Sashe 33
Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ji tayi an riqo tsintsiyar hannunta gam ana janta,babu shiri ta waiwayo abdallah ne tuni har ya fara tafiya,tilas ta saita wa kanta hanya ta bishi a baya tamkar raqumi da kala,don idan tayi tirjiyar bin nasa zata iya zubewa a qasa don da sauri yake jan nata
bai saketa ba sai da suka iao teburin na su kana ya sakar mata hannu hadi da yi mata nuni da kujerar data tashi dazu a kai,tsareta yayi da idanunshin nan masu kaifi
''sit,dake aka hada kutingwilar zuwa na nan,shine kuma duka zaku fashe ku barni zaune ji daya kamar yaron mayu,ki zauna ki kula da ni har mamin ta dawo ta karbeki,daga nan ma idan club zaki wuce ke ya shafa''
Tuni hawaye sun cika idanunta,bata ce masa komi ba ta zame ta zauna,shi kuma yayi tsaye hannayenshi harde bisa qirjinsa yana qarewa gun kallo tamkar mai neman wani
matashin saurayi ne yake dosowa gurin,kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewa ya gogu cikin duniyanci,sannu a hankali yake qarasowa har inda maryam din take,shigowarsa gurin kenan idanunahi sukayi tozali da ita,totally ta gama yi masa fatanshi daya 'yar hannu ce,zai iya kashe mata ko nawa ne matuqar zai samu hadin kanta,ta bayan kujerarta ya zagayo yasa dukka hannayenshi ya dafe makarin kujerar
''hello babe...''
gabanta ne ya yanke ya fadi,har ta kasa jiyowa taga ko waye,ga zatonshi bata ji ba don haka ya ranqwafo bayan nata yana shirin sanya hannunshi ya dafa kafadunta
cafkar da yaji an yiwa hannunshi yasan bata wasa bace,tamkar tarko ya kama bera haka abdallah ya riqe hanun nashi tsam,bai gama qarewa abdallan kallo ba yaji saukar lafiyayyun mari guda biyu da suka gigita shi,
hannu abdallah yasa ya yaye dogon hannun rigar t shirt din dake jikin saurayin,take wasu yan qanan rubutu da suka fi kama da na 'yan china suka bayyana a saman tsintsiyar hannunshi,a tare suka kakki juna ahi da mataahin tashin farko tsoro qarar ya bayyana idanun matashin,motsin da matashin ya fara yi da daya hannun nasa da abdallan bai riqe ba yana qoqarin cusa hannunshi aljihun bayan wandonshi ya ankarar da abdallan,cikin hanzari ya dunqule hannunshi ya daki hannun matashin take ya sagar masa da duk wata jijiya da zata taimaka masa ya iya motsa hannun,ya zura hannunshi aljihun matashin ya ciro 'yar qaramar bindiga ya cillata cikin nashi aljihun,qarar da ya saki ita ta janyo,hankalin mutanen dake kurkusa da su,cikin zafin nama da qwarewa da hannu daya ya tsinke duk wani maballi dake jikin t shirt din matashin ya finciketa daga jikinsa hade da juyo da bayan matashin ya kalla,zane ne kala kala a jiki wanda ba lallai kai ka iya ganewa ba
''anaconda isnt it?um?yaron alhj hamza mai qusa''
Abdallah ya fada bayan ya zagayo gaban matashin sunyi face to face,hannunshi daya ya sanya a aljihub rigarshi ya ciro qaramar wayarahi keypad qirar samsung,cikin qanqanin lokaci ya bada order turo ma'aikata inda suke din kana ya maida wayar aljihunsa,idanunshi qyar cikin na matashin yake tambayarsa
''ku nawa ne agurin nan?''shiru ya masa babu alamun zai amsa masa,hakan ya bawa abdallah damar yin tsai yana karantarshi,ba tare da matashin ya masa nuni ba ya karanci tabbas akwai abokin tafiyarsa ahannun daman abdallah,sai kuwa akayi dace shima ya yunquro da niyyar kubutar da dan uwanshi,duka daya abdallah ya waiwaya ya masa a dokin wuyanahi ya zube a qasa yana malelekuwa.
