Sashe 13
Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
tare suka sauko dukansu abdallah na gaba,mami na bayansa maryam na binsu a baya
''banza a banza kawai,maras kunyar qarya,gidan da kike taqama da shi ina cewa 'yar karo ce ke''
surutan wata matashiya kenan lokacin da take shigowa falon,matashiya ce 'yar zamani wadda shigarta kadai ta isa nuna maka hakan,sanye take da fitted gown wadda tabi lafiyar jikinta,kanta daure da roses sai swagger dinta mai sarqa rataye a kafadarta,takalmin qafarta kuwa kai kace sama take shirin tabowa saboda tsininsa,fuskarta tasha fente fenten kwalliyar zamani
''a'ah salma,ke da wa kuma,hali zanen dutse''inji mami da ta tsaya tana kallonta
''ni da waccar agolan gidan taku mana,duk randa nazo gidan nan sai ta nemi raina min hankali,wallahi abdallah ka ja mata kunne ni ba sa'arta bace,ni na hana ka sota da zata dinga neman huce haushinta akaina,ina ruwan biri da gada,nafsi nafsi kawai''
kafadunshi ya daga yana ware hannayenshi🤷🏻♂
''ina ruwan abdallah ya taku,kina da baki kema fa''ya fada cikin ko in kula
ta yamutse fuska
''baka fa da kirki wani lokacin wallahi,watsamin to qasa a ido,mami kina jinsa ko''
murmushi tayi
''bismillahi Allah,ai kun fara kuma kenan''
ya dubi mama
''manta da ita mami,ni zan wuce masallaci''
''ni matsalata da kai waqanci wlh,ka sani fa sarai saboda kai na zo,shine zaka wani fita''ta fadi mishi tana kallonshi bayan ta zauna tana sabule cogen qafafunta
''sai na fasa sallar juma'a saboda sarauniyar matan duniya ta zo''ya fada yana yin gaba abinsa
''a'a,ni bance ba amma sai yaushe zaka dawo?''
''qarfe biyar,bit ban tabbas ina iya wuce hakan,idan zaki iya jira na fine''
''ina jira sai ka dawo''
ba tare da ya amsata ba ya qarasa ficewa
maryam na kichen take jiyo su
tunda ta shiga kitchen din bata fito ba sai da ta kammala girkin,lokacin da ya fito mami bata falon sai baquwar da taji an kira salma dake kwance dai dai kan three sitter,kanta ta dago tabi maryam da kallo,hada idon da sukayi bak sata dauke idonta ba
''sannu maryam,kada dai ace har kin kammala?''
inji mami dake saukowa daga saman bene
''eh na gama mami''ta amsa mata bayan ta tsagaita daha tafiyar da takeyi
''sannunki''ta amsa mata sannan ta juya don shigewa dakinta,tana jiyota tana tambayar mamin wace ita?saidai bata ji amsar da mamin ta bata ba
kiran da mamin ta yi mata ne ya sake fito da ita tun bayan shigarta dakin wanda wanka kawai taui ta saiya kayanta tayi salla,biyi taga 'yan matam sun zama,saidai iya wannan sanhe take da riga da wando wadanda suka bayuana surarta,inda Allah ya taqaita siririya ce sosai,
tadan dauke kanta zuwa sashen da mamin ke zaune
''gani mami''
''yauwa maryam,baki fito kinci abincinki ba,ga baqi yau agodan amma kin zauna a daki''
''mami na qoshi ne sai anjima''
''to zauna muyo hira,bana son kina zaman dakin nan ke daya,na gaya miki nafison ki dinga jin a ranki ke diya ta ce,wannan sunanta salma 'yar qanwata ce,waccan kuma sunanta saddiqa ita kuma 'yar yaya na ce,dukansu sunzo yoma abdallah sannu da zuwa''
''sannunku''ta fada cikin sassanyar muryarta
amsawar ganin dama suka mata tamkar wadanda aka tilasta,wanda hakan sam bai,mata dadi ba,har taji zamansun ma guri daya babu marching,don sam bata son wulaqanci,maca ce ita mai karamci shi yasa ako yaushe take tsammanin karamci daga gurin duk wanda zata mu'amaleshi
''am...mami da wai kitchen zan koma in dora abincin dare''
''baki gajiya maryam,a qa'ida ai kin gama girkinki na yau tunda sau biyu ne a rana ko''
kanta na aqasa tayi murmushi
''ba aikinta kenan ba,ki barta mana mami''inji saddiqa wadda ta dora qafa daya kan daya tana danne danne waya da bai wuce tana charting ne
