← Book details Abadan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 103

Sashe 61

Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta dago da niyyar dubanshi idanunta cike da qwalla da ya rasa ta meye,take idanunsu suka hadu,da sauri ta janye nata idanun don bata iya dauke nauyin idanunshi cikin nata
''ka sakemin hannu kaga duk ka.....''
''bazan sakeki ba,sai kin gayan meke damunki,tunda bakina ya budu baki,barni nayi magana da ke ba sai wasu ke tayani hira?''
ta sake kau da kanta kana tace
''to me kake so muce ko ince maka ne?''
''bana tunanin baki san me zaki gayan ba maryam,nasha hango maganganu da dama boye cikin idanunki,kin hana bakinki ya furta kina cutar da zuciyarki hakanan babu gaira babu dalili ba tare da ta yi miki laifin komai ba''
kamar wadda ya doka sai ta soma hawaye,ita kanta batasan me yake saurin karya mata zuciya ba
''subhanallah,kuka...kuka kuma maryam me na miki''babu amsa don haka ya janyota ta fada jikinshi ragowar ruwan ya zube mata ya jiqa mata gaban dan yalolon hijabin jikinta wanda takansa duk dare idan zata kwanta,dama ba wani kauri gareahi ba,yauqi ne da shi da rashin kauri take kuwa ya manne mata a jiki.

''yi shiru ki gayan matsalarki,bazanso saki kuka ba maryam cikin irin wannan lokacin,baki cancanci haka ba''
''ka sakeni ni babu abinda ke damuna,ka qyaleni''
kai ya girgiza hakanan mutum,bazai yita kuka ba komai na da dalili''
ta tabbatar indai abdallah ne bazai saketa din ba don ya mata riqon tsauri ne don haka tace
''kayana,ka jiqamin kayana ka sakeni na canza wasu''
idanunshi ya kai kan gaban jijabin nata cikin hasken torch din wayarshin,wani abu ya tairga mishi har qasan qafarshi,ya kai,hannunshi gaban hijabin yana fadin
''bari na cire miki''
kan tayi qoqarin hanashi har yaje,gaba dayansu wuta ta dauke musu shi da itan gaba daya,sai ta sakar masa wani kikan harda dan sauti
''am so sorry my dear''kawai yake fada ya cire hijabin ya cillar gefe daya ya sake mannata kan qirjinsa,yana kin sautin kukanta bai hana ta ba don yasan koma mene idan tayi kuka sosai zuciyarta zata sassauta,tun sautin na fita kadan kadan har ta koma ajiyar zuciya kana numfashinta ya fara sauka a hankali alamun bacci yayi awon gaba da ita.

murmushi ya saka mai qayatarwa qasa qasa yace bayan ya leqa fuskarta
''rigimammiya,kin hana zuciyarki sakat''yana gyara mata kwanciya,ya fuskanci duk ranar da ta kwanta a qirjinshi bata dadewa bacci ke daukanta wani lokacin ma har taso makara gun tashi,ya saki ajiyar zuciya qasa qasa yace
''u dont know how u make me feel duk sanda kike jikina''ya dora kanshi saman habarta cike da wata iriyar nutsuwa.

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

A shirye take cikin riga da wando na pakistan ruwan madara tayi rolling da mayafinsu,zaune take kan kujera ko motsi batayi kanta a duqe tana kallon yatsuntsa,ya sake dubanta tini har ta fara zub da qwallar tata abinda bai son gani
''kina son fita amma kinqi ki gyara ni,nikam yau babu wanda zaimin wanka idan bake ba,see you ko tausayina baki ji,kin gwammace mustafa yayi ta yimin bayan bako ina yake wanke min ba wani gun ni nake da kaina''
maryam cikin muryar kuka ba tare da ta dago ba
''taya zan wuce bandaki ni da kai yi maka wanka inna wuro na kallon mu,haba mana abdal....''
''fine,muyi zamanmu ko baby na ni dake yau cikin daki,babu mai cewa don me ko''qara narkewa tayi tana faman hawaye don tana jiyo muryar inna wuro na jajjabin rashin jin motsin daya daga cikinsu,duk da tasan kara da alkunya bazata bar inna wuron tayi magana ba ko zasu shekara cikin dakin.

