki magani kika shafan da hannayenki masu albarka''
qwallar ta subuce ta zubo ta ido daya,muryarta so cool tace
''amma abdallah kaci gaba da zama a maysayin mai lalura?me yasa ka boye samuwar....''
''shshsh!''ya fada bayan ya sa qwayar idonshi cikin nata
''akwai dalili,sannan yanzun ba muhallin nganar bane''
kai ta girgixa ya gane so take ta fake ne ta masa borin nan nata,don haka ya rigata ta hanyar matse inda ta gurde din,ai kuwa tuni ta saki abinda takeso ta fada din ta maida gurbinsa da fadin
''wayyo qafata''tare da runtse ido ta kuma damqe hannun abdallahn,sake surarta yayi daga kan kujerar ya maida ta kan rabarmar kabar dake shimfide kusa da kujerar ya ajjiyeta,zama yayi ya miqe qafafunshi ya jawo qafar tata kan cinyarsa,idanu a warwaje tace
''me zaka yimin haka abdallah,kada ka fama min ciwo''ta fada a tsorace don tasan irin wannan gurdewar ta taba irinta taja bakinta tayi shiru taqi gayawa mama,sai data yi kwana uku maman ta lura,ta takura mata sai taje an duba mata,da taje ashe targade ne,taqi yarda a gyara mata qarshe sai da maman ta kaita da kanta,ai kuwa har suma tayi kafin a gama gyaran din qafar ta gama yin tsami,shi yasa yanzun ma ta tsorata kada taje irin wancan ne
Bai tanka mata ba kamar yadda bai kalleta ba ya kama gurin,kamawar farko ra saki qara tayo jikinsa baki daya ta nanade shi saboda azaba,kasa ci gaba yayi saboda irin riqon da tayi masa ma baki daya ua zare masa lakar jikinsa,tuni ta fara hawaye tana roqonsa kada ya sake taba mata wlh zafi
shiru yayi yana kallonta yadda taje faman kuka kamar yar baby,sai kukan ya bashi sha'awa saboda duka eye lashes dinta sun jiqe sa hawaye sun sake zara zara
Tazara ya sake bata ya faki idonta ya kuma damqar ciwon,ta qara shigewa jikinsa gumi yana karyo mata tare da wani sabon kukan,har cikin xuciyarsa yake jin kukan amma yasan idan ya qyale mata gaba zafin da zatajin sai yafi haka don ya gane targade ne a qafarta,qarfinsa yasa bai qyaleta ba sai da ya gyara,tuni ta jiqe sharkaf da gumi da hawaye harda majina,ya kalli fuskarta sai yaji dariya tazo masa duk fuskar ta hada ja,miqewa yayi ya nufi daki ta bishi da kallo don har yau mamakin takawarsa bata saketa ba,ya fito da handkherchief mai kyau da kansa ya dinga goge mata fuskar har sai da tayi tsaf kana ya gyara mata zaman ya miqar mata da qafarta ya jinginata da bango
gabanta ya dawo ya zauna dirshan,ganin yadda take jefa masa harara ya sashi daukar qur'aninsa ya bude yaci gaba da tilawarsa a zuciya
sai ta tsinci kanta itama tana qare masa kallo,ko ta ina abdallah cikakken namiji da samun irinsa sai an tona,kyau zubi da tsarinsa kadai ya isheshi ya godewa ubangijin daya qerashi
Komai nashi daidai yake,babu abunda yayi kodan ko yawa a tare da shi
''ya dai yammata akwai magana ne?''taji ya fada,kunya ta kamata ta rasa na cewa sai kawai ta soma qoqarin tashi,hannunta ya riqe yana fadin
''take it easy''sannan ya maidata ya zaunar
''idan kin tashin me zakiyi,ina kuma zaki je?''
