← Book details Abadan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 103

Sashe 14

Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

''for god sake mami,ni babu wadda fa na taba cewa ina ina so duk cikinsu,yanzu mami anan kinga matar aure,kinga wadda ta cancanci zama surukarki matar danki qwaya daya abdallah,ni ban gani ba mami kuma kema na san baki gani ba''
ajiyar zuciya tayi don ta sani gaskiya abdallan ya fada
''amma wulaqancin bai da amfani abdallah,gwara arabu cikin mutunci da salama''
''mami ai bani na kawosu ba,kuma ni ba wulaqanci na musu ba,zuciya sukayi suka tafi''

murmushi tayi cikin zuciyarta,idan banda abun abdallah ai kora da hali ka musu,tace cikin zuciyarta
''tunda kace duka basu maka abida fa?,itadai nutsatstsiya ce ai ko''
yadan yatsine fuska
''ai nutsuwa kam akwaita,amma ba kamun kai,itama ina tabbatar miki mami gobe ko jibi zaki ganta da uban tana tana sum sum sum,marabarsu kadan ce ai''
''abdallah
abdallah,Allah ya shirya min kai''
''ameen mami na''

takaici ne ya rufeshi jin sallamar zubaida,ta qaraso tana wani satar kallonshi
''mami barka da dare''
''yauwa zubaida''filet ya zara ya bude warmers ya zuba abincin ya haura saman mamin abinsa
zubaidan binshi tayi da kallo yayin da ami ta dafe goshinta 🤦🏽‍♀
abdallah na bata damuwa da yawa kan yaran mutane
''ya akayi zubaida?''
maganar mamin ce ta janyo hankalinta daga kallon saman inda abdallan ya haye ya barta

''bab....ba komai mami,cewa nayi dama sai da safe''tace cikin in ina
''Allah y bamu alkhairi,ki gaida nene yau duka bamu hadu ba,insha Allahu zan shigo gobe''
''zasu ji''ta fice daga bangaren cike da takaici

a kwance ta tadda ahi saman three sityer wanda saboda tsahonsa kansa na daya hannun kujerar qafafun na daya hannun har sun zarta sosai
yasan qorafi zata yi don haka yayi saurin riga ta
''nidai,mami banji dadin dawowar nan tawa ba sam,duka yaran nan sun hanani sakewa,gaskiya daga yanzu kada wadda ta sake shigowa indai ina nan har sai na fita kawai''
''to uba na''
dariya yake ciki ciki don yasan tunda ta fadi haka ya quleta ne kuma ba zata sake cewa komai ba

🌲🎄🌲🎄🌲🎄

a fusace huwaila ta fito daga dakin nata,kai tsaye qofar dakin inna hadiza ta durfafa,a fusace ta saka hannunta ta yaye labulen tana fadin
''fito hadiza,wallahi na gaji na wannan iskancin da ake min cikin gidan nan ni da yara na''
inna hadiza dake kwance kan kujerarta da daurin qirji ta miqe ta soma qoqarin zama tare da jawo dankwalinta tana fagamniyar qulle danqararren kanta tare da fadin

''ai ni na girmewa fitowa saidai ashigo a sameni''
ba tayi wata wata na ta gado falon wanda saura ladan ta take qafar binta dake kwance saqe saqe,tayi saurin janye qafar tata tare da fadin
''Allah ya isa na wallahi''saidai bata ji ba kasancewar cikin masifa take da hayagaga

