← Book details Abadan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 103

Sashe 3

Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

a falo ta taddata''kinga kuwa maryam yadda rigar nan ta miki,Allah ya kawo miji na gari,gaskiya ba qaramar hidima zamu sha ba''
''har yanzu babu abinda ya ragu a surutun raliya''
''haka miskilanci kyau da ajin maryam diyana har yau yana nan''duka sai suka sa dariya,yana daya daga abinda ya sa qawancensu ke ma maryam dadi,raliya akwai vbarkwanc,inda kuma halinsu yazo daya ta bangaren haquri da dauke kai

qarar bude get din gidan ne yasa suka ankara da isowar abban fadil
''kinga har sun iso ina nan a zaune,biyar harda kwata''maryama ta fada tana miqewa
''kinga malama koma ki zauna tunda sun riga sun iskemu tare ai bakya tafi ba,ki bari mu tari baqinmu qarasa ladarmu tare''babu yadda ta iya haka ta koma ta zauna,ta fiddo wayarta tqna yiwa hndatu texs ta sanar da mama tana nan tahowa raliya ce ta tsaidata

tana cikin sending sallamar baqin ta ratsa dodon kunnenta,a sanyaye ta dago tana amsawa,su uku ne abban fadil na hudu,duka sai taji ta a takure gashi raliya ta shiga ciki sako mayafi,sai ta miqe tana daukar jakarta tace
''sannunku da zuwa,abban fadil yanzu raliyan ta shiga ciki bari na mata magana''
dakatar da ita yayi
''a'ah yi zamanki,nasan a gajiye kike kunsha aiki bari na fito da ita,jabir bari na fito da madam''

falon yayi shiru su duka harda baqin,wayarta na hannunta tana danne danne amma sai take jinta a takure,gashi daga raliyan har nasir din shiru kamar an shuka dusa
''madam haka ake kula da baqi?''
tajiyo maganar lokaci guda,ta daga kanta don ganin me maganar,shije zaune opposite dinta,sanye yake da shadda hartin da hula,murmushi ta danyi a taqaice
''ai bani bace matar gidan,ku jirayi fitowarta''
''ke da ita din ai daya ne,don na tabbata yarda ce tasa suka barki da baqinsu''
sai ta maida idonta kan wayarta don bata da abun ce masa,Allah ya taimaketa masu gidan suka qaraso

gaishe gaishe ne suka biyo baya da 'yan hirarrki,saidai duk lokacin da bisa kuskure idonta ya kai sashen da wanda ake ka kira da jabir sai ta tsinci idanunsa na bisa kanta,wanda hakan har ya fara damunta,nasir ya musu jagora zuwa dining domin cin abinci hakan yasa ta cema raliya
''to ai na gama ko,bari na wuce gida''
''tunda ba da mota kika zo ba ki bari mu kammala sai mu wuce tare ko?''
ta jiyo muryar jabir din na fadi
''kasan kuwa kusa da unguwar take ba''inji nasir
''haka,ne fa,shikenan kin huta hawa keke napep''inji raliya
''amma kinsan baxaiyiwu su kaini gida ba,idan mama ta ganni kuma nace mata su waye?''
''indai mama kike ji zan kira tq na gaya mata''inji raliyar

cikin zuciyarta ta ja tsaki,
''wannan jabir dan shiga hanci ne wlh''babu damar musu tunda duka ido na kanta haka ta koma ta zauna tana jira su kammala,yana bisa dining din amma idanunsa na kanta har raliya ta ankara,cike da gulma ta tabota
''ke,inafa tsammanin kinyi tsuntuwa yau a gidannan''
cikin rashin fahimta tace
''ta me fa?''
hararta tayi ''kiji min 'yar rainin sense,kina nufin baki lura da irin kallon da jabir ke miki ba?''
''shine me?''
''wlh sonki yake bisa dukka alamu''
wannan karon ita ta maida nata hararar''kijimin mata,kawai daga kallon sarkin fawa sai miya tayi zaqi?''
''wlh da gaske nake,jabir mutumin kirki ne diyana,kada kice zaki qishi don Allah''
''a'ah,kinji ta da wani guntun wa'azinta,ashe har yace miki ma yana sona ko?''
''ni na gaya miki zai fada miki''

