← Book details Abadan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 103

Sashe 15

Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

bata ce masa komai ba ta zagayeshi ta wuce bayan ta kunna qwayayen lantarkin din dake falon,ta riga shi isa dining din don haka ta soma hada mishi tea don kafin ta kammala zuba mishi komai zafin ya dan sarara
kujera ya ja ya zauna daidai lokacin da wayarshi ta soma ringing
tamkar wani mace haka yake amsa waya,ba hayaniya ba daga murya

''shi don ubanshi bai san kai wane ba da,zai hanaka shigowa?,to ya bari mintina biyar su cika ya gani,idan ka ahigo ka sameni gefan mami''abinda kawai taji yace kenan ya kife wayan saman table,fuska a murtuke ya ja kofin shayin ya kai bakinsa,tana ahirin dakatar da shi amma tuni ya kai bakinsa,ai kuwa babu shiri ya dawo dana bakinsa ya fesar

''ke wacce iriyan muguwa ce don Allah,haka ake bawa mjtum tea da azabar zafi kamar za'a dafa mishi baki?''
muryarta a narke tace
''ayyah,don Allah kayi haquri,ina shirin dakatar da kai naga har har ka sha''
''mtswee...you are verru stupid''ya fada sannan cikin hanzari ya dauki wayarshi dake bisa teburin ya fara danne danne

''hello abdallah,lokacin aiki ne fa ina tare da patients''muryar mami kenan
''mami yarinyar nan aiki aka kawota ta min ko kisa?''a razane maryam ta dago ta kalleshi,sai kuma ta maida kqnta qasa ta sadda shi,tini oily eyes dinta suka qara sheqi ssakamakon qwallar da ta soma dan taruwa mata
cikin faduwar gaba mamin tace
''me ya faru abdallah?''
''mami zata kasheni da ruwan zafi,tea mai azabar zafi mami ta bani zai qona ni''
ajiyar zuciya ta saki
''oh my god abdallah,kasan yadda ka bani tsoro kuwa?,just ruwan zafi kawai ahine kake wa haka,sau nawa kana shan tea ba tare da ka fifita shi ba,sannan nasan maryam bazata taba baka tea da zafi tana sane ba''
''gaskiya mami bata san aikinta sam''
''enought abdallah....bani maryam din''

qyashin bata wayarshi yake,sai ya saka handsfree kawai ya dan tura ta gabanta kadan
''maryam,ya akayi''cikin rawar murya tace
''wallahi mami ba da niyya bane kaw....''
''manta da abdallah kinji,kici gaba da aikinki,but ki kula da shi kinga bani nan,hakanan sai kinyi haquri da tabarar abdallah don na....''
cikin hanzari ya dawo da wayar gabanshi bayan ya kashe handsfree din yana cewa
''omg mami''
batasan me tace masa ba ta dai ji yace
''ok bye take care''

daga bakin falon ake sallama,bai dubi gun ba yace
''comone guy,idan zaka shigo ka shigo duk ka cikawa mutane kunne da sallama''
matashi ne kusan sa'a,ne ga abdallah
''kaifa baka da mutunci wallahi''
''kai shine da kai ai''
dariya ya saki bayan ya iso ya bashi hannu suka cafke,kujera daua ya ja ya zauna yana leqen flate din dake gaban abdallan

''kai mutumina,irin wannan liyafa haka,rabona ne kawai ya rantse shi yasa na qaraso kenan,da har nayi fushi nace bazan shigo ba''
''kanka ake ji sarkin kwadayi,yi sarving dinshi''yace da maryama wadda ke goge gun da abincin ya taba
sam bai kula da ita ba sai da abdallan yayi magana
''ina kwana''tace masa idonta na kan flaye din da take zuba masa hadin salad
fuakarsa dauke da mayalwacin murmushi ya amsa
''lafiya lau 'yammata ya gida?''
''lafiya''tace masa ataqaice don ta qagu ta kammala ta bar gun,tun dagowar farko ta lura da yadda yake faman kallonta
tana sauka daga stares din dining atea din taji yana tambayar abdallah
''fatabarakallahu ahsanul khaliqin,abokina wanna fa,cikin family dinku take?''

a qufule abdallan yace''dan iska ban sani ba,kaga wannan tayi kamar da 'yar dangin mu ne,dan rainin hankali?''
''pls guy yimin bayani don Allah''
sai da ya gama shan qamshinsa kafin yace
''cook dina ce,mami ce ta kawota''
har wani dan zullo hisham yayi
''wow,gaskiya ta qeru wallahi ba qarya,kai....man ba cook mami ta kawo maka ba,matar aure ce wallahi wannan''
abincin bakinsa ya tofar bayan ya dalla masa harar kamar zai cinye shi
''allah ua,isa tsakanin mu kawai hisham,wanna ai cin fuska ne,house girl fa,ni abdallah,i think ka manta waye abdallah ne ko,ya kamata kayo gaggawar tunawa,har yau ba'a qera matar abdallah ba,ni,mai ysada ne don,haka mace mai tsada ce matar abdallah,ban tsammanin ma zanyi aure cikin jinsin hausa fulani,sai na shiga cikin larabawa,i hope ka fahimceni?''

dariya hisham ya qyalqyale da ita kafin yace
''nasan waye abdallah,d expensive man,amma ina tsammanin man ka makance ko?,bana zato ko cikin larabawa kowa ke da irin halittar babe din nan''
''kaga malam ni ba ganewa nake ba,u know ni ba irinka bane mayan mata,kai da ka gano,sai kaje ka qarata ai ko''
''is ok...is ok,ni na gani to ina so''
cikin i dont care yace
''ok,ba laifi,amma daga ranar ka cire abdallah daga list din abokanka''
''why?saboda me ?''
goge hannunshi da tissue kana ya tire kujerar da yake kai ya miqe yana duba agogon hannunshi
''coz babu mai zubda min class,kaga nifa ina da wani aiki,ina da bincike cikin unguwar tudun maliki,so bana buqatar securities su rakani saboda is screet,idan ka gama zub da mutuncin naka ka fito mu wuce''
daga haka yayi saukanshi,hisham na daroya ya miqe ya bishi
maryam dake saman kujera ta tabe baki

''lallai,Allah ya tsareni da da tarayya da ire irenku,kai din ma baka min ba bare abokanka,mai girman kai kawai,kudi ai ba sune mutunci ba''cikin zuciyarga take zanta hakan,ta jawo wayarta ta kira raliya don kada ma ta batawa kanta rai a banza

*mrs muhammad ce*👑
Chapter 15 · 0% Book details