''ba komai mami,ai ba wani qa'ida tsakanin mu,kuma ko ba haka bama ai kinga baqi aka yi,kuma aikin ya abdallah nake,tunda aikinsa nake kinga ba laifi na giwa wadanda suka zo gunshi abinci''
sosai ta burge mamin,tana son mutum mai sauqin kai,wanda ta fuskanci halin maryam ne
yayin da salma da,saddiqa suka dago kai suka kalleta,salma ta kasa shiru
''hmmmm,lallaikam,dadin abun ma biyanka ake ba''
sai abun ya bawa maryam din mamaki,to meye kuma hadin kaska da kifi,me haka kuma,me tayi mata,gaza bawa kanta amsa taui don ita dai yasan yau ta fara ganin salma,babu kuma abunda ya hadata da su balle tace ko ta mata wani abun ne
''salma,bana so fa irin wadan nan halayyar naki kin sani sarai ko''mami ta fada cikin dan hade gira
''yi haquri mami,nima ba wani abu nake nufi ba''
''jeki maryam ki hutar da kanki kiyi iya cikin abdallah kawai,shima din kiyi simple kada ki dauka da wuya''
''to''
ta gada sanna ta miqe ta shige kitchen dinmami ta nita da kallo,yanayin yarinyar na burgeta,sanyi sauqin kai da kawaic yakanah da danne abu cikin rai
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:51 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺
▶1⃣6⃣
jallop din couse couse ta hada mishi wadda ta wadata da carrot grean beans da piece,sai qoda da hanta a madadin nama,qamshin curry da tyme kadai ke tashi a ciki,yayi shar gwanin sha'awa,sannan ta hada banana apple anda strawberry juice,baaba uwani ta barwa gyaran gun ta wuce ta shirya dining,duk suna zube a falon kowacce da abinda take,ko saahen da 'yar uwarta ke zaune bai isheta kallo ba tamkar ba 'yan uwa ba,taji dadi da bata tadda mamin cikin falon ba don haka tana kammalawa ta ahige daki don ko alama bata buqatar zama acikinsu
mutum ce ita mai jan mutuncinta da gudun wulaqanci,
har magariba abdallah bai shigo ba hakanan basu fasa jiransa ba,ana kirayen kirayen sallar isha'i sannan salma fa fara hada tarkacenta tana yima mami sallama,bata kai ga fita ba abdallah ya shigo
sanye yake da jeans baqi da red din t.shirt hannayensa soke cikin aljihun wandonsa,kan sa yasha gyara sai qyalli yake sumar ta masa kyau sosai,ma'abocin qamshi ne hakan yasa turare ke masa rakiya duk ta inda zai gifta
duk yadda salma ta dauki zafi ganinshin da tayi sai taji sakayau tamkar ma bai mata komai ba,ta saki ajiyar zuciya wadda har sai da ta fito fili
''a'ah,yaushe ka shigo gidan?''inji mami
''b fore isha,na shigo nayi wanka ne zan fita sallar isha ne waccar yarinyar ta tsaidani zubaida take ko''
dukansu babu wadda bata shaqa ba,mami ce ma ta dan tare masu don ba dadi
''amma dai kasan ana jiranka tun dazu ko''
ya karuar da wuya yana kallon mami
''hakan ne yasa ma na shigo yanzu mami,don nasan kaskar nan na jirana''
kasa magana mamin tayi salma ko da tasan cewa da ita yake wani abu ya tokare mata wuya,tuni qwalla ta ciko mata ido,cikin rawar murya tace
''abdallah ni kake cewa kaska''
yayo wani dan qaramin murmushi irin na gefan bakin nan
''mene don ance miki kaska,ita ba halittar Allah bace kamar yadda kike''
kai ta girgiza tare da cewa
''na gode abdallah''
fuu ta zagayeshi ta wuce
mami ta soma kiranta tare da yunqurin binta,da sauri ya sha gaban mamin yana murmushi
''qyaleta don Allah mami,indai salma ce zata dawo''
harararshi ta danyi
''saboda ka saba mata haka ko,to saddiqa na daki saura itama ka wulaqanta tan kaji abdallah''yarfe hannu hayi cikin gajiyawa
''again mami?''kafin ta bashi amsa saiga saddiqar ta fito tana sakin hannu rigarta wanda ta tattareshi saboda alwalar data daura
bakinta a waahe take fadin
''oyo yo ya abdallah''hannu ya dan daga mata
''🖖🏼qanwa,yaushe ke kuma kika zo?''
