Sashe 71
Abadan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
''au kema zubaida haka zakiyi min,ashe dukkanku matsiyata ne,yayana na cikina babu mai tausayi na kune masu rusani?'''tsayawa tayi cak tana kallonta
''tab lallai ma nene,ke don Allah baki ji kunyar kanki ba?adnan ma yayi miki haka ballanta na ni?''
''yanzu don adnan ya yimin haka kema sai ki biye masa?''
''hmmm,sai kuma kiyi,ina ga kin dade baki bata yawun bakinki ba,ai tunda kika ahiga tsakani na da abdallah kika min asirin da aka ciren sonsa to wlh babu ni babu aure,rayuwar bariki ta fiyemin inda zan zuba jarin jikina na samu kudi''tana fadan haka tana sabule da lalube duk wani abu da yayi saura wanda adnan bai kai ga daukewa ba,cikin haka tayi katari da takardar wani gida ta dauke abinta,tana jin nenen na qwala mata kira har ta koma rsine mata itama amma kallon arziqi bata iaheta ba tayi gaba abinta,don ta riga ta sani uwar tasu ba imani gareta don me ita zataji tausayinta kuma?,ai raba arne da makami ibada ne
A ranar bata bari ta kwanan ba ta hada ya nata ya nata ta nufi gidan wata aminiyarta da ta jima tana mata hudubar shaidan kan cewa ta mori kyanta wlh ta qyale wani abdallah ta tsaya ta nace masa yana wulaqantata bayan ga samari nan da alhazawa na sonta ido rufe
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Duka hidimar ranar ita ta karbeta don inna wuro da abdallah na gurin tsoho alhaji wanda ya sauka qasa nijeria da misalin sha biyu na rana,tayi mamakin ganin hisham shima ya iso a ranar
''ina sane da ranar dawowar tsoho alhaji a lissafe nake maryam,abdallah na raina da shi nake kwana da shi nake tashi ko yaushe''qwarai ta gasgata hakan tunda gashi taga zahiri
Gidan kusan a cike yake da yan sannu da zuwa wanda basu samu sararawar mutanen ba sai bayan sallar la'asar
Tsoho alhaji wanda asalin sunanshi muhammdu dattijo ne mai cikar kamala da nutsuwa,dattijo ne da ya amsa sunan dattijo bawai muna dattijo ba,dattijo ne da kallo daya zaka masa kwarjininsa ya cika maka idanu,yadda matarsa inna wuro(fatima)ke da kirki haka shima yake
Murmushi ya saki har ya dan fidda sauti bayan ya kammal jin dukkan wasu bayanai daga bakin maryam da abdallah hisham harma da inna wuro daga dan abinda ta sani
''in sha Allahu da izinin Allah indai sammun ne bi'iznillah na bada gaskiya ga Allag nan da kwanki bakwai zaka miqe abdullahi ka taka qafafunka komai yazo qarshe,zan yabaki miki maryam kinyi namijin qoqari qwarai da gaske tunda wuro ta gayamin ba haka kuka zo ba,kamar yadda naji bayanai daga bakinki,na abubuwan da kika dinga nasa amfani da su,ayoyo yine masu kyau matuqa da gaske,gakanna masu tasiri qwarai da gaske wajen ruguza sihiri ko wanne iri ne bi'iznillahi ta'ala,yanzu akwai wasu magunguna da saiwayoyi da Allah ya horemin saninsu,yau basai gobe ba zan fara hadasu guri guda insha Allahu baka wuce kwana bakwai ka warke abdullahi kaci gaba da haquri wannan wata jarrabawa ce Allah ya maka don ya gani shin zaka gode masa ne ko zaka butulce masa?,a baya ya maka duk wata ni'ima ta dukiya kyau ilimi nasaba da gata a yanzu ya amshe abinsa yayi ne duka don ya jarabci imaninka,to alhamdulillah bisa dukkan alamu ka karbi duk wata jarrabawa daga gareshi kuma ina maka kyakkyawan fatan samun cikakken lada''
cike da girmamawa ya duqar da kansa
''na gode qwarai da gaske alhaji,Allah ya qara girma,Allah ya qara lafiya da nisan kwana mai amfani''
haka hisham da maryam suka bi sahun tayashi godiya ga dattijon
Ya dubi inna wuro
''muje ki tayani duba kayan nan,don na san yanzu kin canza musu guri''bata ce komai ba ta miqe tabi bayansa
hannun hisham abdallah ya kama ya riqe
''ka taya ni murna abokina na kusa angwancewa''
dan satar kallon maryam yayi
''mtswee,har yau abdallah baka da kunya,ni kake wa irin wannan maganar?''
