Sashe 5
Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
zubewa tayi gaban maryam tana fadin
''ya maryam don Allah me kika yiwa ya jabir?,me kika yi masa da zai miki wannan sakayyar?,me kika yi masa da har ya guje miki ya maida aurenshi kan *JAMILA*?''
dum taji kunnuwanta sunyi,qwaqwalwarta lokaci guda ta gaza yin aikinta,sai ta daina gane komai,meke shirin faruwa d ita?tambayar da taji qwaqwalwarta na mata kenan,kafin bijirowar amsar sai taji tamkar an zare dukkan wata garkuwa da ta sata ta iya tsaiwa da qafafunta,yaraf taji ta zube,daganan komai ya dauke mata dif kamar an dauke wutar nepa adaki mai tsananin duhu........
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:50 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺
▶6⃣
''ya maryam,me kika masa da har ya guje miki ya maida aurensa kan jamila?''
maganar da keta amsa kuwwa cikin kunnenta kenan bayan ta farka,sai hawaye ya fara turereniyar fitowa daga runtsatsun idanunta da ta kasa budesu suna bi ta gefan fuskarta su sauka har cikin kunnenta,wani irin yanayi take ji daban cikin zuciya da gangar jikinta
me ta aikatawa jabir da zafi haka wanda har ta cancanci wannan hukuncin?
a iya saninta ba zata iya tuna abu guda ba mara dadi da ya taba hadasu a tarihin rayuwar soyayyarsu ba
hindatu ce ta fara ankara da farkawar tata ta sanadiyyar hawayen fuskar tata dake bi ta gefen kuncinta,da sauri ta taso
''sannu ya maryam,me yake miki ciwo yanzu''
kai kawai ta gyada mata alamar babu komai
mirya can qasa tace
''dagoni hindatu''
a hankali ta taonaka mata ta tashin ta jingina da filo sannan tace bari na kira ''mama''
maman ce ta takurata kan ta tashi hindatu ta rakata asibiti,bata biqatar fita koda falon nasu ne don bata san da wanne iso zata kalli jama'a,hakanan suma batsan da wanne ido zasu dubeta ba,ta tabbatar maganar ta gama zaga unguwar ma gaba daya ba gidan ba,amma ba zata iya misa mata ba don ita don ma so take tadan gusa daga gidan saboda haka ta zura hijabinta hindatun tace bari ta nemo dan adaidaita sahu sai tayi mata magana
bayan fitar hindatun shiru dakin yayi,baka jiyo komai sai hargowa da hayaniyar jama'arsu huwaila da inna hadiza cike da farinciki,mintuna biyar sai ga hindatun ta dawo ita ta riqe maryamun suka fito yayin da 'yan uwan maman nata dake zaune jugum a rumfar tasu suke mata sannu da jaje,don tuni wasu ma soma hada kayansu don komawa inda suka fito
Sun samu ganin likita cikin qanqanin lokaci don private clinic suka je,likitan yace zai riqe ta zuwa magariba ta huta sosai tasha magungunanta,bata musa din ba suka bata gado hindatu na tare da ita
basu bar asibitin ba sai magariba,suna hanya ne hindatu tace''anty raliya ta kira ki har sau biyu kina bacci,tace zaga sake kira,ya nasir ne yayi kiranta tunda kuma ta fita bata dawo ba''