''girki na dora kuma ban kammala ba,gashi yamma na dada yi''
sai ua dinke girar sama da ta qasa kana yace
''tab,ai kuwa yai saidai kada kowa yaci abinci cikin gidan nan,babu girkin da zakiyi''baki ta saki tana kallonsa yadda yabi ua hade rai tamkar wanda ta zaga,sai taga ya ajjiye qur'anin bayan ya saka alama ta inda zai tashi ya nufi rumfar girkin,kallo ta bishi da shi,sai ta tsinci bakinta yana furta
''ahamdulillahil lazi bini'imatihi ta timmus saalihaat kana ta limshe idonta tana sake gaskgatawa da miqa dukkan imaninta ga Allah,shine mai kun fa ya kun,yadda duk yakeso haka yakeyi haka kuma za'ayin''
Tana kallonshi yana tura wutar iccen tuni hayaqi ya bulbuleshi sai gashi ya fito da sauri daga rumfar idanu jajur hawaye na diga,dariya taso kamata,dama idan banda rigimar sa ina shi ina wutar icce,wataqila ma tunda gake bai taba zuwa gaban murhu ba balle ayi batun girki,yana goge qwallan yana fadin
''kai kai kai,yanzu baby haka kike shaqar wannan abun kamar kanka zai juye,gaskiya daga yau kin gama''dauke kanta tayi kamar bata jishi ba bayan kuma ta gefab ido take satar kallonshi
Baikai ga zama ba nero tayi sallama ta shigo gidan,turus tayi ta tsaya tana kallon abdallah,gani take kamar ba shi ba,sam ta kasa dauke idonta daga kanshi
''wannan kallon fa?''yace da ita sai ta sunne kai wai ita kunya,qarasowa tayi tana fadin
''yaushe ka warka abdullahi?''
''kinga ga girki can inna ta bari jeki qarasa tukunna kya zo muyi hirar''
miqewa tayi ta isa nufi cikin rumfar tana sake mamakin warkewar tasa har ta gaza boyewa tana zaune a rumfar girkin tana waiwayensa
hakanan maryam taji wani abu ya takoreta,ta dade tana qaryata kanta akan irin abunda takeji idan mairo ta rabi kanta da sunan kishi ne saidai a yanzu a yadda abun yaqi barinta ta tabbatar cewa kishin ne
baifi saura awa daya a kira magariba ba inna wuro ta dawo gaggauce don bata kaiwa magariba a unguwa
itama dai da mamakin take kallona abdallah dake tsaye kan maryam ya harde hannayensa a qirji yana kallonta kamar wanda aka baiwa gadinta
''bawan Allah?,Allah mai iko,kaine a tsaye da qafafunka?''
kyakkyawan murmushin nan nasa ya saki kana ya qarasa ga innar yana karban daurin buhu dake hannunta ya sa mata shi daga gefe
''ni ne inna wuro''
tana kame da bakinta tace
''bari malam yazo yaga ikon Allah,Allah gwanin iyawa ya amshi addu'ar bayinsa,kai Allah mun gode maka,sannu bawan Allah,Allah ya qara lafiya''
''ameen ameen inna''
ta dubi maryam dake zaune
''ita kuma wannan fa,meron ta barwa girkin kuma?''
Ya juya ya dubi maryam da ta dan hade rai don tasan yanzun innar zata sako wani abu kuma daban,ita kam gani take sam bata sonta yanzun tafi son abdallah da mero kawai
dariya ta tasowa abdallah,bai iya hadiyeta ba sai da ya dan dara
''inna targade tayi,Allah ma ya soni ya rufan asiri saura kadan tayi iyo cikin rijiya''
cikin tsoro innar ta zaro ido
''rjiya?,garin yaya ni 'yasu mairamu?''sai ta sake yin fuskar shanu ita ala dole sai ta nuna haushi take ji,sai abdallah ne ya bata amsa
''ina tsammani santsin lakar can ne,ba shiri inna na qarasawarkewa naje na tarota''
''to Allah ya rufa asiri''ta fada tana dan masa magana da ido,shi ma ya maida nata amsa ta hanyar langabe kansa da daga hannunshi alamun ban haquri
mairo ko dake bakin wuta cikin zuciyarta take cewa
''shi kuma baya tashi warkewa sai ranar da wani abun zai sameta,haka ma fa bakinsa yayi''
(hmmm,abdallah na maryam)
