← Book details Abadan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 103

Sashe 78

Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

''maryam,me kika ce?''inji mami,sai tsoro ya sake kamata kada dai ace taji muryoyinsu,ta dan daga muryarta tace
''am...am...cewa nayi...cewa nayi dama ina bandaki ne wanka nake''ta fada cikin tsoro
''ok,to shikenan nari na shiga gun abdallah dukkanku baku karya ba shima daga cemin zaije wanka shiru,idan kin fito ki samemu a dining''ajiyar zuciya ta saki da taji alamun mamin ta tafi

Miqewa yayi ya sauka a gadon jin mamin ta soma qwaqwasa qofar dakin nashi,tana kallonshi ya murza key ya bude dakin,lallima *SAMUN WURI*(by maman farida),har ma wani key ya saka mata a daki kamar nashi dakin,bata tanka masa ba har ya fice don kada kulashi y sake dawowa ba qaramin dan neman magana bane kadan daga aikinshi

Yana fitowa suka hada ido da mami,duk sai ya dububurce,kunyarta yaji ta kamashi ganin yadda ta harde hannunta aqirji ta zuba masa ido,sai ya soma shafa qeyarsa,dariya ma ya bata ta kama hannunshi suna tafiya dining tace
''yaushe abdallah ya fara kunyar maminshi?,hala maryam ce ta koya masa?''baice komai ba sai murmushi da yayi

Cikin atamfa ta shirya super sharaton kalar lemon green da milk,ba qaramin kyau tayi mata,duk da ba wani makeup tayi ba amma hodar data shafa tabi fuskarta sosai ta qawata farar fatarta,ta sanya dan kunne sa sarqa na fashion lemon green

Tun daga nesa ya kasa kaucewa kallonta,wani kishinta da sonta na ratsashi,tayi masa kyau matuqa da gaske don bata yafa mayafi ba ma,tayi hakan ne sabida mami,tasan zata iya ganin baiken yafa mayafin da tayi bayan su biyu ne cikin gidan

Ta rusuna ta gaida mamin cikin kunya da girmamawa,ta amsa tana murmushi tare da dubansu
''nikam ai gaba dayanku kun fini kyawun gani,fatarku tayi kyau kamar ma ba'a qauye kuka zauna ba,lallai su inna wuro sun iya kiwo,dole ne kam mu nuna godiyarmu''dukkansu dariya sukayi ta ja kujera ta zauna tana gaida aliyun,ta qasan ido yake dubanta kana yayi qasa qasa da murya
''baby kinyi kyau fa ''banza tayi da shi kamar bata jishi ba,bata mantashi ba bai kunyar idon mamin yanzun sai ya jawo mata abun kunya tana zaman zamanta

Duk da haka bai qyaleta ba ganin taqi kulashi,hannu ya dinga sawa cikin kwanonta yana cinye mata chips dinta,nan ma qin biye masa tayi,saidq mami ta kula tukun
''a'ah,abdallah ya haka?,ga naka cikin olate nan kuma ma naga tare muke ci da kai ko?,don me yau zaka matsa mata''shi kansa sai ya danji kunya da ya tuna tare fa suke ci da mamin ko yaushe amma yau ya manta da ita

Ringin na wayarta ta jiyo wadda ta tabbata abdallah ne ya kunna mata don ta ajjiye ta ne kawai bata kai ga kunnawar ba,ta miqe daga cin abincin ta nufi dakin
sunan hindatu ta gani kan screen dinta,dan uwa mai dadi,wani farinciki taji ya kamata ta haye kan gado kana ta amsa
''yar uwa rabin jiki''inni hindatun,dariya maryam ta saki sannan ta qarashe mata
''banga mai kamarki ba''
''da gaske adda maryam kun dawo ya abdallah ya samu lafiya?,yanzu mukayi waya da mama ta gayamin mamin abdallah ke fada nata jiya bayan dawowarku,wallahi kinganni bani da lpy amma har naji na warke''
''eh da gaske mama take hindatu yanzu haka muna gida,ya gida ya mai gidan......''
katseta hindatun tayi cikin zumudi
''inaa,wlh adda maryam,bazan iya zama ba,ki duba hanya gani nan zuwa''tun kafin ta amsa ma ta katse wayar,ta dubi wayar tana murmushi
''hindatu uwar rawar kai da karadi,har yau ba'a canza hali ba''

Tana fitowa sukayi karo da baaba uwani na fitowa daga kitchen,cike da murna baaba uwani ta kalleta
''a'ah maryamu''
''baaba uwani''itama ta amsa mata fuskarta dauke da murmushi,sai da suka bata mintina suna hira a gun kafin ta wuce

ko da ta koma dining din tuni su mami sun kusa kammalawa,daman ita tuni taji ta qoshi zuwan hindatu kawai yasa ta qoshi,don haka jujjuya abincin kawai take
''har yanzu banga abun kirkin da kika ci ba maryam''
''na qoshi mami''ta fada tana mirmushi
''ko a ni'ima ma haka takeyi mami,batason abinci''inji abdallah cikin salon jan fada

Ya dan ja kujerarsa baya alamun ya qoshi yana hamdala abayyane
''mami,tun jiya fa aka soma turo min saqon komawa gurin aiki,don watanni da muka diba sun cika,so jiya bamu jima da dawowa ba saiga tex dinsu,zamu zauna da mr presdent gobe a abuja insha Allahu''
shiru mami tayi na dan lokaci kana tace
''anya Abdallah ba za'a haqura da aikin nan ba kuwa?''
murmushi yayi kadan bayan yayi miqa
''ba komai mami,ai duka aikin taimakon al'umma ne,idan lokacin barin yayi za'a barshi,yanzun aikin da na fara nakeso na idar da shi,alhj hamza mai qusa ina da zargi mai qarfi akansa''
''Allah ya taimaka,yanzun yaushe zaka tafi''
''da la'asar in sha Allahu,jirgin yamma ne''
''Allah ya kaimu''
satar kallon maryamun yake yaga ya yanayinta yake saidai sam taqi yarda su hada ido