minti goma kyawawa basu cika ba jami'an ss suka iso gurin ya damqa musu su yace su kira jamal hussain ya fara aiki a kansu kafin gobe ya iso office din,mutanen dake gurin kam kowa godiya yake ma Allah suna fadin Allah ne kadai yasan me zai faru badon zuwanshi ba,sai da koma cikin mota ya kira mami yace suzo su taci don baya son,jama'suci gaba da shaida fuskarshi
ko cikin motar tamkar kace ket maryam ta zura a guje take ji,tsoron abdallah ya kuma cikata,ya dubeta da madubin motar lokacin da yake goge hannunshi da handkherchief suka hada ido,hade rai yayi yaja tsaki
''mutum sai shegen tsoro,komai ma tsorataka yake''mami tayi zaton da jama'ar inda suka baro yake
''a'ah wannan lamari fa da tsoro,wannan aikin ai saiku,kawai dai Allah ya tsare mana ku daga dukkan sharri''
murmushi ya saki
''haba mami na,kema fa jaruma ce,kin manta ke ke fede mutum ki ciro abun cirowa ki,mai da na mai dawa ki hadeshi ki dinke ya tashi tsaf yaci gaba da rayuwa cikin ikon ubangiji'
''um um,wannna daban da naku abdallah,a'uzubika bi kalmaatillahit taammaat min kullu ainin lammah wamin kulli shaidanin wa hamma''ta mishi irin addu'ar neman tsari da annabi s a w kewa hassan da usaini r.a
''ameen mami''ya fada don kusan a bakinta ya haddace wanna addu'ar tsabar yi masan da take yi,kuma yasha ganin riba da fa'idar ta
🌲🎄🌲🎄🌲🎄
ana jibi za'a dauki azumi ta tafi gidan raliya don su tattauna,ba qaramin dadi raliyan taji ba dq jin fitowar abdur rahim da dukkan qarfinshi neman auren aminiyar tata,ta jira har nasir ya dawo tayi mishi bayanin abdurrahim da kwantancan anguwarsu,ya dauka mata alqawarin xaiyi tattaki da kanshi har unguwar ta qoqi don ya mata bincike a kanshi,sosai taji dadin kara da karamcin da hayi mata,sun rabu kan duk yadda ake ciki nan da sati zaya sanar mata,ta mishi godiya sosai,yace babu komai ai an zama daya ya zolayeta da don ma ta qishi ne,dukkansu dariya suka saka da tuno baya da sukayi
kwanki shida kacal ba'a cika na bakwai din ba nasir ya kirata ya mata bayanin abdur rahim bashi da matsala,dukkan abunda ya fadi din haka yake,saidai abu guda bayan kasuwanci da yakeyi din yana da damara wato ma'aikacin tsaro ne,ta masa godiya mai qima sannan suka rabu,data tambayi abdur rahim din dariya kawai yayi yace yana tsammanin bata son auren mai unifoarm ne ya boye mata,bata dauki abun wani seriousd ba duk da ta nuna masa rashin jin dadinta ya kuma nemi afuwarta maganar ta wuce
azumi na da kwana goma ta sanar da abdur rahim ya shirya yazo ya gaida mami,bai musa ba ya amince,ta shirya masa girki na musamman,cikin wani dan kebantaccen gu dake harabar gidan ta ahirya komai,guri ne mai kyau davtsari cike da shuke shuke tamkar qaramin lamvu,duk da cewa daga can bayan gida akwai lambun amma wanna hakanan aka yishi darumfar bunu qwaya daya,qasanta shirye da fararen kujerun roba
mintina goma sha hudu ya rage akira magariba ta shiga wanka,ta ahirya tsaf cikin baqar doguwar riga mai sulbi data wadatu da dutsuna masu sheqi saqar qasar oman,mai kawavta shafa hoda ta zizara kwalli da man lebe,ta taje gashinta tayi acuci da shi daidai lokacin da masallatan garin kano suka soma kwarar kiran sallar magariba dabinonta dan madina dake cikin qaramin fridge din dakin ta ciro ta ciri uku taci ta ciro ruwa tasha sanna tayi add'ar buda baki,bandakinta ta koma tayi brush hadi da alwala ta yi sallar magaribar,kusan tunda aka fara azumi tare suke yin buda baki gaba dayansu,don haka bakwai na qarasa cika ta sauko qasan