ya dubeshi a hagunce
''to akan me bazan maka ba?,rashin aure fa nasifa ne abokina ban sani ba sai yanzu''cikin rashin fahimta yake dubanshi
''like how,kana da mata kana kiran rashin aure a kanka?''
''neman wani auren nake cikin garin nan hisham na wata 'yar fulani''
wani irin kallo hisham din yake masa
''kanka daya kuwa abdallah?,kana da mata kake cewa wani auren kake nema?''
''tunda anqi ka meye na cusa kai hisham don Allah fa,matar tace bata yi zaka mata dole ne?''ya fada qwayar idanunshi na sauya kala,da alamu abinda yake fada din na taba zuciyarshi
''kuma a shekaru na bazan iya zama babu mace ba,kai ka sani da din ma rakawa kawai akeyi''
duk da maganar ta taba hisham yaji wani iri amma maganar abdallahn ta qarshe taso bashi dariya kafin yace komai mero ta kwada sallama bakin qofar dakin wanda duka wunin yau bata shigo gidan ba sai yanzu
''yauwa shigo ga abokina zaku gaisa''inji abdallah yana duban hisham din
jin haka yasa ta dago labulan ta shigo kanta a qas alamun kunya,gefe ta rabe ta gaidasu su duka banda maryam da da qyar ta iya amsaqa can qasab maqoshi,kasa sakewa meron tayi ta miqe zata fita abdallan ya tambayeta ina zuwa tace zata yiwa tsoho alhaji ne barka da dawowa
''idan kin masan ki dawo ina son ganinki''inji shi ta gyada kana ta fice hisham ya bita da kallo,sai da ta fice din baki daya kana ya dawo da kallonsa kan abdallah
''wannan kuma wace ce,yar fillo haka''murmushi ya saka irin mai hade nishadin nan yace
''daina saurin yabawa,itace wadda nake gaya maka ina neman aurenta a qauyen nan''
Wata guduma maryam taji ta sauka kan qirjinya,kanta da gangar jikinta sukayi mata nauyi gaba daya,a hankali ta soma fusgar numfashinya yana son qwace mata,sai ta miqe sama sama tana jiyo sa in sarsu shi da hisham,ganin tana niyyar fita ya sanya hisham kiranta,shi din ma sama sama take jin muryarshi don haka bata bi ta kansa ba ta lalubi hanya ta fice,ba kowa tsakar gidan kai tsaye dakin inna wuro ta shige,gadonta irin na qauye ne da ake kira gadon bunu mai rumfar shi ta haye,can qurya ta takure kanta tana jin wani abu na mata yawo cikin zuciyarta kuka take so tayi ko zata ji sanyi cikin zuciyarta,shin wannan shine kishin?,da gaske kishin abdallah take?sune tambayoyin data ringa jefawa kanta ta kuma takurawa kan nata sai ta fidda amsarsu
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶5⃣3⃣
*_Daga Abu hurairah Allah ya qara ya yarda shi yace:Manzan Allah S A W bai taba aibata wani abinci ba ko kadan,idan ya burgeshi(abincin)sai yaci,idan bai masa(bai kwanta masa ba ko ba cimarsa bace)sai ya barshi (ba tare da ya aibata shi ba ko ya wulaqanta shi ba)_*
*ina kuke 'yan*
*huguma conversation and novels room*
*maman aysha hausa novels group*
*haske writers asso*
*DA*
*Z.B.I*
*_bazan gaji da sadaukar muku da shafuka na ba,ina yabawa qwarai da qaunarku gareni,ina roqon Allah ya tashe mu qarqashin inuwarsa ranar gobe qiyama,ya bar mu tare bisa soyayya ta domin Allah_*🙏🏽🙏🏽
Sake lafewa tayi kan gadon inna wuron tana matse idanunta don fidda hawayen dake maqale cikinsu