murmushi ta saki hade da kashe ido daya cikin sigar son jan hankali
''cikin awa ta ta kusan hudu nake da zaman jiranka,kuma naga na kiraka nace maka zanzo''
ya dage kafadunshi
''nayi,tsammanin mami zaki gaida ko qanwata''
''ni gunka nazo''tace cikin salon shagwaba
''kuma kinga yanzun bani da time,time din mami na ne,jiya na dawo kinga baici ace mun gama hirar yaushe rabo ko,da zaki yi tafiyarki next time na baki appointment''yana murmushin mugunta qasan zuciyarsa ya fada,duk da yana jin yadda mami keta zungurinshi amma sai yayi kamar baiji ba
saddiqa gwanar girman kai da ganin ta isa ce,ki tayo tafi qarfin abdallah ya mata haka,son haka ta figi gyalenta wanda shi da babu duk daya
''abdallah....wai da ka fuskanci ina sonka shine ya baka damar takani yadda kaga dama,to wallahi aji na ya wuce nan''
murmushi ya kuma saki wanda ya qarawa kyansa kyau da kwarjini
''ni kaina nasan ke me aji ce''qufula ta sake yi don tuni ta fuskanci magana yake yaba mata a fakaice
''to indai don son da kake taqama ina maka ne daga yau na daina son naka sai me?''
''fine kin huta wallahi,kin kuma burge abdallah''wani zafi taji ranta na mata tuni ta durfafi fita ba tare da ta yima ko mamin sallama ba kamar yadda salma tayi
da sauri mamin tayi yunqurin binta,ya sake shan gabanta da hanzari
''pls mami ki qyaleta itama,wallahi hutu ta zabarwa kanta,hukuncinta yayi dai dai''
wata iriyar harara ta maka mishi
''matsa min abdallah agun tun ban sabar maka ba''
baice uffan ba ya janye gefe ya bata hanya,sai yayi komawarsa saman dining yayi zaune abinshi yana kallonsu
tana cimmata sai ta saki kuka,mamin tadan daddaki kafadarta a hankali
''meye kuma na kuka haka saddiqa da girmanki''ba don mamin bace da sai ta daka mata harara,amma sai ta toge tace
''haba mami,don kawai ana sonshi zai tsaya yana wulaqanta ni,yasan fa koni wace,su waye ke sona,to an daina sonshi din ma''
''ya isa daina kukan haka,ki barni da shi kinji''
da qyar ta lallaba saddiqan ta tafi,ta iso kan dining din inda abdallan ke zaune hankalinshi kwance tamkar babu abinda yayi,kujera ta ja ta zauna
''abdallah so kake kawai ka dauko min magana,kasan Allah akan haka zamu saba ni da kai?''
''ya salaaam....mami me kuma nayi da kike fadin wanna maganar mara dadi?''
