Sashe 102
Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
''ummi ki yiwa diyarki magana,tafa matsanta min''ya fada qasa qasa yadda abdul_ahad dake sanya socks a qafarshi yana shirin nacci da mami dake cikin toilet tana dauro alwala duka ba zasu jishi ba
baki ta tabe cikin tsokana tace
''meye nawa?,itaku,ina cewa dazu ka siya mata ice cream ka hanamu kace mamarka ce?''
kai ya dan sosa don kada ta gansu a rana su masu dariya ya sunkuya yana daukarta bisa kafadarsa yace
''haka ne fa,mama na tafi ta kowa ai''ya juya ya fita maryam na qyalqyala musu dariya,ganin yaaran na kallonta saboda dariya da suka ha tanayi da basu san dalilinta ba yasa ta daidaita natsuwarta,ta kammala shirya abdus samad ya haura gadon da abdul ahad ke kai,ta dubi abdul ahad
''idan ka kammala addu'anka ka karanta masa shima kafin ya sake komawa baccin''
''to ummi''
gadon mami ta koma ta sake gyara mata gami da shimfida mata abun sallah don ta riga ta saba bata kwanciya sai tayi sallah raka'a biyu,har ta koyawa maryam din ma,saida mamin ta fito sannan ta shiga itama ta daura alwalar
tana bisa abun sallan mami na zaune gefan gadon tana laranta azkar da bata samu damar yi ba,wayarta na hannun abdul ahad yana danne danne,bata fiye damuwa don ya dauki wayarta ba don ta san hakin yaron indai kaga wayar a hannunshi wani abu mai mihimmanci da zai qareshi yake dubawa,Allah ya zubawa yaron tsantsar basira,hankali da nutsuwa,uwa uba ya samu ingantacciyar tarbiyya ta buga misali,ba qaramar tsaiwa maryam tayi kan tarbiyyan 'ya'yanta ba musamman abdul_ahad wanda dama danka na faro kusan shine tubalin sauran 'yan uwansa,irin tarbiyyar daka nashi to sauran ma idan ka haifesu zasu taahi ne kan aninda suka ga na gaba da su nayi wato babban yayansu,saboda ko yaushe suna tare,suna ganin irin abubuwan da yakeyi suma zasuyi qoqarin yin koyi da shi,hakann idan gurbatacciyar tarbiyya ya samu,da sun fara girma zasu bi sahunsa
Ta shafa addu'o'inta kana ta miqe ta ninke abun sallar,mami ta dubeta
''ya kamata kam ki tafi haka ki kwanta maryamu,kullum ace sai kin tayamu hira zaki tafi daki ko kwanta,banda abunki ai bani,kadai ce a dakin ba balle kice kewa zata dameni,ga mai gida na ma baiyi bacci ba''
murmushi maryam din tayi cikin kunyarta din nan da har yau bata canza ba,har yau babu wani abu da ya ragu daga qaunar da mami ke mata sai ninkuwa ma da yayi
''kije ki,kwanta maryam kinji,Allah yayi miki albarka,haqiqa har *ABADAN* bazan daina alfahari da ke ba,kin cika uwa ta gari mai fidda kyakkyawar yabanya,fata na ubangiji ya cika rayuwarku da haske farinciki da kwanciyar hankali,kin haifa min jikoki maryam hudu ne amma inaji sunfi miliyan,sabida samun yara kamarsu wallahi ba don suna jikokina ba sai an tona,Allah ya miki albarka,Allah ya miki albarka''kanta na aqasa take amsawa da amin zuciyarta cike da farinciki da qaunar mami