kai ta iya gyada mata kawai don bata jin zata iya bude bakinta
suna shigowa layin gabanta ya dinga dukan uku uku,ji take tamkar ta,canza wani gidan ba nasu ba,ji take kamar ta yanka a guje ta bace a nemeta a rasa,motocine a jere har zuwa qofar gidan nasu,sauka sukayi suka biya shi sannan suka dutfafi gidan wanda har qofar gida jama'a ne
duhun da garin yayi yasa babu wanda ya shaidasu har suka shige gidan wanda tun daga soron suke jiyo tashin muryoyi cike da hargowa,babu wadda tace da 'yar uwarta komai har suka shigo ainihin tsakar gidan,ga mamakinsu qofar dakinsu ne cike yake da jama'a wanda ya tabbatar musu da koma mene ya shafesu
da qyar suka kutsa cikin rumfar tasu,mamansu ce zaune bisa kujera fuskarta dauke da tashin hankali,sai anty kubra qanwar mamansu,inna hadiza da baba huwaila sai jamila dake gefansu tana zuba ruwan bala'i har daurin zaninta na kwancewa anty kubra na maida mata da raddi
baba huwaila ke riqo,jamilan ta fincike kana ta zabga mata harara
''kinga malama ki qyaleni kawai,wallahi babu inda zani sai da lefena koda motocin daukar amaryar zasu shekare,a qa'ida ai lefe nawa ne kuma sai in zuba ido a take min haqqina,wallahi babu wanda ya isa ko duk duniya gatanshi ne yau sai kun fiddo lefen nan''
''qwarai kuwa haqqinki ne ai''babarta hadiza ta fadi cike da nuna goyan baya,wani abu ne ya tsirga wa huwaila,wato tsiyar ma har da ita a ciki yau
'yan mata biyun dake tsaye bakin qofa cikin 'yan daukar amarya suka hada ido,cikin tashin hankali dayar ta cewa 'yar uwarta,muryarta can qasa''mun shiga uku malika,wacce iriyar mace ya jabir ya kwaso mana''babu mai amsar duk cikinsu,saboda haka jiki a sanyaye suka zame,suka fice daga gidan
hindatu dake jiran qiris ta saki jakar hannunta tana huci ta qaraso gaban jamila
''rufe mana baki matsiyaciyar banza matsihaciyar wofi 'yan taka hayen arziqi,lefen banza lefan wofi,mj jabir ma yanzu bai ishemu kallo ba balle abinda ya fito daga hannunsa,idan kinsa ranki a inuwa ma zamu fito muku da gayuar tsiuarku ba sai kinzo kina haushi kina ragewa kanki daraja ba idon dangin miji ba''
sai ta,hau ihu
''e hooo,munji dai duka haushin rashi ne ,kaya dai sai kun bada su''
''ai dama zamu bada din amma ba saboda wannan hayagagar taki ba,zamu baku ne saboda mu a gun mu ba yanke talauci jabir ya bamu ba,kune nake tsammanin zai iya zama yanke talauci a gunku''
hannu inna hadiza ta saka zata zabga mata mari,tuni ta tare ta kana ta sake taku uku zuwa gabanta tana huci da nuna ta da yatsa
''kada ki kuskura wallahi,don idan a baya kin saba tabani ina qyaleki ta yanzu babu wannan maganar,idan kuma kika yi gigin aiwatar da hakan wallahi ko kadan bazaji kunyarkk ba daga hannu zanyo nima in nuna miki salon nawa iya marin,tsohuwar banza wadda shekarunt basu dade ta da k.....''