''ka sani sarai abdallah yadda muke da yaran nan,ka san kuma irin magan ganun da ake tayi a kanka ko?,to ni na gaji gaskiya,ka zabi wadda kake so acikinsu kawai kowa ya huta abun ya isa haka''
''banza a banza kawai,maras kunyar qarya,gidan da kike taqama da shi ina cewa 'yar karo ce ke''
surutan wata matashiya kenan lokacin da take shigowa falon,matashiya ce 'yar zamani wadda shigarta kadai ta isa nuna maka hakan,sanye take da fitted gown wadda tabi lafiyar jikinta,kanta daure da roses sai swagger dinta mai sarqa rataye a kafadarta,takalmin qafarta kuwa kai kace sama take shirin tabowa saboda tsininsa,fuskarta tasha fente fenten kwalliyar zamani
''a'ah salma,ke da wa kuma,hali zanen dutse''inji mami da ta tsaya tana kallonta
''ni da waccar agolan gidan taku mana,duk randa nazo gidan nan sai ta nemi raina min hankali,wallahi abdallah ka ja mata kunne ni ba sa'arta bace,ni na hana ka sota da zata dinga neman huce haushinta akaina,ina ruwan biri da gada,nafsi nafsi kawai''
kafadunshi ya daga yana ware hannayenshi🤷🏻♂
''ina ruwan abdallah ya taku,kina da baki kema fa''ya fada cikin ko in kula
ta yamutse fuska
''baka fa da kirki wani lokacin wallahi,watsamin to qasa a ido,mami kina jinsa ko''
murmushi tayi
''bismillahi Allah,ai kun fara kuma kenan''
ya dubi mama
''manta da ita mami,ni zan wuce masallaci''
''ni matsalata da kai waqanci wlh,ka sani fa sarai saboda kai na zo,shine zaka wani fita''ta fadi mishi tana kallonshi bayan ta zauna tana sabule cogen qafafunta
''sai na fasa sallar juma'a saboda sarauniyar matan duniya ta zo''ya fada yana yin gaba abinsa
''a'a,ni bance ba amma sai yaushe zaka dawo?''
''qarfe biyar,bit ban tabbas ina iya wuce hakan,idan zaki iya jira na fine''
''ina jira sai ka dawo''
ba tare da ya amsata ba ya qarasa ficewa
maryam na kichen take jiyo su
tunda ta shiga kitchen din bata fito ba sai da ta kammala girkin,lokacin da ya fito mami bata falon sai baquwar da taji an kira salma dake kwance dai dai kan three sitter,kanta ta dago tabi maryam da kallo,hada idon da sukayi bak sata dauke idonta ba
''sannu maryam,kada dai ace har kin kammala?''
inji mami dake saukowa daga saman bene
''eh na gama mami''ta amsa mata bayan ta tsagaita daha tafiyar da takeyi
''sannunki''ta amsa mata sannan ta juya don shigewa dakinta,tana jiyota tana tambayar mamin wace ita?saidai bata ji amsar da mamin ta bata ba
kiran da mamin ta yi mata ne ya sake fito da ita tun bayan shigarta dakin wanda wanka kawai taui ta saiya kayanta tayi salla,biyi taga 'yan matam sun zama,saidai iya wannan sanhe take da riga da wando wadanda suka bayuana surarta,inda Allah ya taqaita siririya ce sosai,
tadan dauke kanta zuwa sashen da mamin ke zaune
''gani mami''
''yauwa maryam,baki fito kinci abincinki ba,ga baqi yau agodan amma kin zauna a daki''
''mami na qoshi ne sai anjima''
''to zauna muyo hira,bana son kina zaman dakin nan ke daya,na gaya miki nafison ki dinga jin a ranki ke diya ta ce,wannan sunanta salma 'yar qanwata ce,waccan kuma sunanta saddiqa ita kuma 'yar yaya na ce,dukansu sunzo yoma abdallah sannu da zuwa''
''sannunku''ta fada cikin sassanyar muryarta
amsawar ganin dama suka mata tamkar wadanda aka tilasta,wanda hakan sam bai,mata dadi ba,har taji zamansun ma guri daya babu marching,don sam bata son wulaqanci,maca ce ita mai karamci shi yasa ako yaushe take tsammanin karamci daga gurin duk wanda zata mu'amaleshi
''am...mami da wai kitchen zan koma in dora abincin dare''
''baki gajiya maryam,a qa'ida ai kin gama girkinki na yau tunda sau biyu ne a rana ko''
kanta na aqasa tayi murmushi
''ba aikinta kenan ba,ki barta mana mami''inji saddiqa wadda ta dora qafa daya kan daya tana danne danne waya da bai wuce tana charting ne