tun tana jiyo maganganun mutane masu ahigowa jifa jifa yiwa tsoho alhaji barka da dawowa har jin nata ya dayke baki daya,wani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita
********
Qaton fili ne dake malale da koiyar ciyawa wadda ake kira da grass carfet jifa jifa kuma jajayen furanni ne ke dashe ta tsakanin ciyawar
Iska mai dadi ke kada fingilar rigar dake jikinta wadda bata da nauyi ko kadan sai santsi,kamar yadda gashin kanta keta yawo tsakanin kafadarta da fuskarta,dauke take da faranti fari qal wanda akanshi kofuna ne fuda uku da jug tsakiyarsa wanda cike yake da madarar shanu,a hankaki take tafiya yana daga nesa cikin fararen kaya hannayensa harde a qirjinsa,dukkan wani hankali nashi da tunaninshi yana a akanta ne,kyakkyawan murmushinsa kadai ya sata mance a ina rake har ta qaraso gareshi,hannu yasa ya karbe farantin ya ajjiye a tsakiyarsu kana ya riqo hannunta
''maryama''
''na'am''ta amsa masa kanta a qasa
''maryam ki kalleni tun kafin na zauce''
ya fada qasa qasa yadda dagashi sai ita kadai zasu iya jin abinda yake fada,babu musu ta daga kanta idanunsu suka mannu da juna,kallon juna suka shiga yi babu qaqqautawa tamkar zasu hadiye junansu,kowanne na ganin zallar qauna qarar cikin idanun dan uwanshi
Shi yafara bude bakinsa
''maryam,kinsan yadda nakeji game da ke cikin zuciyata kuwa''ya fada yana tura hannunta cikin qirjinsa bayan ya balle maballan rigarsa,take tafin hannunta ya mannu da fatar qirjinsa dake cike da gashi
''kina iya jiyo bugun zuciyata a haka?''kai ta gyada masa tana murmushi don tana jin yadda zuciyar tasa kera fat fat fat da sauri
kai ya girgiza
''abinda kika ji yanzu baikai kaso daya cikin dari na yadda nakeji cikin zuciyata game da ke ba,idan da zan iya zuciyar zan ciro miki dungurun gun na ajjiye miki ita wata qila kya iya ganin kaso hamasin cikin darin abinda nake gaya miki,ragowar hamsin din sai ni da Allah''
qayataccen murmushi ta sakar masa tana sadda kanta qasa,da sauri yace
''dago ki kalleni da kyau maryamu na,kallon da kike min kawai na rage radadin da nake ji''bata musa din ba ta dago taci gaba da kallon nashi fuskarta dauke da murmushi
ya matso kusa da ita har suna gwaren numfashi
''i love d look in ur eyes maryam''murmushi ta kuma yi tana dan kawar da idanunta
''i luv ur smile,maryam ke ta musamman ce u make me feel safe nd secure,ban damu da duk wani abu da na rasa ba idan ka cire mami na matuqar ina tare da ke,i know u luv me 4 who am,pls maryam tell me kina sona...kina son abdallah''
idanunta ta lumshe kana ta bude tattausan labbanta
''abdallah''
''yes ina jinki''
''abdallah ina.....''
''umh comeon baby ina jinki''
''abdallah''
''na'ammmm''
sai taji amsawar ta qarahe tamkar ido biyu ne ba cikin mafarki ba,a hankali ta fara bude idanunta don tantance a inda take,yana zaune sosai kan kekenshi idanunsa akanta kamar wanda ya samu hoto,a firgice ta miqe ta zauna dirshan kan gadon innna wuron tana mutstsuka idanu
''tab lallai ma nene,ke don Allah baki ji kunyar kanki ba?adnan ma yayi miki haka ballanta na ni?''