Wayar tata dake hannun abdul ahad ta dauki tsuwwa wanda tun tana cikin yin sallah ta ji tanayi,abdul ahad ya dubi umminsa
''ummi,abba ke kira tun dazun''yana saukowa daga gadon ya miqa mata wayar,ta riga da ta horesu,sam basa daga mata kira sai sun kawo mata ko sun sanar mata,ta daga kana ta kanga wayar a kunnenta
''please dear ki taho haka don Allah,i nedd you''murmushi ya subuce mata,kunyar mami tasa ta kana magana sai kawai ta katse kiran,minti biyu tsakani saiga tex dinshi
''gaskiya fa ina alkunya da yawa,na baki minti biyar matuqar baki taho ba da kaina zanzo har,gaban mami na sungumeki,kin sani zan iya ko?''murmushi ta sake saki taci gaba da duba agogo
sai da ta minti biyar din sun cika daidai sanan ta miqe ta yiwa mami sallam,a bakin qofar dakinsu mamin taci karo da shi dauke da amatullah,dariya ta subuce mata
''gaskiya kun samu aikinyi,ta yadda kenan zata kwana cikin 'yan uwanta''
''me ruwanki da mu?,kedai ki kuka da kanki,yau sai kin biya dukka bashin da kika ci''kai ta girgiza tana murmushi ta wucesu shi kuma ya shiga dakin
Bandaki ta fada kai tsaye bata zauna ba,sai data yi wanka mai kyau kana tazo ta mulke jikinta da turaruka masu dadi wadanda ta siyosu dazu da rana da suka fita yawin miqe qafa,dukkansu na kamfanin alharamain ne masu dadi qamshi,daya daga cikin kayan baccin data siyo ta cira,doguwar riga ce har qasa mai hannun shimi mai azabar yauqi da santsi tana da dan duhun kala kadan ta sanyata,ta feshe kanta da turaren gashi kana ta rage hasken fitilar dakin ta haura gadon ta kwanta,jin shiru bai dawo,ba ya tabbatar mata yana can ana tataburza wata qila da amatullah,kiran da ya ahigo wayarta ne ya katse mata zancan zucin da take yi,lubabatu ce da hanzarinta ta daga don tana sa ran jin daddadan labari saboda sun baro nijeria hindatun nada tsohon cikin haihuwarta ta biyu ita da hisham dinta,ai kuwa abinda ta zata dinne ta sauka dazu qn samu baby girl da take ta sha'awar haifa,don haihuwar fari namiji ne ABDULKAREEM wanda yaci sunan mahaifin abdallah
''adda na haifawa abdul_ahad mata,din gaskiya tun yau na mata miji,ina son absul_ahad adda wallahi dama yaya abdallah zai barmin shi,amma na sani bazai iya ba don ya fimu qulafucinsa''dariya maryam ta saka tana cewa
''Allah ya tabbatar,zanso haka lubabatu,Allah ya raya mana baby''
''adda sunanki taci fa,nayi alqawari dama ina fatan Allah yasa ta dauko halayenki,maryam sunanta saiki zaba mata nickname''ba qaramin farinciki maryam taji ba take tace
''mu dinga kiranta AMEERA ai yayi ko?''