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Washegari da hisham suka wayi gari cikin garin ni'ima cikin kuma gidan inna wuro,dukkansu tare suka zauna karin safe,kowanne ka dubi fuskarsa zuwa zuciyarsa cike take da farinciki mara misali,hira suke a tsakaninsu har suka kammala,maryam ta kwashe kayan ta gyara gurin
tsoho alhaji yace
''to alhmdlh abdullahi,kaga dai yadda ubangiji ya karbi addu'armu cikin lokaci qanqani''
kanshi a qasa yace
''hakane,malam naga darasi cikin rayuwa sosai,naga abunda da can bansan da shi na sai da Allah ya jarrabaceni da lalura,rayuwa abar tsoro ce haka duniya ma abar tsoro ce,darasi ne babba na koya cikin lalurar da Allah ya jarabceni da ita''
''gaskiya ne,dama wani abun baka saninsa ko gane shi sai ka shiga wata jarabtar,Allah ka bamu ikon cinye jarrabawarsa''
dukkaninsu suka amsa da ameen
tsoho alhaji ya dubeshi
''yanzu sai shirye shiryen tafiya gida kenan''
murmushi ya saki kana yace
''banjin barin garin nan da wurwuri haka,garinku ya yimin malam sosai,yaci sunanshi ni'ima,bazan taba mance wa da garin nan cikin tarihin rayuwata har abada,baya ga haka neman aure nake malam cikin garin naku''
dum kunnenta taji gaba daya yayi tamkar ba zata iya ci gaba da sauraren komai ba,sai ta rasa gane a wanne bigire take a zaune?,duk wata laka ta jikinta ta daina aiki,so take ta tashi ta bar dakin amma haka ya gagara
''a cikin karkaran nan tamu kuwa?''tsoho alhaji ua fada cikin mamaki,cike da tabbatarwa ya gyada kansa
''eh malam''
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[5:05pm, 10/4/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶5⃣5⃣
*Daga abdullahi dan mas'ud Allah ya yarda da shi yace:Manzan Allah S A W yace ''duk wanda yayi nuni(fara aikatawa) akan wani aiki na alkhairi yana da kwatankwacin ladan wanda ya ya kwaikwayeshi(ba tare da an tauyewa kowa cikinsu daga ladansa ba''(haka yake ga wanda ya qirqiri wani aiki na sharri kuma wani koyi da shi shima yana da zunubi kan duk mutum daya daya aikata irin aikin kwatankwacin zunubin wanda ya aikata aikin)*
Gabanta ya dawo ya durqusa baiko damu da rairayin dake gurin kada ya bata masa kaya ba,ya kama kyakkyawar qafarta da yake tunani anan ta gurde din
matsawa wani guri yayi sannan yace
''nan ne?''bata fahimci ma da ita yake ba don ta tafi cikin duniyar mamaki,saida yasa bakinsa ya hure mata brown oily eyes dinta da suka qara sheqi sakamakon sabuwar qwallar dake ciki tana yawo,bata kai ga fitowa ba
''kada ki cinyewa mero ni mana,ina ne gun ciwon?''ya tambayeta yana sake duban qafar tata
''abdallah ka warke?ka fara tafiya fa abdallah ko baka gani ba?''kyakkyawan murmushi ya saki kana ya dago ya dubeta kana ya sake maida kansa ga qafarta
''na sani kuma na gani,tun shekaran jiya na warke maryam,ranar da kika kwana a qijina,ranar da tsoho alhaji ya baki magani kika shafan da hannayenki masu albarka''
qwallar ta subuce ta zubo ta ido daya,muryarta so cool tace
''amma abdallah kaci gaba da zama a maysayin mai lalura?me yasa ka boye samuwar....''
''shshsh!''ya fada bayan ya sa qwayar idonshi cikin nata
''akwai dalili,sannan yanzun ba muhallin nganar bane''
kai ta girgixa ya gane so take ta fake ne ta masa borin nan nata,don haka ya rigata ta hanyar matse inda ta gurde din,ai kuwa tuni ta saki abinda takeso ta fada din ta maida gurbinsa da fadin
''wayyo qafata''tare da runtse ido ta kuma damqe hannun abdallahn,sake surarta yayi daga kan kujerar ya maida ta kan rabarmar kabar dake shimfide kusa da kujerar ya ajjiyeta,zama yayi ya miqe qafafunshi ya jawo qafar tata kan cinyarsa,idanu a warwaje tace