tuni har mami da abida sun hallara don haka ta gaida mamin da yi mata sannu da shan ruwa ta soma sarving dinsu,ta kammala ta ja nata ta zauan,bata kai ga fara ci ba abdallah ya shigo ya ja kujera kusa da mamin yana fadin
''mami ke daya zaki ci ki bar autan naki''
''hmmm su auta manya''abida ta cafe zancan,harararta ya danyi
''kinga bansa da ke ba,wanna magana ce tsakanin d'a da mahaifiya''
hannu yasa cikin plate din chips dinta ya soma kaiwa baki dadin na ratsashi,bai ko kalli farantinsa guda biyu da cup da maryam ta shirya masa ba
sai teburin yayi shiru kowa na harkar gabanshi,cakula kawai maryam keyi don bata qaunar zaman cin abincin nan tare,sam bata sakewa
mami ta dubeta tana goge hannunta da ya dan baci da maiqo da tissue
''amma dai maryam ba wanna ce shigar fita zancan ba ko''
tayi murmushi har dimple dinta na lobawa kanta aduqe
''itace''ta fada kanta asunkuye,kallonta abida tayi ta sheqe da dariya kana tace tab,kallonta take kwaia wadda kanta yake cikin tukunya
''ban me yasa baki wa fuskarki makeup ba ko don kinsan ke din mai kyau ce,kyanki yana qara......''
bata iya qarasa zancan ba sakamon ciko pork da abdallah yayi da chips ya cusa ma mamin a baki
tilas ta karba sai davta fara taunawa ta dubeshi
''meye haka abdallah,dure zaka min''
ya marairaice
''mami baki qoshi ba fa,kuma idan ana cin abinci ba'a magana,ki qyale koma mene sai kin qoshi''
dauke kanta tayo ta dubi maryam
''ki duba kan mirrow dina akwai makevup kit ki dauko min yau da kaina zan miki kwalliyar
raka'a shida kacal ta samuyi sallar tarawih a maimakon raka'a goma sha uku davtakeyi,cikin awa daya saiga fuskar maryam din ta canza,zama mamin tayi sosai ta mata make up,abida kanta mamaki ta dinga yi,haka mami ta iya make up mai ma'ana?haka maryam ke da kyau,tun usuli ita din ba maison cika tarkace bace ta makevup a fuska,wannan kaye kayen sai hindatu,kyan da ta yiwa mamin yasa ta ta gaza barinta sai data mata hotuna,ta yi azabqr fita kuwa ahoton
aka gama kuwa a daidai,don gamawar tasu bai wuce da minti uku ba abdur rahim ya kirata gashi a compound din gidan ya samu shigowa bayan tarin tambayoyi da waya da mami ta yiwa securities din kan su barshi ya shigo
''jeki maza diyata ki shigo da shi''mami ta fada tana maida hijabinta data idar da sallar asham
tana qoqarin fita saqo ya shigo wayarta ta zaro tana dubawa,number din abdur rahim ta gani wanda hakan ya sanyata sakin murmushi ta soma qoqarin duba abinda ya turo mata
''ya subhanallah''taji ance bayan taga inuwar mutum a gabanta,da sauri ta daga kanta kana ta duba abinda taji ta taka
qafafan abdallah ne,taja baya kadan da sauri a tsorace,dawowarshi kenan daga sallar asham,sanye da jallabiya fara sol mai gajeran hannu wadda hakan ya sanya dukka gargasar hannunshi bayyana da hular tashi ka fiya naci itama fara,sai ya koma tamkar wani balarabe,kallonta yake kawai wanda har hakan ya bata tsoro,sexy eyes dinshi ya lumshe bisa fuskarta na aecond biyu ya bude