''yayi adda,Allah ya qara girma,kinga mama ce a gurina(maman maryam din)ga maijidda(kulu,da yake haka suka koma ce mata) ta takuramin sai na bata ta tuna kiki tsarabar da tace tana so,kuma wai abdus samad ya cika mata alqawarin da ya daukar mata''dariya ta saki kana tace
''kice mata sunfi kusa,don abdus samad yanzu,haka,ma ya jima da yin bacci amma gobe zan kira na hadasu'',ta karba suka gaisa kana ta hadata da mama ma suka gaisa sannan sukayi sallama
Bata kai ga ajjiyewa ba kiran shamsiyya (qanwarta yar inna hadiza)ya shigo,suna gama hira zara ta kira sai bintu kamar hadin baki,dukkansu taya ta murna suke kan zuwa ta daya da abdul_ahad yayi,taji dadi sosai kan yadda kullum Allah ke dada hada kansu suka fuskanci gaskiya suka zamo tsintsiya madaurinki daya,tana cikin addu'ar bacci ne jin shirun na abdallah yayi yawa kiran hindatu ya shigo,tana kaiwa kunnenta abdallah ya shigo dakin yana sakin hannun rigar baccinsa da ada ya nannade,dariya ya bata cikin zuciyarta tana cewa hala dambe akasha kafin amatallah ta yarda
''ke kam baki duba agogo?mufa anan qarfe sha biyu na dare''
''tun dazun nake kiranki naji busy wayar taki''
''eh wallahi muna ta waya da su azara''
''lubabatu ai ta haihu,shegiyar gari,dazu naje gidan na gama yi mata tsiya ai,can na samu su shamsiyyan ma....''maryam din na shirin tambayarta tsiyan me abdallah ya wafece wayar ya kara a kunnensa
''sai da safe,a barmin gimbiya ta ta huta hakanan''ya fada,dariya hindatun tayi tace
''ranka ya dade,girman kujerarka,ai kafi gaban haka ma,Allah ya bamu alkhairi''
''ameen,ki gaida min boss(haka yake kirab jabir idan yaso tsokanarsa) da duka yaran''daga haka ya katse wayar yana jifan maryam din da wani shu'umin kallo
Bayanta ya fada kana ya janyota ya rungumeta tsam a jikinsa dukkansu suna murmushi yace
''idan na barki da wannan hindatun yauma saidai na haqura''
murmushi ta saki a boye cikin son jan tsokana
''yanzun ma haqurin zakayi,tunda jibi zamu koma so nake nayi bacci sosai don gobe wuni nakeso nayi a harami ina da addu'o'i sosai''bai bi ta maganarta ba ya fara aike mata da saqonni sannan yace
''wacce buqata kike da shi haka,tunda kika sameni ai baki da sauran matsalar rat
yuwa''murmushi ta saki kaina ta juyo suka koma fuskantar juna numfasinsu na,haduwa guri guda,fuskanta qunshe da kyakkyawan murmushin daya bayyana fararen haqoranta,kasa daurewa abdallah yayi har sai da ya shafi fuskartata yana fadin
''maryam diyana''wani murmushin ta kuma yi ta kwantar da kanta cikin qirjinsa,don duk lokacin da ya mata irin haka din tssan ta taba zuciyarshi sosai,sai data saki ajiyar zuciya sannan tace
''ba shakka bawan Allah ka gama tare min komai,na tabbatar da cewa na gama samun aljannar duniya tunda Allah ya mallakamin miji kamar kai,ya bani baiwar 'ya'ya nagartattu,ya bani suruka irin mami,ya bani mahaifiya irin mama,nikam Allah ya gama min komai babu abinda ya rage gareni face inta miqa godiya ta agareshi tare da neman lahira ta kuma''kai ya jinjina yana sake jin qaunarta a ranshi,duk da ni'ima da daular da take ciki hakan bai hanata tsayawa,bautar Allah ba ka'in da na'in,hatta da abdus samad dan shekara goma sha biyu ta koya masa azumin tadawwu'i,su amatul jabbar ne kadai basa yi suma jira take sukai shekara goma goma,mace ta gari kam ya riga da ya gama mallakarta sai godiya ga madaukakin sarki
''dazun bayan fitata kai amatullah mukayi magana da abdur rahim,shikam yace mai binta mai sunan mamana yarinyar inna hadiza ta masa duk duniya so yake du Allah a bashi aurenta,adda ta taimakeshi kada ta hanashi''
''ok....abdur rahim abokin hadin bakinka ko?''dariya ya qyalqyale da ita itama ta tayashi,din duk lokacin da suka tuno da moments din a yanzu nishadi da dariya yake sasu
''kinsan kuwa sanda yana zuwa mini zance idan yazo din yadda kikasan na mutu sabida kishi,zirga zirgar da nake muku fa take hanashi sakewa maza maza yake tafiya,zaki ga yana yawan duba waya nike masa tex nace ya gaggauta tafiya hakanan fa,ke kuma kiyita jin haushi ke a lallai saurayinki abdur rahim baya dadewa yake tafiya,bakisan abdallah bane a rigar abdur rahim''
baki ta tabe cikin tsokana tace
''meye nawa?,itaku,ina cewa dazu ka siya mata ice cream ka hanamu kace mamarka ce?''