Narkewa yayi shima cikin filallukan dake kan whellchair dinshi dariya na cinshi,ya sani cewa ba zata taba iyawa ba,ko kaya na shan iska bata yarda ta gani jikinsa kuma duka ua gama karantota,ta daukeshi kamar wani muharraminta
sallama mairo tayi tana daga labulen dakin
''yaya abdullahi muna ta cigiyarku shiru?''ta fada tana kallonashi tana kuma kallon maryam
girarshi ya dage guda daya
''eh,muma muna ta cigiyarku,daman ke nake jira ki taimaka min inyi wanka,yau meramu ta gaji''ya ambaci sunan ta irin salon da yaji suna fada
zuciyar mero qal ta rufe fuskarta da tafukan hannunta,da sauri maryam ta dago babu shiri ta dubi abdallah qirjinta ya buga kamar an dakeshi da guduma,ido daya ya kashe mata kana ya dauke kanshi ya maida kan mero wadda take fadin
''kai yaya abdullahi''cikin salon nuna jin kunya.

kan mero ta bude idonta har maryam ta taashi ta kama wheelchair din tayi hanyar fita da shi,sai data bude idon nata raga dakin wayam har sun fice,jiki ba qwari jtama ta fice a dakin
inna wuro bata a tsakar gidan don haka tayi maza ta tura suka shige bayan gidan
''take it easy mana madam,kada ki fadar da bawan Allah''inji abdallah cike da dariyar mugunta da yake qunsheta
tana tsaye ya soma cire kayanshi ta dauke kanta qirjinta na lugude,saura gajeran wandon daya rage wanda yake bari a jikinsa idan zaiyi wanka,gaba daya ta rude don bata yarda taga jikinshi har kamar haka,hatta da cinyoyinshi dake cike da gargasa sun fito,ganin yana niyyar fidda shi shima yasa ta qarasa rudewar gaba daya,batasan ta dafe hannunshi ba
''ayya mana abdallah ba kyau fa don Allah''ta fada cikin son fashewa da kuka
dariya sosai ta kamshi amma ya hade rai yayi kicin kicin
''to me naki,dazun fa adaki kika gayan babu ruwan wani da wani,kema me ruwanki da ni ko na cire din,ba wanka zaki tayani ba?,kimin wankanki kawai ki maida ni daki,wai haka ma ake jinyar mutum?,oh ni abdallah sam baki iya jinya ba''ba bakin maida amsa girgiza kai tayi yaci gaba da kiciniyarshi,a guje ta kwasa ta fice a bayin dariyar da yake boyewa tilas ta fito,mamaki take bashi tamkar cikin qauyen aka haifeta ko kuma shi din ba mijinta bane,kunyarta ta mata yawa ta maida shi kamar wani dodo,Allah yasa komai na wanka na gabanshi don haka ya qyaleta yayi abunshi tunda hannunshi na kaiwa.

sai da ya kammala ya bubbuga qofan bandakin tazo ta fidda shi,tana ta rarraba ido kamar wadda ta yiwa sarki qarya ta shigo idanunta a qasa taqi yarda su hada idanu,itakam rashin kunyar shi ta fara isarta,daga warkewarsa jiya zuwa yau ya addabeta gaba daya ya hanata sukuni,ina dalili,yana abu kamar su biyu ne kadai cikin gidan.