''yanzu don adnan ya yimin haka kema sai ki biye masa?''
''hmmm,sai kuma kiyi,ina ga kin dade baki bata yawun bakinki ba,ai tunda kika ahiga tsakani na da abdallah kika min asirin da aka ciren sonsa to wlh babu ni babu aure,rayuwar bariki ta fiyemin inda zan zuba jarin jikina na samu kudi''tana fadan haka tana sabule da lalube duk wani abu da yayi saura wanda adnan bai kai ga daukewa ba,cikin haka tayi katari da takardar wani gida ta dauke abinta,tana jin nenen na qwala mata kira har ta koma rsine mata itama amma kallon arziqi bata iaheta ba tayi gaba abinta,don ta riga ta sani uwar tasu ba imani gareta don me ita zataji tausayinta kuma?,ai raba arne da makami ibada ne
A ranar bata bari ta kwanan ba ta hada ya nata ya nata ta nufi gidan wata aminiyarta da ta jima tana mata hudubar shaidan kan cewa ta mori kyanta wlh ta qyale wani abdallah ta tsaya ta nace masa yana wulaqantata bayan ga samari nan da alhazawa na sonta ido rufe
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Duka hidimar ranar ita ta karbeta don inna wuro da abdallah na gurin tsoho alhaji wanda ya sauka qasa nijeria da misalin sha biyu na rana,tayi mamakin ganin hisham shima ya iso a ranar
''ina sane da ranar dawowar tsoho alhaji a lissafe nake maryam,abdallah na raina da shi nake kwana da shi nake tashi ko yaushe''qwarai ta gasgata hakan tunda gashi taga zahiri
Gidan kusan a cike yake da yan sannu da zuwa wanda basu samu sararawar mutanen ba sai bayan sallar la'asar
Tsoho alhaji wanda asalin sunanshi muhammdu dattijo ne mai cikar kamala da nutsuwa,dattijo ne da ya amsa sunan dattijo bawai muna dattijo ba,dattijo ne da kallo daya zaka masa kwarjininsa ya cika maka idanu,yadda matarsa inna wuro(fatima)ke da kirki haka shima yake
Murmushi ya saki har ya dan fidda sauti bayan ya kammal jin dukkan wasu bayanai daga bakin maryam da abdallah hisham harma da inna wuro daga dan abinda ta sani
''in sha Allahu da izinin Allah indai sammun ne bi'iznillah na bada gaskiya ga Allag nan da kwanki bakwai zaka miqe abdullahi ka taka qafafunka komai yazo qarshe,zan yabaki miki maryam kinyi namijin qoqari qwarai da gaske tunda wuro ta gayamin ba haka kuka zo ba,kamar yadda naji bayanai daga bakinki,na abubuwan da kika dinga nasa amfani da su,ayoyo yine masu kyau matuqa da gaske,gakanna masu tasiri qwarai da gaske wajen ruguza sihiri ko wanne iri ne bi'iznillahi ta'ala,yanzu akwai wasu magunguna da saiwayoyi da Allah ya horemin saninsu,yau basai gobe ba zan fara hadasu guri guda insha Allahu baka wuce kwana bakwai ka warke abdullahi kaci gaba da haquri wannan wata jarrabawa ce Allah ya maka don ya gani shin zaka gode masa ne ko zaka butulce masa?,a baya ya maka duk wata ni'ima ta dukiya kyau ilimi nasaba da gata a yanzu ya amshe abinsa yayi ne duka don ya jarabci imaninka,to alhamdulillah bisa dukkan alamu ka karbi duk wata jarrabawa daga gareshi kuma ina maka kyakkyawan fatan samun cikakken lada''
cike da girmamawa ya duqar da kansa
''na gode qwarai da gaske alhaji,Allah ya qara girma,Allah ya qara lafiya da nisan kwana mai amfani''
haka hisham da maryam suka bi sahun tayashi godiya ga dattijon
Ya dubi inna wuro
''muje ki tayani duba kayan nan,don na san yanzu kin canza musu guri''bata ce komai ba ta miqe tabi bayansa
hannun hisham abdallah ya kama ya riqe
''ka taya ni murna abokina na kusa angwancewa''
dan satar kallon maryam yayi
''mtswee,har yau abdallah baka da kunya,ni kake wa irin wannan maganar?''