kai ya dan sosa don kada ta gansu a rana su masu dariya ya sunkuya yana daukarta bisa kafadarsa yace
''haka ne fa,mama na tafi ta kowa ai''ya juya ya fita maryam na qyalqyala musu dariya,ganin yaaran na kallonta saboda dariya da suka ha tanayi da basu san dalilinta ba yasa ta daidaita natsuwarta,ta kammala shirya abdus samad ya haura gadon da abdul ahad ke kai,ta dubi abdul ahad
''idan ka kammala addu'anka ka karanta masa shima kafin ya sake komawa baccin''
''to ummi''
gadon mami ta koma ta sake gyara mata gami da shimfida mata abun sallah don ta riga ta saba bata kwanciya sai tayi sallah raka'a biyu,har ta koyawa maryam din ma,saida mamin ta fito sannan ta shiga itama ta daura alwalar
tana bisa abun sallan mami na zaune gefan gadon tana laranta azkar da bata samu damar yi ba,wayarta na hannun abdul ahad yana danne danne,bata fiye damuwa don ya dauki wayarta ba don ta san hakin yaron indai kaga wayar a hannunshi wani abu mai mihimmanci da zai qareshi yake dubawa,Allah ya zubawa yaron tsantsar basira,hankali da nutsuwa,uwa uba ya samu ingantacciyar tarbiyya ta buga misali,ba qaramar tsaiwa maryam tayi kan tarbiyyan 'ya'yanta ba musamman abdul_ahad wanda dama danka na faro kusan shine tubalin sauran 'yan uwansa,irin tarbiyyar daka nashi to sauran ma idan ka haifesu zasu taahi ne kan aninda suka ga na gaba da su nayi wato babban yayansu,saboda ko yaushe suna tare,suna ganin irin abubuwan da yakeyi suma zasuyi qoqarin yin koyi da shi,hakann idan gurbatacciyar tarbiyya ya samu,da sun fara girma zasu bi sahunsa
Ta shafa addu'o'inta kana ta miqe ta ninke abun sallar,mami ta dubeta
''ya kamata kam ki tafi haka ki kwanta maryamu,kullum ace sai kin tayamu hira zaki tafi daki ko kwanta,banda abunki ai bani,kadai ce a dakin ba balle kice kewa zata dameni,ga mai gida na ma baiyi bacci ba''
murmushi maryam din tayi cikin kunyarta din nan da har yau bata canza ba,har yau babu wani abu da ya ragu daga qaunar da mami ke mata sai ninkuwa ma da yayi
''kije ki,kwanta maryam kinji,Allah yayi miki albarka,haqiqa har *ABADAN* bazan daina alfahari da ke ba,kin cika uwa ta gari mai fidda kyakkyawar yabanya,fata na ubangiji ya cika rayuwarku da haske farinciki da kwanciyar hankali,kin haifa min jikoki maryam hudu ne amma inaji sunfi miliyan,sabida samun yara kamarsu wallahi ba don suna jikokina ba sai an tona,Allah ya miki albarka,Allah ya miki albarka''kanta na aqasa take amsawa da amin zuciyarta cike da farinciki da qaunar mami
Wayar tata dake hannun abdul ahad ta dauki tsuwwa wanda tun tana cikin yin sallah ta ji tanayi,abdul ahad ya dubi umminsa
''ummi,abba ke kira tun dazun''yana saukowa daga gadon ya miqa mata wayar,ta riga da ta horesu,sam basa daga mata kira sai sun kawo mata ko sun sanar mata,ta daga kana ta kanga wayar a kunnenta
''please dear ki taho haka don Allah,i nedd you''murmushi ya subuce mata,kunyar mami tasa ta kana magana sai kawai ta katse kiran,minti biyu tsakani saiga tex dinshi