Can saman dining dinma jabirne ke cewa cikin qasa qasa da murya
''kai mutumina nifa nazo gidanka a sa'a,Allah yasa bata da wani''
dariya ya saka''tuni na harbo jirginka ai,indai bilkisu ce a iya sanina ba'a tsaida mata miji ba''
''ai kuwa bazan tsaya kallon ruwa ba,a yau zan kafa kaina''

A bakin layinsu tasa ya tsaida motar,ta bude murfin tana cewa
''na gode''
''haba madam da sauri haka?''
sai ta juyo cikin mamaki tana dubansa
''eh mana,ya zaki min illa kuma ki tafi ki barni ba tare da kin bani magani ba''
ci gaba tayi da dubansa,sai ya saisaita nutsuwarsa,baiji ko,nauyi ba ya bayyana mata duka manufarshi,da farko ta ja masa yace shikam yace baisan wannan zancan ba,babu inda,zata tafi ta barshi cikin qila wa qala,idan,ko ta tafi to zai tare ne a qofar gidansu har sai ta amsa masa koda zai shekara

maganar da sukayi da raliya ce ta fado ranta
''maryam,wlh indai aure kike so kiyi kada kiqi karbar tayin jabir matuqar yayi miki maganar,jabir bazai taba tararki da maganar banza ba,nasan jabir tuntuni,abokin nasir ne da dewa,halayensu kusan daya,hakan shi ya qara danqon abotarsu''
ita kanta a zahirance bata ga wani aibu ba tattare da jabir din,yana da kyau daidai wanda duk hassada ba zaka kira shi mummuna ba,a iya abinda ta gani da bayanan da raliya ta mata ta fuskanci zata iya amsa tayin jabir,ko don ma ran mahaifiyarta yayi fari,ko don ta samu itama ta zauna a nata dakin kamar sauran qawayenta da 'yan uwanta

ganin shirun nata yayi yawa yasa ya sake marairaice mata ga tsammaninsa zata wofantar da buqatarsa ne
''shikenan,Allah ya shige mana gaba''
''um um maryama,wannan ba amsa bace,kice ina sonka jabir shine magana''
kanta ta girgiza cikin alkunya tace''don Allah ka barni na wuce gida,na tabbata zan sha fada gun mama,don na kai magariba a waje,tunda ka kwaahe min numbers ai sun isa''

fitowa yayi ya zagayo ya bude mata murfin yana cewa''shikenan,kin bani izini na kiraki?''
kai ta gyada masa,kafin ta dauko jakarta yayi sauri ya rigata ya bude zif din ya jefa mata kudi,ta noqe alamun ba zata amsa ba shi kuma yace indai bata karba ba to tana nufin bata sonshi,tilas ta karbi kyautar tasa,sukai sallama amma sai taga ya ja ya tsaya,kallonshi tayi ya daga mata gira
''sai na hango,shigarki gida don tsaron lafiyarki da kuma gane gidan naku koda na tashi zuwa''
murmushi kawai tayi tajuya domin shigewa layin nasu

katsam idonta kan isyaku,kai ya gyada sannan ya kwasa da gudu yayi gida,la'ilaha illa nata subhanaka inni kuntu minaz zalimin,tasan tamkar a idanun iyayenshi tayi,cikin fargaba taci gaba da takawa jabir na mata rakiya da idanu har ta shige gidan

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📓✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:49 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺

▶4⃣

sai da tayi dira dira a soron kafin ta gano ainihin hanyar wucewa,saboda cike yake da 'yan zance,can hauwa can binta can maijidda kai abun takaicin ma harda zainabu wadda du du du ba zata wuce shekaru goma sha hudu ba kacal a duniya
ta tsakiyarsu ta raba ta wuce,taji dadi sosai da babu wadda ta tanka mata a cikinsu

cirko cirko ta samesu a tsaye cikin tsakar gidan,inna hadiza ce da baba huwaila sai babansu dake bakin famfo yana daura alwala da alama haramar sallar isha'i yake yi,sai kuma isyaku dake qame a gefe da alama tuni ya gama fesar da abunda ya qunso
''la ha ila ha illallahu,muhammadu dan abdullahi''suka dauko salatin tare yayin da huwaila ta dire ita daya ta kuma dora
''wlh yaya da gaske ne yaro baya qarya,tayani gani don Allah,suturar jikinta ma ai ba da ita ta fita ba,lallai dandi na dada samun gindin zama a gidannan''

inna hadiza dake ta faman gyada kai tana kallon maryamu wadda ke tube takalmanta a qofar dakinsu ba tare da ta dubedu ba tace''qwarai da aniya,ya gama yawon barikin da ita ya kwashi na kwasa ba dole ta canza sutura ba,yo zata shigo mana gida ne da najasa ne''
''ke meramu zo nan''
kiran baban nata da baqin qazafin da suka jefeta da shi ya daki zuciyarta lokaci guda,a sanyaye ta dawo gabansa ta durqusa kanta a qasa
''wanne dan iska ne ya dauko ki a mota har gidan ubanki?''
muryarta a sanyaye tace''ba dan iska bane baba,gidan raliya muka hadu yace yana sona''
''yana sonki?''
huwaila da hadiza suka fadi kusan a tare

bai biya ta kansu ba ya dora da nashi bayanin
''alhmdl dama ni na gaji,na gaji wallahi kullum rana a unguwarnan sai anyi da ni kan na ajjiye babbar mace a gida,saboda haka ki shaida masa matuqar da gaske yake to na bashi kwana goma ya fito ayi kowa ma ya huta''
''yo idan banda abunka malam amadu saurayin qwarai ne zai dinga yayibar yarinya yaro kwararo kwararo kuma yace zai aureta,ai qarya ne dan yaudara ne kawai''inna hadiza ta,cafe maganar
''oho,koma dai meye nidai na gama magana,tashi ki bani guri''

jikinta a sabule ta miqe tayi hanyar dakinsu,har yanzu kunnuwanta badu daina jiyo mata qananun magan ganun da suke yi bq marasa dadi akanta ba,taimakon da Allah yayi mata daya yau baban nasu bai bi ta kansu ba yayi ficewarsa masallaci,wannan wace iriyar masifa ce?,tamkar ita ke da ikon rubutawa kanta qaddararta?,ita ta hana kanra aure ne?,shikenan a rayuwa babu dama Allah ya qaddara maka wani abu sai jahilan cikin mutane su dinga ganin tamkar kai ka jawowa kanka ko da amincewarka hakan ta faru?,

mamanta na cikin rumfar a zaune amma tamkar bata a cikin gidan,wannan dabi'arta ce,tana da dauke kai da yakana akan 'ya'yanta,da wuya ka taba mata yaro kaji bakinta,da wannan damar mutanen gidan ke amfani suke cin karansu babu babbaka a kansu,duk da wasu lamuran hindu na masu tambotsai idan taga cin kashin yayi yawa,don ma mama na kwabarta

yanzun ma baqinciki ne ya hanata motsi da kuma umarnin maman,don tana zaune ne tana karatun waec da fitilar qwai a gabanta,sallamar ta kawai hindun ta amsa ta dora da cewa
''yanzu fisabilillahi yaya maryam haka zaki ci gaba da zama ana miki cin mutunci ba zaki kare kanki ba?''
''kinci gidanku nace hindatu,nace kinci gidanku,da baban nata zatayi sa'insa ko da matan ubanta?,ke maryamu,ina kika samo kayan jikinki?''
kai ita kam dai ta shiga uku,wato ko ina cikin tuhuma take
''mama tsarabar da raliya ta bani ce,na tayata aiki tace bazan taho ba sai nayi wanka,shine aciki na cire nasa wannan''
''madalla,amma daga yau kada ki sake ki sake kaiwa magariba a waje kina jina ko?''
''to mama''
Chapter 3 · 0% Book details