*mrs muhammad*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[7:06pm, 10/6/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶5⃣7⃣

*Daga sahal dan sa'ad Allah ya yarda da shi yace''wani mutum yazo wajen manzan Allah S A W,sai yace,ya manzan Allah,nuna min wani aiki wanda idan na aikatashi Allah zai soni mutane zasu soni?,sai manzan Allah S A W yace: KA GUJI DUNIYA(dadin dake cikinta da qyale qyalenta) Allah zai soka,sannan KA GUJI ABUN HANNUN MUTANE MUTANE ZASU SOKA*
*_ruwayar ibnu maaja_*

Sam taqi dubansa,hidimad gyara gurin da suka kammala cin abinci kawai takeyi,ya san tana sanen rayi haka
''idan kinsan wata baki san wata ba yammata,duk abunki sai na dan more kan na tafi''ya fada cikin zuciyarsa yana danne danne waya,kansa ya dago kamar wanda ya tuna da wani abu da gaske ya dubeta
''af,maryam,taimakamin ki dauko mim wasu takaddu cikin cupboard please''kamar ba zata je ba haka taji saboda kunyar idon mami amma sai taga mamin ma ta sauko daga kan dining din ta koma cikin falo tayo zamanta kan kujeru,ba tare da tace komai ba ta miqe ta nufi inda ya aikata din.

Ta kusa aqalla minto goma tana dube dube cikin dakin nasa amma sam bata ga abinda yake fada din ba,dole ta juyo ta fito don ta sanar masa,a kusa da maminta tadda shi yana zaune yana nuna mata abu a waya,ta dan rusuna kadan''ban gansu ba''tace da shi,ba tare da ya dago ya dubeta ba yace
''ki sake dubawa dai da kyau,suna nan ciki ko locker din mirrow dina''a yanzu kam jikinta ya fara bata aiken bogi ne,don iya dubawa tq duba ko ina din,amma sabida bata son musu yasa ta miqe ta koma.

Ko minti biyu batayi da komawar ba ya dafe kai yana fadin
''af,na manta asge na sauya musu gu shi yasa ta kasa ganinsu,bari naje na dauka''ya fada yana satar duban mami,bata ko dubeshi ba har ya miqe yayi hanyar dakin,binsa tayi da kallo tana murmushi can qasan ranta tana fadin''dama ai bazan hanaka kebewa da matarka kuyi sallama a abdallah'',tattare itama ya nata ya nata tayi ta haye sama abinta

A hankali cikin sanda ya tura qofar dakin ya shiga,tana duqe ta duqufa neman takardu
''har yau maryam ke yarinyace na yarda da hakan ba wuya a miki wayo''ya fada cikin xuciyarsa
jingina yayi da qofar ya harde hannayenshi a qirji yana kallonta son ranshi,sai datq gaji da dubawa kana ta dago,ta juyo da niyyar fita amma hankalinta na kan gado tana dubawa ko nan ya ajjiye,dalili kenan da yasa bata ganshi ba har sukayi karo,baya ta ja da sauri,tana yarfe hannunta tace
''na duba ko ina ban gansu ba nikam''.

Hannun nata ya kama yana fadin
''ba wasu takardu dama,son ganinki kawai nakeyi dama kafin nawuce,ma tabbata idan ba haka ba bazaki bari na ganki din ba sai a gaban mami''
so take ta qwace amma ya gwada mata qarfi irin na 'yan maza sai da ya kaita gefan gado ya zaunar da ita kana yayi tsalle ya fada gadon,kwanciya yayi ruf da ciki,kanshi ya dora saman cinyarta ya saka hannayenshi ya zagaye qugunta,ya gama kanainaye jikinta bata da ikon motsi
''ummm,baby,har yau bansan matsayina a gunki ba baby kin barni cikin duhu fa?''ta dan hadiye wani abu,yana nufin yace har yau bai fuskanci komai daga gareta na ko so yake sai ya qureta ya sata fadin abunda bata yi niyya ba
''ka riga da ka san matsayinka tuni a gurina ba tun yau ba''shiru ya danyi kana yace''na riga ni kuma da na manta baby,pls ki sake gayamin''.

Shiru ta sake yi don ya sakata cikin kokwanto biyu,idan ta buda baki abinda duk zata gaya masa ta tabbatarwa kanta qarya take a yanzu,idan kuma ta fadi gaskiyar wanne kallo zai mata,jin taqi cewa komai ya saka shi juyowa da sauri ya koma rigingine duka akan cinyar tata yana kallin fuskarta,sai tayi saurin runtse idonta,murmushi yayi ya saka yatsanshi ya lakace mata hanci
''yar qauye kawai,shi kenan tunda kin barni cikin duhu,idan kuma na mutu kafin na dawo burinki ya cika kenan ko?''
bata san lokacin da ta bude brown oily eyes dinta ta watsasu cikin nashi ba tana zazzaro su,shima kallon nata ya tsaya yi can qasan zuciyarsa wani sanyi na ratsashi
''mutuwa kum....''sai ta kasa idawa ganin yana sake fadada murmushinsa yana lumshe ido,idanun nata ta sake ja ta rufe ba tare da ta qarasa din ba
''a hakan ake so ace ba'a sona?,bansan lokacin da kika koyi yima kanki da kanki qarya ba''.
Chapter 78 · 0% Book details