''hadiza,ki jawa diyarki
binta kunne,iskancin da take cikin gidan nan ya soma isata,haka kawai sai ta kama lubabatu ta dinga jibga,babu dama ta dauki aron wani abu nata''
''ahaf,kince haka kawai sannan kin dawo kin warware maganarki kince tana daukan aron abun ta,to ke da ita ku bude kunnuwanku da kyau,indai lubabatu bata daina daukar aron kayan binta bazan hana binta jibgarta ba,wutsiyar raqumi ai tayi nesa da qasa,mu yanzu cikin gidan nan babu sa'an mu don arziqi ba qarya bane''

kallon tara saura huwaila tayi mata,kana ta saki guda
''aikin banza....hara ra aduhu,arziqin nan fa da kike ta taqama da shi a sa hannuna ya samu,amma da yake butulu ce ke had kina da bakin goranta min,baya ga butulcin da kullum kwanan duniya kike min na hanani morar duka wani abu da jamila ta kawo cikin gidan nan,to bari kiji wallahi ki bini a hankali,don wallahi duk abinda kike taqamar da shi a yau idan naso sai na warware miki zarenki tas ta yadda baki isa ki maidashi ba''

hindatu dake parlour tana yiwa mama tsifa ta dubeta
''mama...kunnenki yana jiyo miki abinda nake ji kuwa?''
duk da cewa,zamcan ya duketa amma sai tace
''ina ruwanki hindatu?manzan Allah yace yana daga cikin kyawun musulincin mutum ya bar abinda babu ruwansa''gilma na cin hindatu amma dole haka ta ja bakinta tayi shiru tana addu'ar Allah ya kawo mata ya maryam,kai qila ma sai ta kira ta ayau din cikas din kawai mama da zata hanata

sai kuwa inna hadiza ta hauro itama huwailan dake kusa ta bi mata,sai fada ua zama hudu,binta nayi da lubabatu,huwaila nayi da hadiza ,mama ta yunqura zata fita bada haquri hindatu ta tareta tace wallahi mama babu inda zaki,lokacin da suke 'yar dadin babu wanda auka dauka abanza ieinki saboda haka yanzun ma ba ruwanki,su kashe kansu''a haka malam mamuda ua sjigo ya tadda gidan nasa

zancan ya bibiya amma daga qarshe sai ya goyawa inna hadiza baya,ko dama can itace mowar,balle yanzu da jamila ke satowa tana kawowa uwarta ita kuma take yagar masa,bayan sun shige daki ba qaramin ciwo abun ya yiwa huwaila ba,ta cizi yatsa yafi sau ashirin,lubabatu dake tsaye tana taya uwar tata takaici tace
''wallahi huwaila duk ke kika ja mana tun asali,da tuni nice kan matsayin jamila kika tsaya gina wasu kika qi gina kanki,ai da arziqi,a garin wasu gwara a garinku a garinku ma aunguwarku a unguwarma agidanku a gidanku ma adakinku''
''duk banga haka na lubabatu sai yanzu,nayi dana sani wallahi yafk a qirga,tsinanniyar mata ta kuma samun power a gida?''
''ato,shawara dai ta rage ga mai shiga rijiya,saiki zauna ki tuna bunyi''

kamar tayi mata allura ta figo mayafinta dake ajjiye saman qofar falon ta tace
''kinga zauna ki jiremin daki na,ba'a bori da sanyin jiki,bari naje gidan talatuwa''
saman tabarmar dakin ta zube tana fadin
''sai kin dawo''cikin zuciyarta tana addu'ar Allah yasa adace,tuni ta fara hango kanta a irin daular da jamila ke ciki,tana yin son ranta wanda tuni an maida jabir wani sususu,aure dai an yishi amma amma fa na cin abinci da cin kayan dadi da dibar kudi

*mrs muhammad ce👑*

📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:51 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺

▶1⃣7⃣

sama sama hadarin ke hadowa yana bajewa tun daren jiya,hakan ne ya sanya har safiyar yau garin yake da lullumi,lullube sama take da hadari mai duhu saidai sanyi sanyi yake bayarwa har yau ruwan bai kai ga sauka ba,qarfe goma ta kammala komai,wankanta tayi ta shirya cikin pskistan riga da wando daya daya daga cikin tsarabar da raliya tayi mata ta south africa,orange ne wanda aka yiwa adon dutsina dark blue daga gaban rigar da qafar wandon