''ba komai mami,ai ba wani qa'ida tsakanin mu,kuma ko ba haka bama ai kinga baqi aka yi,kuma aikin ya abdallah nake,tunda aikinsa nake kinga ba laifi na giwa wadanda suka zo gunshi abinci''
sosai ta burge mamin,tana son mutum mai sauqin kai,wanda ta fuskanci halin maryam ne
yayin da salma da,saddiqa suka dago kai suka kalleta,salma ta kasa shiru
''hmmmm,lallaikam,dadin abun ma biyanka ake ba''
sai abun ya bawa maryam din mamaki,to meye kuma hadin kaska da kifi,me haka kuma,me tayi mata,gaza bawa kanta amsa taui don ita dai yasan yau ta fara ganin salma,babu kuma abunda ya hadata da su balle tace ko ta mata wani abun ne
''salma,bana so fa irin wadan nan halayyar naki kin sani sarai ko''mami ta fada cikin dan hade gira
''yi haquri mami,nima ba wani abu nake nufi ba''
''jeki maryam ki hutar da kanki kiyi iya cikin abdallah kawai,shima din kiyi simple kada ki dauka da wuya''
''to''
ta gada sanna ta miqe ta shige kitchen dinmami ta nita da kallo,yanayin yarinyar na burgeta,sanyi sauqin kai da kawaic yakanah da danne abu cikin rai
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:51 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺
▶1⃣6⃣
jallop din couse couse ta hada mishi wadda ta wadata da carrot grean beans da piece,sai qoda da hanta a madadin nama,qamshin curry da tyme kadai ke tashi a ciki,yayi shar gwanin sha'awa,sannan ta hada banana apple anda strawberry juice,baaba uwani ta barwa gyaran gun ta wuce ta shirya dining,duk suna zube a falon kowacce da abinda take,ko saahen da 'yar uwarta ke zaune bai isheta kallo ba tamkar ba 'yan uwa ba,taji dadi da bata tadda mamin cikin falon ba don haka tana kammalawa ta ahige daki don ko alama bata buqatar zama acikinsu
mutum ce ita mai jan mutuncinta da gudun wulaqanci,
har magariba abdallah bai shigo ba hakanan basu fasa jiransa ba,ana kirayen kirayen sallar isha'i sannan salma fa fara hada tarkacenta tana yima mami sallama,bata kai ga fita ba abdallah ya shigo
sanye yake da jeans baqi da red din t.shirt hannayensa soke cikin aljihun wandonsa,kan sa yasha gyara sai qyalli yake sumar ta masa kyau sosai,ma'abocin qamshi ne hakan yasa turare ke masa rakiya duk ta inda zai gifta
duk yadda salma ta dauki zafi ganinshin da tayi sai taji sakayau tamkar ma bai mata komai ba,ta saki ajiyar zuciya wadda har sai da ta fito fili
''a'ah,yaushe ka shigo gidan?''inji mami
''b fore isha,na shigo nayi wanka ne zan fita sallar isha ne waccar yarinyar ta tsaidani zubaida take ko''
dukansu babu wadda bata shaqa ba,mami ce ma ta dan tare masu don ba dadi
''amma dai kasan ana jiranka tun dazu ko''
ya karuar da wuya yana kallon mami
''hakan ne yasa ma na shigo yanzu mami,don nasan kaskar nan na jirana''
kasa magana mamin tayi salma ko da tasan cewa da ita yake wani abu ya tokare mata wuya,tuni qwalla ta ciko mata ido,cikin rawar murya tace
''abdallah ni kake cewa kaska''
yayo wani dan qaramin murmushi irin na gefan bakin nan
''mene don ance miki kaska,ita ba halittar Allah bace kamar yadda kike''
kai ta girgiza tare da cewa
''na gode abdallah''
fuu ta zagayeshi ta wuce
mami ta soma kiranta tare da yunqurin binta,da sauri ya sha gaban mamin yana murmushi
''qyaleta don Allah mami,indai salma ce zata dawo''
harararshi ta danyi
''saboda ka saba mata haka ko,to saddiqa na daki saura itama ka wulaqanta tan kaji abdallah''yarfe hannu hayi cikin gajiyawa
''again mami?''kafin ta bashi amsa saiga saddiqar ta fito tana sakin hannu rigarta wanda ta tattareshi saboda alwalar data daura
bakinta a waahe take fadin
''oyo yo ya abdallah''hannu ya dan daga mata
''🖖🏼qanwa,yaushe ke kuma kika zo?''