ya dubeshi a hagunce
''to akan me bazan maka ba?,rashin aure fa nasifa ne abokina ban sani ba sai yanzu''cikin rashin fahimta yake dubanshi
''like how,kana da mata kana kiran rashin aure a kanka?''
''neman wani auren nake cikin garin nan hisham na wata 'yar fulani''
wani irin kallo hisham din yake masa
''kanka daya kuwa abdallah?,kana da mata kake cewa wani auren kake nema?''
''tunda anqi ka meye na cusa kai hisham don Allah fa,matar tace bata yi zaka mata dole ne?''ya fada qwayar idanunshi na sauya kala,da alamu abinda yake fada din na taba zuciyarshi
''kuma a shekaru na bazan iya zama babu mace ba,kai ka sani da din ma rakawa kawai akeyi''
duk da maganar ta taba hisham yaji wani iri amma maganar abdallahn ta qarshe taso bashi dariya kafin yace komai mero ta kwada sallama bakin qofar dakin wanda duka wunin yau bata shigo gidan ba sai yanzu
''yauwa shigo ga abokina zaku gaisa''inji abdallah yana duban hisham din
jin haka yasa ta dago labulan ta shigo kanta a qas alamun kunya,gefe ta rabe ta gaidasu su duka banda maryam da da qyar ta iya amsaqa can qasab maqoshi,kasa sakewa meron tayi ta miqe zata fita abdallan ya tambayeta ina zuwa tace zata yiwa tsoho alhaji ne barka da dawowa
''idan kin masan ki dawo ina son ganinki''inji shi ta gyada kana ta fice hisham ya bita da kallo,sai da ta fice din baki daya kana ya dawo da kallonsa kan abdallah
''wannan kuma wace ce,yar fillo haka''murmushi ya saka irin mai hade nishadin nan yace
''daina saurin yabawa,itace wadda nake gaya maka ina neman aurenta a qauyen nan''
Wata guduma maryam taji ta sauka kan qirjinya,kanta da gangar jikinta sukayi mata nauyi gaba daya,a hankali ta soma fusgar numfashinya yana son qwace mata,sai ta miqe sama sama tana jiyo sa in sarsu shi da hisham,ganin tana niyyar fita ya sanya hisham kiranta,shi din ma sama sama take jin muryarshi don haka bata bi ta kansa ba ta lalubi hanya ta fice,ba kowa tsakar gidan kai tsaye dakin inna wuro ta shige,gadonta irin na qauye ne da ake kira gadon bunu mai rumfar shi ta haye,can qurya ta takure kanta tana jin wani abu na mata yawo cikin zuciyarta kuka take so tayi ko zata ji sanyi cikin zuciyarta,shin wannan shine kishin?,da gaske kishin abdallah take?sune tambayoyin data ringa jefawa kanta ta kuma takurawa kan nata sai ta fidda amsarsu
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶5⃣3⃣
*_Daga Abu hurairah Allah ya qara ya yarda shi yace:Manzan Allah S A W bai taba aibata wani abinci ba ko kadan,idan ya burgeshi(abincin)sai yaci,idan bai masa(bai kwanta masa ba ko ba cimarsa bace)sai ya barshi (ba tare da ya aibata shi ba ko ya wulaqanta shi ba)_*
*ina kuke 'yan*
*huguma conversation and novels room*
*maman aysha hausa novels group*
*haske writers asso*
*DA*
*Z.B.I*
*_bazan gaji da sadaukar muku da shafuka na ba,ina yabawa qwarai da qaunarku gareni,ina roqon Allah ya tashe mu qarqashin inuwarsa ranar gobe qiyama,ya bar mu tare bisa soyayya ta domin Allah_*🙏🏽🙏🏽