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[2:36pm, 9/27/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶4⃣9⃣

*GA WASU FA'IDOJI*👌🏽

*_daga bakin mai gaskiya abun gasgatawa assaadiq al masduq Annabi Muhammad S A W yace''abinda yake zama hijabi tsakanin al'aurar dan adam da idon shaidanu fadin wannan addu'ar yayin da zaka cire tufarka BISMILLAHILLAZI LA ILAHA ILLA HUWA_*''

*_don samun kariya yayin yin baccinka,bayan ka kammla dukkan addu'ar baccin da annabin rahama ya koyar,ki karanta wadan nan ayoyin suma ki tofa musamman ga 'yan mata da suke fama da jinnul aashiq wato aljanin dare_*
1⃣ *_katamallahu ala qulubihim wa'ala sam'ihim wa ala absaarihim gishawah,ealahum azabun alim_*
2⃣ *_waja'alna min bani aydihim saddan wamin khalfihim saddan fa agshaynahum fahum la yubsirun_*
3⃣ *_wa'iza qara'atal qur'ana ja'alna bainaka wa bainal lazina la yu'u minuna bil aakhirati hijaban mastura,wa iza zakarta rabbuka bil qur'ani wahdahu wallau ala adbarihim nufura_*

Hira suke kamar kowanne dare zaune warqashin rumfar qofar dakin inna wuro,dukkansu sauraron inna wuron suke su ukun tana basu labarin yanayin zaman aure a shekarun baya can da suka shude
ita kam maryam fadi take taga ta kanta,ta sani sarai da biyu inna wuro ta tsiro da wannan tarihin,tana ankare da abdallah yana satar kallonta,da sun hada ido kuma ya dauke kai sai ka rantse ba kallonta yake ba.

wata yarinyarce tayi sallama ta shigo gidan,inna wuro ta kalli yarinyar lokacin da ta duqa tana gaidata
''lpy qalau indo,ya mutan gidan''
''suna nan lpy suna gaisheku''ta juya ta kalli abdallah da maryam ta gaidasu kana ta kalli mero dake qoqarin miqewa tana fadin
''amma indo yaushe kuka dawo daga kanon,gaskiya birni ta karbeki kinga yadda kika canza kika zama 'yar gayu kuwa?''.

Abdallah da maryam suka dubeta dukkansu dariya ce taso kamasu ita marysm cikin zuciyar ta ne,ina wani gayu anan,amma ita mero ganin wayewarta take a haka,abdallah kuwa sai da murmushi ya bayyana a fuskarshi yana duban yarinyar da ake batun wai ta canza din ta waye,idanun maryam yakai kansa,sai taji wani abu ya tokareta,ga zatonta su meron yakewa murmushi,ta janye idanunta a hankali tana gargadin zuciyarta.

Kama hannun indo mero tayi tana fadin ''muje waje indo''
''dan dalin fa?labaran yace tunda na tafi bai sake ganinki a dandali ba,yanzu ma shi ya aikoni na kai masa ke''bata amsa mata ba sai figar hannun indon da tayi suka fice,ci gaba sukayi da hurar wadda kusan inna wuro da abdallah ne jigon.

Kwanukan maryam ta kwashe ta kai cikin tukunyar tuwon da aka cikata da ruwa don inna wuro tuni ta hanata wanke wanken dare
ta tattare gun ta nufi soron inda suke ajjiye abun shararsu don ta zubar,soron babu haske don wearing din solar da kayi banda nan don haka bata iya ganinsu sosai,saidai tana ganin tsaiwatsu daga can qofar ficewa a gidan baki daya,muryar indo ta fara ji
''yanzu ke mero idan banda tsaurin ido inake ina wannan balaraben tsabar daukowa kai masifa da kuma jan abinda yafi qarfinka,ins laifin ma ki tsayawa labaran dinki,tunfa kina mitsitsiyarki yake sonki kuma an bashi ke,rashin kudin kayan daki ne ya hana auranku amma da tuni yanzu ai kina da yara''
''babu jan masifa,wallahi indo kada ki dauka wasa nake,da gaske sonsa nake wallahi tun ranar da na fara ganinsa,inason abdullahi sosai wallahi''
''tab,to kuwa kin debo da zafi,daidai ruwa fa daidai qurji,wai shin wannan 'yar indiyar ta gefensa ba matarsa bace,idan kuwa hakane to inake ina hada kai da ita,aradu baki fice irin aikinsu da ake kai musubirni ba,ta gurin gashi ne kawai zaku goga da ita amma ta wuceki mero,kiyi haquri kada ki wahal da kanki''.
Chapter 61 · 0% Book details