''gaskiya fa ina alkunya da yawa,na baki minti biyar matuqar baki taho ba da kaina zanzo har,gaban mami na sungumeki,kin sani zan iya ko?''murmushi ta sake saki taci gaba da duba agogo
sai da ta minti biyar din sun cika daidai sanan ta miqe ta yiwa mami sallam,a bakin qofar dakinsu mamin taci karo da shi dauke da amatullah,dariya ta subuce mata
''gaskiya kun samu aikinyi,ta yadda kenan zata kwana cikin 'yan uwanta''
''me ruwanki da mu?,kedai ki kuka da kanki,yau sai kin biya dukka bashin da kika ci''kai ta girgiza tana murmushi ta wucesu shi kuma ya shiga dakin
Bandaki ta fada kai tsaye bata zauna ba,sai data yi wanka mai kyau kana tazo ta mulke jikinta da turaruka masu dadi wadanda ta siyosu dazu da rana da suka fita yawin miqe qafa,dukkansu na kamfanin alharamain ne masu dadi qamshi,daya daga cikin kayan baccin data siyo ta cira,doguwar riga ce har qasa mai hannun shimi mai azabar yauqi da santsi tana da dan duhun kala kadan ta sanyata,ta feshe kanta da turaren gashi kana ta rage hasken fitilar dakin ta haura gadon ta kwanta,jin shiru bai dawo,ba ya tabbatar mata yana can ana tataburza wata qila da amatullah,kiran da ya ahigo wayarta ne ya katse mata zancan zucin da take yi,lubabatu ce da hanzarinta ta daga don tana sa ran jin daddadan labari saboda sun baro nijeria hindatun nada tsohon cikin haihuwarta ta biyu ita da hisham dinta,ai kuwa abinda ta zata dinne ta sauka dazu qn samu baby girl da take ta sha'awar haifa,don haihuwar fari namiji ne ABDULKAREEM wanda yaci sunan mahaifin abdallah
''adda na haifawa abdul_ahad mata,din gaskiya tun yau na mata miji,ina son absul_ahad adda wallahi dama yaya abdallah zai barmin shi,amma na sani bazai iya ba don ya fimu qulafucinsa''dariya maryam ta saka tana cewa
''Allah ya tabbatar,zanso haka lubabatu,Allah ya raya mana baby''
''adda sunanki taci fa,nayi alqawari dama ina fatan Allah yasa ta dauko halayenki,maryam sunanta saiki zaba mata nickname''ba qaramin farinciki maryam taji ba take tace
''mu dinga kiranta AMEERA ai yayi ko?''
''yayi adda,Allah ya qara girma,kinga mama ce a gurina(maman maryam din)ga maijidda(kulu,da yake haka suka koma ce mata) ta takuramin sai na bata ta tuna kiki tsarabar da tace tana so,kuma wai abdus samad ya cika mata alqawarin da ya daukar mata''dariya ta saki kana tace
''kice mata sunfi kusa,don abdus samad yanzu,haka,ma ya jima da yin bacci amma gobe zan kira na hadasu'',ta karba suka gaisa kana ta hadata da mama ma suka gaisa sannan sukayi sallama
Bata kai ga ajjiyewa ba kiran shamsiyya (qanwarta yar inna hadiza)ya shigo,suna gama hira zara ta kira sai bintu kamar hadin baki,dukkansu taya ta murna suke kan zuwa ta daya da abdul_ahad yayi,taji dadi sosai kan yadda kullum Allah ke dada hada kansu suka fuskanci gaskiya suka zamo tsintsiya madaurinki daya,tana cikin addu'ar bacci ne jin shirun na abdallah yayi yawa kiran hindatu ya shigo,tana kaiwa kunnenta abdallah ya shigo dakin yana sakin hannun rigar baccinsa da ada ya nannade,dariya ya bata cikin zuciyarta tana cewa hala dambe akasha kafin amatallah ta yarda