bai saketa ba sai da suka iao teburin na su kana ya sakar mata hannu hadi da yi mata nuni da kujerar data tashi dazu a kai,tsareta yayi da idanunshin nan masu kaifi
''sit,dake aka hada kutingwilar zuwa na nan,shine kuma duka zaku fashe ku barni zaune ji daya kamar yaron mayu,ki zauna ki kula da ni har mamin ta dawo ta karbeki,daga nan ma idan club zaki wuce ke ya shafa''
Tuni hawaye sun cika idanunta,bata ce masa komi ba ta zame ta zauna,shi kuma yayi tsaye hannayenshi harde bisa qirjinsa yana qarewa gun kallo tamkar mai neman wani
matashin saurayi ne yake dosowa gurin,kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewa ya gogu cikin duniyanci,sannu a hankali yake qarasowa har inda maryam din take,shigowarsa gurin kenan idanunahi sukayi tozali da ita,totally ta gama yi masa fatanshi daya 'yar hannu ce,zai iya kashe mata ko nawa ne matuqar zai samu hadin kanta,ta bayan kujerarta ya zagayo yasa dukka hannayenshi ya dafe makarin kujerar
''hello babe...''
gabanta ne ya yanke ya fadi,har ta kasa jiyowa taga ko waye,ga zatonshi bata ji ba don haka ya ranqwafo bayan nata yana shirin sanya hannunshi ya dafa kafadunta
cafkar da yaji an yiwa hannunshi yasan bata wasa bace,tamkar tarko ya kama bera haka abdallah ya riqe hanun nashi tsam,bai gama qarewa abdallan kallo ba yaji saukar lafiyayyun mari guda biyu da suka gigita shi,
hannu abdallah yasa ya yaye dogon hannun rigar t shirt din dake jikin saurayin,take wasu yan qanan rubutu da suka fi kama da na 'yan china suka bayyana a saman tsintsiyar hannunshi,a tare suka kakki juna ahi da mataahin tashin farko tsoro qarar ya bayyana idanun matashin,motsin da matashin ya fara yi da daya hannun nasa da abdallan bai riqe ba yana qoqarin cusa hannunshi aljihun bayan wandonshi ya ankarar da abdallan,cikin hanzari ya dunqule hannunshi ya daki hannun matashin take ya sagar masa da duk wata jijiya da zata taimaka masa ya iya motsa hannun,ya zura hannunshi aljihun matashin ya ciro 'yar qaramar bindiga ya cillata cikin nashi aljihun,qarar da ya saki ita ta janyo,hankalin mutanen dake kurkusa da su,cikin zafin nama da qwarewa da hannu daya ya tsinke duk wani maballi dake jikin t shirt din matashin ya finciketa daga jikinsa hade da juyo da bayan matashin ya kalla,zane ne kala kala a jiki wanda ba lallai kai ka iya ganewa ba
''anaconda isnt it?um?yaron alhj hamza mai qusa''
Abdallah ya fada bayan ya zagayo gaban matashin sunyi face to face,hannunshi daya ya sanya a aljihub rigarshi ya ciro qaramar wayarahi keypad qirar samsung,cikin qanqanin lokaci ya bada order turo ma'aikata inda suke din kana ya maida wayar aljihunsa,idanunshi qyar cikin na matashin yake tambayarsa
''ku nawa ne agurin nan?''shiru ya masa babu alamun zai amsa masa,hakan ya bawa abdallah damar yin tsai yana karantarshi,ba tare da matashin ya masa nuni ba ya karanci tabbas akwai abokin tafiyarsa ahannun daman abdallah,sai kuwa akayi dace shima ya yunquro da niyyar kubutar da dan uwanshi,duka daya abdallah ya waiwaya ya masa a dokin wuyanahi ya zube a qasa yana malelekuwa.