Sake lafewa tayi kan gadon inna wuron tana matse idanunta don fidda hawayen dake maqale cikinsu
tun tana jiyo maganganun mutane masu ahigowa jifa jifa yiwa tsoho alhaji barka da dawowa har jin nata ya dayke baki daya,wani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita
********
Qaton fili ne dake malale da koiyar ciyawa wadda ake kira da grass carfet jifa jifa kuma jajayen furanni ne ke dashe ta tsakanin ciyawar
Iska mai dadi ke kada fingilar rigar dake jikinta wadda bata da nauyi ko kadan sai santsi,kamar yadda gashin kanta keta yawo tsakanin kafadarta da fuskarta,dauke take da faranti fari qal wanda akanshi kofuna ne fuda uku da jug tsakiyarsa wanda cike yake da madarar shanu,a hankaki take tafiya yana daga nesa cikin fararen kaya hannayensa harde a qirjinsa,dukkan wani hankali nashi da tunaninshi yana a akanta ne,kyakkyawan murmushinsa kadai ya sata mance a ina rake har ta qaraso gareshi,hannu yasa ya karbe farantin ya ajjiye a tsakiyarsu kana ya riqo hannunta
''maryama''
''na'am''ta amsa masa kanta a qasa
''maryam ki kalleni tun kafin na zauce''
ya fada qasa qasa yadda dagashi sai ita kadai zasu iya jin abinda yake fada,babu musu ta daga kanta idanunsu suka mannu da juna,kallon juna suka shiga yi babu qaqqautawa tamkar zasu hadiye junansu,kowanne na ganin zallar qauna qarar cikin idanun dan uwanshi
Shi yafara bude bakinsa
''maryam,kinsan yadda nakeji game da ke cikin zuciyata kuwa''ya fada yana tura hannunta cikin qirjinsa bayan ya balle maballan rigarsa,take tafin hannunta ya mannu da fatar qirjinsa dake cike da gashi
''kina iya jiyo bugun zuciyata a haka?''kai ta gyada masa tana murmushi don tana jin yadda zuciyar tasa kera fat fat fat da sauri
kai ya girgiza
''abinda kika ji yanzu baikai kaso daya cikin dari na yadda nakeji cikin zuciyata game da ke ba,idan da zan iya zuciyar zan ciro miki dungurun gun na ajjiye miki ita wata qila kya iya ganin kaso hamasin cikin darin abinda nake gaya miki,ragowar hamsin din sai ni da Allah''
qayataccen murmushi ta sakar masa tana sadda kanta qasa,da sauri yace
''dago ki kalleni da kyau maryamu na,kallon da kike min kawai na rage radadin da nake ji''bata musa din ba ta dago taci gaba da kallon nashi fuskarta dauke da murmushi
ya matso kusa da ita har suna gwaren numfashi
''i love d look in ur eyes maryam''murmushi ta kuma yi tana dan kawar da idanunta
''i luv ur smile,maryam ke ta musamman ce u make me feel safe nd secure,ban damu da duk wani abu da na rasa ba idan ka cire mami na matuqar ina tare da ke,i know u luv me 4 who am,pls maryam tell me kina sona...kina son abdallah''
idanunta ta lumshe kana ta bude tattausan labbanta
''abdallah''
''yes ina jinki''
''abdallah ina.....''
''umh comeon baby ina jinki''
''abdallah''
''na'ammmm''
sai taji amsawar ta qarahe tamkar ido biyu ne ba cikin mafarki ba,a hankali ta fara bude idanunta don tantance a inda take,yana zaune sosai kan kekenshi idanunsa akanta kamar wanda ya samu hoto,a firgice ta miqe ta zauna dirshan kan gadon innna wuron tana mutstsuka idanu