''ke kam baki duba agogo?mufa anan qarfe sha biyu na dare''
''tun dazun nake kiranki naji busy wayar taki''
''eh wallahi muna ta waya da su azara''
''lubabatu ai ta haihu,shegiyar gari,dazu naje gidan na gama yi mata tsiya ai,can na samu su shamsiyyan ma....''maryam din na shirin tambayarta tsiyan me abdallah ya wafece wayar ya kara a kunnensa
''sai da safe,a barmin gimbiya ta ta huta hakanan''ya fada,dariya hindatun tayi tace
''ranka ya dade,girman kujerarka,ai kafi gaban haka ma,Allah ya bamu alkhairi''
''ameen,ki gaida min boss(haka yake kirab jabir idan yaso tsokanarsa) da duka yaran''daga haka ya katse wayar yana jifan maryam din da wani shu'umin kallo
Bayanta ya fada kana ya janyota ya rungumeta tsam a jikinsa dukkansu suna murmushi yace
''idan na barki da wannan hindatun yauma saidai na haqura''
murmushi ta saki a boye cikin son jan tsokana
''yanzun ma haqurin zakayi,tunda jibi zamu koma so nake nayi bacci sosai don gobe wuni nakeso nayi a harami ina da addu'o'i sosai''bai bi ta maganarta ba ya fara aike mata da saqonni sannan yace
''wacce buqata kike da shi haka,tunda kika sameni ai baki da sauran matsalar rat
yuwa''murmushi ta saki kaina ta juyo suka koma fuskantar juna numfasinsu na,haduwa guri guda,fuskanta qunshe da kyakkyawan murmushin daya bayyana fararen haqoranta,kasa daurewa abdallah yayi har sai da ya shafi fuskartata yana fadin
''maryam diyana''wani murmushin ta kuma yi ta kwantar da kanta cikin qirjinsa,don duk lokacin da ya mata irin haka din tssan ta taba zuciyarshi sosai,sai data saki ajiyar zuciya sannan tace
''ba shakka bawan Allah ka gama tare min komai,na tabbatar da cewa na gama samun aljannar duniya tunda Allah ya mallakamin miji kamar kai,ya bani baiwar 'ya'ya nagartattu,ya bani suruka irin mami,ya bani mahaifiya irin mama,nikam Allah ya gama min komai babu abinda ya rage gareni face inta miqa godiya ta agareshi tare da neman lahira ta kuma''kai ya jinjina yana sake jin qaunarta a ranshi,duk da ni'ima da daular da take ciki hakan bai hanata tsayawa,bautar Allah ba ka'in da na'in,hatta da abdus samad dan shekara goma sha biyu ta koya masa azumin tadawwu'i,su amatul jabbar ne kadai basa yi suma jira take sukai shekara goma goma,mace ta gari kam ya riga da ya gama mallakarta sai godiya ga madaukakin sarki
''dazun bayan fitata kai amatullah mukayi magana da abdur rahim,shikam yace mai binta mai sunan mamana yarinyar inna hadiza ta masa duk duniya so yake du Allah a bashi aurenta,adda ta taimakeshi kada ta hanashi''
''ok....abdur rahim abokin hadin bakinka ko?''dariya ya qyalqyale da ita itama ta tayashi,din duk lokacin da suka tuno da moments din a yanzu nishadi da dariya yake sasu
''kinsan kuwa sanda yana zuwa mini zance idan yazo din yadda kikasan na mutu sabida kishi,zirga zirgar da nake muku fa take hanashi sakewa maza maza yake tafiya,zaki ga yana yawan duba waya nike masa tex nace ya gaggauta tafiya hakanan fa,ke kuma kiyita jin haushi ke a lallai saurayinki abdur rahim baya dadewa yake tafiya,bakisan abdallah bane a rigar abdur rahim''