tsawa mamarta ta daka mata''kada ki kuskura kici gaba,zo ki wuce ki debo musu kayansu kawai idan na isa da ke''yarfar da hannun inna hadizan tayi a fusace ta shiga dakin maman inda anan kayan ke ajjiye ta soma fiddo da su tana watsosu falon
''kada fa ta barnata muku kaya kuyi mata gana''
''ina ruwanki,da muka zo da ke wanne taimako kika iya yi,tunda dai sun fiddosu ai shikenan''inji jamilar
takaici yasa huwaila jiyawa ta bar dakin
a warwatse haka hindatu ta dinga jefomusi su tas tun mama na mata magana har ta gaji da qyaleta,bayan kuma ta gama tace wallahi ian basuyi gaggawar kwashesu daga rumfar tasu ba zasu ga qasqanci,duk iya ikancinsu sun sqn halin hindatu sqrai bata iya fushi ba,don haka cikin rawar jiki suka dinga kwashewa ciki harda uwar amarya inna hadiza
sai da suka gama sannan taji kuka yazo mata cikin dakin nasu da ta shiga da niyyar rage qincin zuciyarta,sai ta tadda maryam nayin nata,kasa lallashinta tayi hala suka hada kai suka dinga risgar kukan da qyar anty kubra ta sha kansu
haka suka kwashi amaryarsu suka kaita gidan da aka shirya shi da sunan maryam din,wanda hatta kayan gado fiye da rabi kudinta ne ta baiwa baban nata ya hada da na gurinsa aka siyesu,abu daya ne inna hadizan tasa aka jado aka dawo musu da shi kayan kitchen,duk da haka sun cire manya manyan warmers masu tsada da maryam din ta siya cikin albashinta
🎄🎄🎄🎄🎄🎄
kwana biyu gidan yayi da ragowar baqin su inna hadiza da basu ida tafiya ba,kwanakin biyun nan daidai suke da shekara goma na tsanani gurin maryam,kallo daya zaka mata ka dauke kai,hatta da mamarta wannan karon ta kasa daurewa zuciyarta sai da ta taya diyar tata kokawa
🎄🎄🎄🎄🎄🎄
ciwon kwana na hudu bayan sallar la'asar raliya ta iso gidan,maryam na kan dadduma bata kai ga tashi ba tunda tayi sallar la'asar,suna hada ido ta soma share qwalla,itama raliyan sai ta kasa daurewa duk da alqawarin da tayi ma nasir din bazata zo su hada kai suyita kuka ba
kusa da ita ta zauna suka soma aikin kuka wanda mama dake dakinta bata ji shigowarta ba sai rishin kukansu,leqowa tayi don ganin waye''ashshsha,haba raliya,abu da ya riga ya wuce kuma,don Allah ya isa haka,tashi ku shiga daki''ta fada tana karbar fadil daga gunta ta fice ta bar musu rumfar
da taimakon ambato Allah da take ta samu zuciyarta ta rage zugin da take
''raliya me n yiwa jabir haka da zafi?,wace iriuar qiyayya ce wannan ya gwada min,idan yasan tun farko baya sona me yasa bai gayamin ba tunda ba tilas aka mishi ba?''
girgiza kai kawai raliyan take
''maryam,ke kanki idan kika ga jabir sai kin tausaya masa,kallo daya zaki masa ki tabbata ba'a cikin hayyacinsa yake ba,kinsan me ya fafu ne?,lafiya suka zo gurin daurin auren amma kafin a kai ga gama taruwa ana zaune kawai su nasir suka ga jabir ya sume,mintina kadan ya dawo hayyacinsa,kinsan abinda bakinsa ya fara fada?,jamila nidai jamila nake so wallahi,zan iya rasa rayuwata idan ban mallaketa ba wallahi,abbanshi uazo yabi ba'ason maganar sai yace shi wallahi baisan wata maryam b ai tab cewa yana son wata mai suna marym ba,abbanshi ya dauka iskanci ne ya hau maa fada yace bazai maidashi mutumin banza ba,
abu kamar wasa sai ga jabir ya sake sumewa jin an hanashi jamila,da babanku yaga haka sai yace wa abban nashi ya barshi ai dake da jamilan duka daya ne''ajiyar zuciya maryam din ta ski mai tafe da hawaye,idon raliyan ciki natan tace
''maryama don Allah ki dinga saka abir a addu'o'inki,don ya hadu da jarabta,jiya nasir ya debeni muka je gidan,kinga yadda ake zaman?,yadda kika san bawa da uban gidansa,jabir ya zama abun tasayi,da jamila ta yi magan sai kiga ya zabura,tana saman kujera kwatankwacin bawa da uban gidansa''
a maimakon haushi takaici da tsanar jabir sai tausayinsa ya maye gurbi,take taji fiye da rabin quncin zuciyarta ya tafi,bata jin komai a ayanzu sai tsantsar tausayinsa,lallai ya fada cikin jarrabawa mai girma,sun dade tare da raliyan suna tattuna lamarin har daf da magariba sannan tayi musu sallama ta tafi
''ya maryam don Allah me kika yiwa ya jabir?,me kika yi masa da zai miki wannan sakayyar?,me kika yi masa da har ya guje miki ya maida aurenshi kan *JAMILA*?''