minti goma kyawawa basu cika ba jami'an ss suka iso gurin ya damqa musu su yace su kira jamal hussain ya fara aiki a kansu kafin gobe ya iso office din,mutanen dake gurin kam kowa godiya yake ma Allah suna fadin Allah ne kadai yasan me zai faru badon zuwanshi ba,sai da koma cikin mota ya kira mami yace suzo su taci don baya son,jama'suci gaba da shaida fuskarshi
ko cikin motar tamkar kace ket maryam ta zura a guje take ji,tsoron abdallah ya kuma cikata,ya dubeta da madubin motar lokacin da yake goge hannunshi da handkherchief suka hada ido,hade rai yayi yaja tsaki
''mutum sai shegen tsoro,komai ma tsorataka yake''mami tayi zaton da jama'ar inda suka baro yake
''a'ah wannan lamari fa da tsoro,wannan aikin ai saiku,kawai dai Allah ya tsare mana ku daga dukkan sharri''
murmushi ya saki
''haba mami na,kema fa jaruma ce,kin manta ke ke fede mutum ki ciro abun cirowa ki,mai da na mai dawa ki hadeshi ki dinke ya tashi tsaf yaci gaba da rayuwa cikin ikon ubangiji'
''um um,wannna daban da naku abdallah,a'uzubika bi kalmaatillahit taammaat min kullu ainin lammah wamin kulli shaidanin wa hamma''ta mishi irin addu'ar neman tsari da annabi s a w kewa hassan da usaini r.a
''ameen mami''ya fada don kusan a bakinta ya haddace wanna addu'ar tsabar yi masan da take yi,kuma yasha ganin riba da fa'idar ta
🌲🎄🌲🎄🌲🎄
ana jibi za'a dauki azumi ta tafi gidan raliya don su tattauna,ba qaramin dadi raliyan taji ba dq jin fitowar abdur rahim da dukkan qarfinshi neman auren aminiyar tata,ta jira har nasir ya dawo tayi mishi bayanin abdurrahim da kwantancan anguwarsu,ya dauka mata alqawarin xaiyi tattaki da kanshi har unguwar ta qoqi don ya mata bincike a kanshi,sosai taji dadin kara da karamcin da hayi mata,sun rabu kan duk yadda ake ciki nan da sati zaya sanar mata,ta mishi godiya sosai,yace babu komai ai an zama daya ya zolayeta da don ma ta qishi ne,dukkansu dariya suka saka da tuno baya da sukayi
kwanki shida kacal ba'a cika na bakwai din ba nasir ya kirata ya mata bayanin abdur rahim bashi da matsala,dukkan abunda ya fadi din haka yake,saidai abu guda bayan kasuwanci da yakeyi din yana da damara wato ma'aikacin tsaro ne,ta masa godiya mai qima sannan suka rabu,data tambayi abdur rahim din dariya kawai yayi yace yana tsammanin bata son auren mai unifoarm ne ya boye mata,bata dauki abun wani seriousd ba duk da ta nuna masa rashin jin dadinta ya kuma nemi afuwarta maganar ta wuce
azumi na da kwana goma ta sanar da abdur rahim ya shirya yazo ya gaida mami,bai musa ba ya amince,ta shirya masa girki na musamman,cikin wani dan kebantaccen gu dake harabar gidan ta ahirya komai,guri ne mai kyau davtsari cike da shuke shuke tamkar qaramin lamvu,duk da cewa daga can bayan gida akwai lambun amma wanna hakanan aka yishi darumfar bunu qwaya daya,qasanta shirye da fararen kujerun roba
mintina goma sha hudu ya rage akira magariba ta shiga wanka,ta ahirya tsaf cikin baqar doguwar riga mai sulbi data wadatu da dutsuna masu sheqi saqar qasar oman,mai kawavta shafa hoda ta zizara kwalli da man lebe,ta taje gashinta tayi acuci da shi daidai lokacin da masallatan garin kano suka soma kwarar kiran sallar magariba dabinonta dan madina dake cikin qaramin fridge din dakin ta ciro ta ciri uku taci ta ciro ruwa tasha sanna tayi add'ar buda baki,bandakinta ta koma tayi brush hadi da alwala ta yi sallar magaribar,kusan tunda aka fara azumi tare suke yin buda baki gaba dayansu,don haka bakwai na qarasa cika ta sauko qasan