''me zaka yimin haka abdallah,kada ka fama min ciwo''ta fada a tsorace don tasan irin wannan gurdewar ta taba irinta taja bakinta tayi shiru taqi gayawa mama,sai data yi kwana uku maman ta lura,ta takura mata sai taje an duba mata,da taje ashe targade ne,taqi yarda a gyara mata qarshe sai da maman ta kaita da kanta,ai kuwa har suma tayi kafin a gama gyaran din qafar ta gama yin tsami,shi yasa yanzun ma ta tsorata kada taje irin wancan ne
Bai tanka mata ba kamar yadda bai kalleta ba ya kama gurin,kamawar farko ra saki qara tayo jikinsa baki daya ta nanade shi saboda azaba,kasa ci gaba yayi saboda irin riqon da tayi masa ma baki daya ua zare masa lakar jikinsa,tuni ta fara hawaye tana roqonsa kada ya sake taba mata wlh zafi
shiru yayi yana kallonta yadda taje faman kuka kamar yar baby,sai kukan ya bashi sha'awa saboda duka eye lashes dinta sun jiqe sa hawaye sun sake zara zara
Tazara ya sake bata ya faki idonta ya kuma damqar ciwon,ta qara shigewa jikinsa gumi yana karyo mata tare da wani sabon kukan,har cikin xuciyarsa yake jin kukan amma yasan idan ya qyale mata gaba zafin da zatajin sai yafi haka don ya gane targade ne a qafarta,qarfinsa yasa bai qyaleta ba sai da ya gyara,tuni ta jiqe sharkaf da gumi da hawaye harda majina,ya kalli fuskarta sai yaji dariya tazo masa duk fuskar ta hada ja,miqewa yayi ya nufi daki ta bishi da kallo don har yau mamakin takawarsa bata saketa ba,ya fito da handkherchief mai kyau da kansa ya dinga goge mata fuskar har sai da tayi tsaf kana ya gyara mata zaman ya miqar mata da qafarta ya jinginata da bango
gabanta ya dawo ya zauna dirshan,ganin yadda take jefa masa harara ya sashi daukar qur'aninsa ya bude yaci gaba da tilawarsa a zuciya
sai ta tsinci kanta itama tana qare masa kallo,ko ta ina abdallah cikakken namiji da samun irinsa sai an tona,kyau zubi da tsarinsa kadai ya isheshi ya godewa ubangijin daya qerashi
Komai nashi daidai yake,babu abunda yayi kodan ko yawa a tare da shi
''ya dai yammata akwai magana ne?''taji ya fada,kunya ta kamata ta rasa na cewa sai kawai ta soma qoqarin tashi,hannunta ya riqe yana fadin
''take it easy''sannan ya maidata ya zaunar
''idan kin tashin me zakiyi,ina kuma zaki je?''
''girki na dora kuma ban kammala ba,gashi yamma na dada yi''
sai ua dinke girar sama da ta qasa kana yace
''tab,ai kuwa yai saidai kada kowa yaci abinci cikin gidan nan,babu girkin da zakiyi''baki ta saki tana kallonsa yadda yabi ua hade rai tamkar wanda ta zaga,sai taga ya ajjiye qur'anin bayan ya saka alama ta inda zai tashi ya nufi rumfar girkin,kallo ta bishi da shi,sai ta tsinci bakinta yana furta
''ahamdulillahil lazi bini'imatihi ta timmus saalihaat kana ta limshe idonta tana sake gaskgatawa da miqa dukkan imaninta ga Allah,shine mai kun fa ya kun,yadda duk yakeso haka yakeyi haka kuma za'ayin''
Tana kallonshi yana tura wutar iccen tuni hayaqi ya bulbuleshi sai gashi ya fito da sauri daga rumfar idanu jajur hawaye na diga,dariya taso kamata,dama idan banda rigimar sa ina shi ina wutar icce,wataqila ma tunda gake bai taba zuwa gaban murhu ba balle ayi batun girki,yana goge qwallan yana fadin
''kai kai kai,yanzu baby haka kike shaqar wannan abun kamar kanka zai juye,gaskiya daga yau kin gama''dauke kanta tayi kamar bata jishi ba bayan kuma ta gefab ido take satar kallonshi
Baikai ga zama ba nero tayi sallama ta shigo gidan,turus tayi ta tsaya tana kallon abdallah,gani take kamar ba shi ba,sam ta kasa dauke idonta daga kanshi
''wannan kallon fa?''yace da ita sai ta sunne kai wai ita kunya,qarasowa tayi tana fadin
''yaushe ka warka abdullahi?''