dum taji kunnuwanta sunyi,qwaqwalwarta lokaci guda ta gaza yin aikinta,sai ta daina gane komai,meke shirin faruwa d ita?tambayar da taji qwaqwalwarta na mata kenan,kafin bijirowar amsar sai taji tamkar an zare dukkan wata garkuwa da ta sata ta iya tsaiwa da qafafunta,yaraf taji ta zube,daganan komai ya dauke mata dif kamar an dauke wutar nepa adaki mai tsananin duhu........
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:50 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺
▶6⃣
''ya maryam,me kika masa da har ya guje miki ya maida aurensa kan jamila?''
maganar da keta amsa kuwwa cikin kunnenta kenan bayan ta farka,sai hawaye ya fara turereniyar fitowa daga runtsatsun idanunta da ta kasa budesu suna bi ta gefan fuskarta su sauka har cikin kunnenta,wani irin yanayi take ji daban cikin zuciya da gangar jikinta
me ta aikatawa jabir da zafi haka wanda har ta cancanci wannan hukuncin?
a iya saninta ba zata iya tuna abu guda ba mara dadi da ya taba hadasu a tarihin rayuwar soyayyarsu ba
hindatu ce ta fara ankara da farkawar tata ta sanadiyyar hawayen fuskar tata dake bi ta gefen kuncinta,da sauri ta taso
''sannu ya maryam,me yake miki ciwo yanzu''
kai kawai ta gyada mata alamar babu komai
mirya can qasa tace
''dagoni hindatu''
a hankali ta taonaka mata ta tashin ta jingina da filo sannan tace bari na kira ''mama''
maman ce ta takurata kan ta tashi hindatu ta rakata asibiti,bata biqatar fita koda falon nasu ne don bata san da wanne iso zata kalli jama'a,hakanan suma batsan da wanne ido zasu dubeta ba,ta tabbatar maganar ta gama zaga unguwar ma gaba daya ba gidan ba,amma ba zata iya misa mata ba don ita don ma so take tadan gusa daga gidan saboda haka ta zura hijabinta hindatun tace bari ta nemo dan adaidaita sahu sai tayi mata magana
bayan fitar hindatun shiru dakin yayi,baka jiyo komai sai hargowa da hayaniyar jama'arsu huwaila da inna hadiza cike da farinciki,mintuna biyar sai ga hindatun ta dawo ita ta riqe maryamun suka fito yayin da 'yan uwan maman nata dake zaune jugum a rumfar tasu suke mata sannu da jaje,don tuni wasu ma soma hada kayansu don komawa inda suka fito
Sun samu ganin likita cikin qanqanin lokaci don private clinic suka je,likitan yace zai riqe ta zuwa magariba ta huta sosai tasha magungunanta,bata musa din ba suka bata gado hindatu na tare da ita
basu bar asibitin ba sai magariba,suna hanya ne hindatu tace''anty raliya ta kira ki har sau biyu kina bacci,tace zaga sake kira,ya nasir ne yayi kiranta tunda kuma ta fita bata dawo ba''
kai ta iya gyada mata kawai don bata jin zata iya bude bakinta