tuni har mami da abida sun hallara don haka ta gaida mamin da yi mata sannu da shan ruwa ta soma sarving dinsu,ta kammala ta ja nata ta zauan,bata kai ga fara ci ba abdallah ya shigo ya ja kujera kusa da mamin yana fadin
''mami ke daya zaki ci ki bar autan naki''
''hmmm su auta manya''abida ta cafe zancan,harararta ya danyi
''kinga bansa da ke ba,wanna magana ce tsakanin d'a da mahaifiya''
hannu yasa cikin plate din chips dinta ya soma kaiwa baki dadin na ratsashi,bai ko kalli farantinsa guda biyu da cup da maryam ta shirya masa ba
sai teburin yayi shiru kowa na harkar gabanshi,cakula kawai maryam keyi don bata qaunar zaman cin abincin nan tare,sam bata sakewa
mami ta dubeta tana goge hannunta da ya dan baci da maiqo da tissue
''amma dai maryam ba wanna ce shigar fita zancan ba ko''
tayi murmushi har dimple dinta na lobawa kanta aduqe
''itace''ta fada kanta asunkuye,kallonta abida tayi ta sheqe da dariya kana tace tab,kallonta take kwaia wadda kanta yake cikin tukunya
''ban me yasa baki wa fuskarki makeup ba ko don kinsan ke din mai kyau ce,kyanki yana qara......''
bata iya qarasa zancan ba sakamon ciko pork da abdallah yayi da chips ya cusa ma mamin a baki
tilas ta karba sai davta fara taunawa ta dubeshi
''meye haka abdallah,dure zaka min''
ya marairaice
''mami baki qoshi ba fa,kuma idan ana cin abinci ba'a magana,ki qyale koma mene sai kin qoshi''
dauke kanta tayo ta dubi maryam
''ki duba kan mirrow dina akwai makevup kit ki dauko min yau da kaina zan miki kwalliyar
raka'a shida kacal ta samuyi sallar tarawih a maimakon raka'a goma sha uku davtakeyi,cikin awa daya saiga fuskar maryam din ta canza,zama mamin tayi sosai ta mata make up,abida kanta mamaki ta dinga yi,haka mami ta iya make up mai ma'ana?haka maryam ke da kyau,tun usuli ita din ba maison cika tarkace bace ta makevup a fuska,wannan kaye kayen sai hindatu,kyan da ta yiwa mamin yasa ta ta gaza barinta sai data mata hotuna,ta yi azabqr fita kuwa ahoton
aka gama kuwa a daidai,don gamawar tasu bai wuce da minti uku ba abdur rahim ya kirata gashi a compound din gidan ya samu shigowa bayan tarin tambayoyi da waya da mami ta yiwa securities din kan su barshi ya shigo
''jeki maza diyata ki shigo da shi''mami ta fada tana maida hijabinta data idar da sallar asham
tana qoqarin fita saqo ya shigo wayarta ta zaro tana dubawa,number din abdur rahim ta gani wanda hakan ya sanyata sakin murmushi ta soma qoqarin duba abinda ya turo mata
''ya subhanallah''taji ance bayan taga inuwar mutum a gabanta,da sauri ta daga kanta kana ta duba abinda taji ta taka
qafafan abdallah ne,taja baya kadan da sauri a tsorace,dawowarshi kenan daga sallar asham,sanye da jallabiya fara sol mai gajeran hannu wadda hakan ya sanya dukka gargasar hannunshi bayyana da hular tashi ka fiya naci itama fara,sai ya koma tamkar wani balarabe,kallonta yake kawai wanda har hakan ya bata tsoro,sexy eyes dinshi ya lumshe bisa fuskarta na aecond biyu ya bude