murmushi ta saki hade da kashe ido daya cikin sigar son jan hankali
''cikin awa ta ta kusan hudu nake da zaman jiranka,kuma naga na kiraka nace maka zanzo''
ya dage kafadunshi
''nayi,tsammanin mami zaki gaida ko qanwata''
''ni gunka nazo''tace cikin salon shagwaba
''kuma kinga yanzun bani da time,time din mami na ne,jiya na dawo kinga baici ace mun gama hirar yaushe rabo ko,da zaki yi tafiyarki next time na baki appointment''yana murmushin mugunta qasan zuciyarsa ya fada,duk da yana jin yadda mami keta zungurinshi amma sai yayi kamar baiji ba
saddiqa gwanar girman kai da ganin ta isa ce,ki tayo tafi qarfin abdallah ya mata haka,son haka ta figi gyalenta wanda shi da babu duk daya
''abdallah....wai da ka fuskanci ina sonka shine ya baka damar takani yadda kaga dama,to wallahi aji na ya wuce nan''
murmushi ya kuma saki wanda ya qarawa kyansa kyau da kwarjini
''ni kaina nasan ke me aji ce''qufula ta sake yi don tuni ta fuskanci magana yake yaba mata a fakaice
''to indai don son da kake taqama ina maka ne daga yau na daina son naka sai me?''
''fine kin huta wallahi,kin kuma burge abdallah''wani zafi taji ranta na mata tuni ta durfafi fita ba tare da ta yima ko mamin sallama ba kamar yadda salma tayi
da sauri mamin tayi yunqurin binta,ya sake shan gabanta da hanzari
''pls mami ki qyaleta itama,wallahi hutu ta zabarwa kanta,hukuncinta yayi dai dai''
wata iriyar harara ta maka mishi
''matsa min abdallah agun tun ban sabar maka ba''
baice uffan ba ya janye gefe ya bata hanya,sai yayi komawarsa saman dining yayi zaune abinshi yana kallonsu
tana cimmata sai ta saki kuka,mamin tadan daddaki kafadarta a hankali
''meye kuma na kuka haka saddiqa da girmanki''ba don mamin bace da sai ta daka mata harara,amma sai ta toge tace
''haba mami,don kawai ana sonshi zai tsaya yana wulaqanta ni,yasan fa koni wace,su waye ke sona,to an daina sonshi din ma''
''ya isa daina kukan haka,ki barni da shi kinji''
da qyar ta lallaba saddiqan ta tafi,ta iso kan dining din inda abdallan ke zaune hankalinshi kwance tamkar babu abinda yayi,kujera ta ja ta zauna
''abdallah so kake kawai ka dauko min magana,kasan Allah akan haka zamu saba ni da kai?''
''ya salaaam....mami me kuma nayi da kike fadin wanna maganar mara dadi?''
''ka sani sarai abdallah yadda muke da yaran nan,ka san kuma irin magan ganun da ake tayi a kanka ko?,to ni na gaji gaskiya,ka zabi wadda kake so acikinsu kawai kowa ya huta abun ya isa haka''