suna shigowa layin gabanta ya dinga dukan uku uku,ji take tamkar ta,canza wani gidan ba nasu ba,ji take kamar ta yanka a guje ta bace a nemeta a rasa,motocine a jere har zuwa qofar gidan nasu,sauka sukayi suka biya shi sannan suka dutfafi gidan wanda har qofar gida jama'a ne
duhun da garin yayi yasa babu wanda ya shaidasu har suka shige gidan wanda tun daga soron suke jiyo tashin muryoyi cike da hargowa,babu wadda tace da 'yar uwarta komai har suka shigo ainihin tsakar gidan,ga mamakinsu qofar dakinsu ne cike yake da jama'a wanda ya tabbatar musu da koma mene ya shafesu
da qyar suka kutsa cikin rumfar tasu,mamansu ce zaune bisa kujera fuskarta dauke da tashin hankali,sai anty kubra qanwar mamansu,inna hadiza da baba huwaila sai jamila dake gefansu tana zuba ruwan bala'i har daurin zaninta na kwancewa anty kubra na maida mata da raddi
baba huwaila ke riqo,jamilan ta fincike kana ta zabga mata harara
''kinga malama ki qyaleni kawai,wallahi babu inda zani sai da lefena koda motocin daukar amaryar zasu shekare,a qa'ida ai lefe nawa ne kuma sai in zuba ido a take min haqqina,wallahi babu wanda ya isa ko duk duniya gatanshi ne yau sai kun fiddo lefen nan''
''qwarai kuwa haqqinki ne ai''babarta hadiza ta fadi cike da nuna goyan baya,wani abu ne ya tsirga wa huwaila,wato tsiyar ma har da ita a ciki yau
'yan mata biyun dake tsaye bakin qofa cikin 'yan daukar amarya suka hada ido,cikin tashin hankali dayar ta cewa 'yar uwarta,muryarta can qasa''mun shiga uku malika,wacce iriyar mace ya jabir ya kwaso mana''babu mai amsar duk cikinsu,saboda haka jiki a sanyaye suka zame,suka fice daga gidan
hindatu dake jiran qiris ta saki jakar hannunta tana huci ta qaraso gaban jamila
''rufe mana baki matsiyaciyar banza matsihaciyar wofi 'yan taka hayen arziqi,lefen banza lefan wofi,mj jabir ma yanzu bai ishemu kallo ba balle abinda ya fito daga hannunsa,idan kinsa ranki a inuwa ma zamu fito muku da gayuar tsiuarku ba sai kinzo kina haushi kina ragewa kanki daraja ba idon dangin miji ba''
sai ta,hau ihu
''e hooo,munji dai duka haushin rashi ne ,kaya dai sai kun bada su''
''ai dama zamu bada din amma ba saboda wannan hayagagar taki ba,zamu baku ne saboda mu a gun mu ba yanke talauci jabir ya bamu ba,kune nake tsammanin zai iya zama yanke talauci a gunku''
hannu inna hadiza ta saka zata zabga mata mari,tuni ta tare ta kana ta sake taku uku zuwa gabanta tana huci da nuna ta da yatsa
''kada ki kuskura wallahi,don idan a baya kin saba tabani ina qyaleki ta yanzu babu wannan maganar,idan kuma kika yi gigin aiwatar da hakan wallahi ko kadan bazaji kunyarkk ba daga hannu zanyo nima in nuna miki salon nawa iya marin,tsohuwar banza wadda shekarunt basu dade ta da k.....''