''kinga ga girki can inna ta bari jeki qarasa tukunna kya zo muyi hirar''
miqewa tayi ta isa nufi cikin rumfar tana sake mamakin warkewar tasa har ta gaza boyewa tana zaune a rumfar girkin tana waiwayensa
hakanan maryam taji wani abu ya takoreta,ta dade tana qaryata kanta akan irin abunda takeji idan mairo ta rabi kanta da sunan kishi ne saidai a yanzu a yadda abun yaqi barinta ta tabbatar cewa kishin ne
baifi saura awa daya a kira magariba ba inna wuro ta dawo gaggauce don bata kaiwa magariba a unguwa
itama dai da mamakin take kallona abdallah dake tsaye kan maryam ya harde hannayensa a qirji yana kallonta kamar wanda aka baiwa gadinta
''bawan Allah?,Allah mai iko,kaine a tsaye da qafafunka?''
kyakkyawan murmushin nan nasa ya saki kana ya qarasa ga innar yana karban daurin buhu dake hannunta ya sa mata shi daga gefe
''ni ne inna wuro''
tana kame da bakinta tace
''bari malam yazo yaga ikon Allah,Allah gwanin iyawa ya amshi addu'ar bayinsa,kai Allah mun gode maka,sannu bawan Allah,Allah ya qara lafiya''
''ameen ameen inna''
ta dubi maryam dake zaune
''ita kuma wannan fa,meron ta barwa girkin kuma?''
Ya juya ya dubi maryam da ta dan hade rai don tasan yanzun innar zata sako wani abu kuma daban,ita kam gani take sam bata sonta yanzun tafi son abdallah da mero kawai
dariya ta tasowa abdallah,bai iya hadiyeta ba sai da ya dan dara
''inna targade tayi,Allah ma ya soni ya rufan asiri saura kadan tayi iyo cikin rijiya''
cikin tsoro innar ta zaro ido
''rjiya?,garin yaya ni 'yasu mairamu?''sai ta sake yin fuskar shanu ita ala dole sai ta nuna haushi take ji,sai abdallah ne ya bata amsa
''ina tsammani santsin lakar can ne,ba shiri inna na qarasawarkewa naje na tarota''
''to Allah ya rufa asiri''ta fada tana dan masa magana da ido,shi ma ya maida nata amsa ta hanyar langabe kansa da daga hannunshi alamun ban haquri
mairo ko dake bakin wuta cikin zuciyarta take cewa
''shi kuma baya tashi warkewa sai ranar da wani abun zai sameta,haka ma fa bakinsa yayi''
(hmmm,abdallah na maryam)
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Washegari da hisham suka wayi gari cikin garin ni'ima cikin kuma gidan inna wuro,dukkansu tare suka zauna karin safe,kowanne ka dubi fuskarsa zuwa zuciyarsa cike take da farinciki mara misali,hira suke a tsakaninsu har suka kammala,maryam ta kwashe kayan ta gyara gurin
tsoho alhaji yace
''to alhmdlh abdullahi,kaga dai yadda ubangiji ya karbi addu'armu cikin lokaci qanqani''
kanshi a qasa yace
''hakane,malam naga darasi cikin rayuwa sosai,naga abunda da can bansan da shi na sai da Allah ya jarrabaceni da lalura,rayuwa abar tsoro ce haka duniya ma abar tsoro ce,darasi ne babba na koya cikin lalurar da Allah ya jarabceni da ita''
''gaskiya ne,dama wani abun baka saninsa ko gane shi sai ka shiga wata jarabtar,Allah ka bamu ikon cinye jarrabawarsa''
dukkaninsu suka amsa da ameen
tsoho alhaji ya dubeshi
''yanzu sai shirye shiryen tafiya gida kenan''
murmushi ya saki kana yace
''banjin barin garin nan da wurwuri haka,garinku ya yimin malam sosai,yaci sunanshi ni'ima,bazan taba mance wa da garin nan cikin tarihin rayuwata har abada,baya ga haka neman aure nake malam cikin garin naku''
dum kunnenta taji gaba daya yayi tamkar ba zata iya ci gaba da sauraren komai ba,sai ta rasa gane a wanne bigire take a zaune?,duk wata laka ta jikinta ta daina aiki,so take ta tashi ta bar dakin amma haka ya gagara
''a cikin karkaran nan tamu kuwa?''tsoho alhaji ua fada cikin mamaki,cike da tabbatarwa ya gyada kansa
''eh malam''
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[5:05pm, 10/4/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶5⃣5⃣
*Daga abdullahi dan mas'ud Allah ya yarda da shi yace:Manzan Allah S A W yace ''duk wanda yayi nuni(fara aikatawa) akan wani aiki na alkhairi yana da kwatankwacin ladan wanda ya ya kwaikwayeshi(ba tare da an tauyewa kowa cikinsu daga ladansa ba''(haka yake ga wanda ya qirqiri wani aiki na sharri kuma wani koyi da shi shima yana da zunubi kan duk mutum daya daya aikata irin aikin kwatankwacin zunubin wanda ya aikata aikin)*