mayafinshi shara shara ne amma yana da dan girma shi ta saka ta yane kanta da shi,tun baiwai yau mami ta fita saboda ta cinye hutunta na kwanaki ukun saboda haka bangaren babu kowa sai ita daya,kusan tunda tazo gidan bata fita ko ina ba saboda hala tayo sha'awar dan zagaya wa,wayarta na hannunta ta saka flat shoes ta fito

iya girma gidan yana da shi,ba ma wannan ba yanayin ginin ya burge maryam,bugu da qari yanayin da gafin yake ya qarawa maryam nishadi,lokaci gida hadarin ya yaso garin yayi duhu sosai,cikin qanqanin lokaci iska ta taso ruwa ya kece

da sauri sauri take nufar hanyar sashen nasu don bata son ruwan ya tabata,su uku me ysaye a waiting parlour din,nene zahariyya sai wani matashi da ya bawa qofa baya yana fuskantar nene,shigowar tata taji sunyi dif a maimakon sauti sautin maganar da take iya ji duk da cewa baka iya tantance abunda suke fadin,binta sukayi duka su biyun da kallo wanda hakan ya ja hankalin saurayin ya juya shima don ganin abunda suke kallon

har cikin jikinta take jin kallon nasu hade da faduwar gaba,hakanan take jin wani tsarguwa duk lokacin da suka bita da irin wannan kallon,saida ta shige sannan suka dauke idonsu
''nene,wace wannan?''ya tambayeta idonsa cikin nata cikin son jin amsa
sai da ta kuma tsuke fuskarta kafin ta amsa masa
''yar aikin da bintu ta sakewa abdullahi ce,bana buqatar kuma kace komai,idan ma wani abu kake shirin sawa zuciyarka kayi gaggawar cireshi,don wannan karon babu gudu babu ja da baya sai mun cika burin mu,a shirye nake da kawar da duk wani abu da zai kawo wa plan din mu cikas,kuma ina fatan haka ne cikin zuciyarku''

zahariyya ta tauna chewing gum dinta ya bada sautin qas qaqass
''nifa nene na fiki son cikar burin nan,sabodda haka har abunda ma ke ba zaki iya ba ni tsaf zan aikata shi''
''to balle kuma ni da nake namiji,ina da burika da dama...saidai fa...gaskiya naji yarinyar cikin jini na,tana da fitinannen kyau,any way zan ajiiyeta a side har sai bayan kammaluwar plan din mu''
''ato ya dai fi maka alkhairi''cewar nene tana buda hanci

garam taji taci karo da wani abu wanda tsabar sauri da rudewa yasa bata gane ko meye ba,ga duhu da ya mamaye falon kasan cewar duk wani qwan lantarki ta kasheshi lokacin da zata fita din
tsoro yaso kamata da tabi inuwar abun da kallo dogo ne wanda duk tsawonta ya kereta,yana kuma tsaye qiqam bai ko motsa ba
gabanta yayi mummunar faduwa,bata sake rudewa ba sai da taji muryarsa na fadin
''wannan wanne irin shshanci ne haka da hauka,kina tafiya kamar mai tabin qwaqwalwa,yanzun kuma da kinji min ciwo fa''

haushi maganar ta bata,wato ita ce ma mahaukaciyar?,shi da yake namiji baiji mata ciwo ba sai ita ce,zata ji masa?ita fa bata son rainin hankali shi ya sanya har yau bata bari su hada gu da shi,don ta fuskanci ya raina ajawalin mata saboda yaga yadda suke masa rushing

cikin dan daga murya yace
''kin wani tsaya kamar wata doluwa,ina breakfast din mu yake?''
''tun dazu na dora saman dining ai''
''ok it means ni zan sarving da kaina kenan,haka kika ga mami na na yimin''
kamar tace mishi to ai ni ba mamin ka bace,sai kuma taga bai dace ba,don tana kallonta ne tamkar mamanta
''comone dallah...dole ki dinga showing caring like my mami,babu buqatar nana ta miki aikinki,duk da cewa u can't replace my mami ko da digo daya cikin kaso dari ne,idan kuma ba zaki iya ba the door is opened''
Chapter 14 · 0% Book details