tsawa mamarta ta daka mata''kada ki kuskura kici gaba,zo ki wuce ki debo musu kayansu kawai idan na isa da ke''yarfar da hannun inna hadizan tayi a fusace ta shiga dakin maman inda anan kayan ke ajjiye ta soma fiddo da su tana watsosu falon
''kada fa ta barnata muku kaya kuyi mata gana''
''ina ruwanki,da muka zo da ke wanne taimako kika iya yi,tunda dai sun fiddosu ai shikenan''inji jamilar
takaici yasa huwaila jiyawa ta bar dakin
a warwatse haka hindatu ta dinga jefomusi su tas tun mama na mata magana har ta gaji da qyaleta,bayan kuma ta gama tace wallahi ian basuyi gaggawar kwashesu daga rumfar tasu ba zasu ga qasqanci,duk iya ikancinsu sun sqn halin hindatu sqrai bata iya fushi ba,don haka cikin rawar jiki suka dinga kwashewa ciki harda uwar amarya inna hadiza
sai da suka gama sannan taji kuka yazo mata cikin dakin nasu da ta shiga da niyyar rage qincin zuciyarta,sai ta tadda maryam nayin nata,kasa lallashinta tayi hala suka hada kai suka dinga risgar kukan da qyar anty kubra ta sha kansu
haka suka kwashi amaryarsu suka kaita gidan da aka shirya shi da sunan maryam din,wanda hatta kayan gado fiye da rabi kudinta ne ta baiwa baban nata ya hada da na gurinsa aka siyesu,abu daya ne inna hadizan tasa aka jado aka dawo musu da shi kayan kitchen,duk da haka sun cire manya manyan warmers masu tsada da maryam din ta siya cikin albashinta
🎄🎄🎄🎄🎄🎄
kwana biyu gidan yayi da ragowar baqin su inna hadiza da basu ida tafiya ba,kwanakin biyun nan daidai suke da shekara goma na tsanani gurin maryam,kallo daya zaka mata ka dauke kai,hatta da mamarta wannan karon ta kasa daurewa zuciyarta sai da ta taya diyar tata kokawa
🎄🎄🎄🎄🎄🎄
ciwon kwana na hudu bayan sallar la'asar raliya ta iso gidan,maryam na kan dadduma bata kai ga tashi ba tunda tayi sallar la'asar,suna hada ido ta soma share qwalla,itama raliyan sai ta kasa daurewa duk da alqawarin da tayi ma nasir din bazata zo su hada kai suyita kuka ba
kusa da ita ta zauna suka soma aikin kuka wanda mama dake dakinta bata ji shigowarta ba sai rishin kukansu,leqowa tayi don ganin waye''ashshsha,haba raliya,abu da ya riga ya wuce kuma,don Allah ya isa haka,tashi ku shiga daki''ta fada tana karbar fadil daga gunta ta fice ta bar musu rumfar
da taimakon ambato Allah da take ta samu zuciyarta ta rage zugin da take
''raliya me n yiwa jabir haka da zafi?,wace iriuar qiyayya ce wannan ya gwada min,idan yasan tun farko baya sona me yasa bai gayamin ba tunda ba tilas aka mishi ba?''
girgiza kai kawai raliyan take
''maryam,ke kanki idan kika ga jabir sai kin tausaya masa,kallo daya zaki masa ki tabbata ba'a cikin hayyacinsa yake ba,kinsan me ya fafu ne?,lafiya suka zo gurin daurin auren amma kafin a kai ga gama taruwa ana zaune kawai su nasir suka ga jabir ya sume,mintina kadan ya dawo hayyacinsa,kinsan abinda bakinsa ya fara fada?,jamila nidai jamila nake so wallahi,zan iya rasa rayuwata idan ban mallaketa ba wallahi,abbanshi uazo yabi ba'ason maganar sai yace shi wallahi baisan wata maryam b ai tab cewa yana son wata mai suna marym ba,abbanshi ya dauka iskanci ne ya hau maa fada yace bazai maidashi mutumin banza ba,
abu kamar wasa sai ga jabir ya sake sumewa jin an hanashi jamila,da babanku yaga haka sai yace wa abban nashi ya barshi ai dake da jamilan duka daya ne''ajiyar zuciya maryam din ta ski mai tafe da hawaye,idon raliyan ciki natan tace
''maryama don Allah ki dinga saka abir a addu'o'inki,don ya hadu da jarabta,jiya nasir ya debeni muka je gidan,kinga yadda ake zaman?,yadda kika san bawa da uban gidansa,jabir ya zama abun tasayi,da jamila ta yi magan sai kiga ya zabura,tana saman kujera kwatankwacin bawa da uban gidansa''
a maimakon haushi takaici da tsanar jabir sai tausayinsa ya maye gurbi,take taji fiye da rabin quncin zuciyarta ya tafi,bata jin komai a ayanzu sai tsantsar tausayinsa,lallai ya fada cikin jarrabawa mai girma,sun dade tare da raliyan suna tattuna lamarin har daf da magariba sannan tayi musu sallama ta tafi