Sashe 30
Yar Zaman Wanka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Saura sati biyu ne ashe ba yau bane dan haka ki rufe idanunki sai kin daÉ—e sannan za ki buÉ—e" Ya katse wa Inna zancen zucin ta.
"Allah na gode maka ai har na bayar sa wasiyya in nemi yafiyar jama'a" Cewar Inna a zuciyarta.
"Kuma ba a baiwa kowa labari ki ja bakin ki ki yi shiru".
"Bakina ƙanin ƙafata" Cewar Inna cikin rawar murya.
Ai Inna da ta rufe idanunta gam, ko alamar ɗagawa bata yi ba, har Imran ya lallaɓa ya tsugunna ya fice daga ɗakin da rarrafe amma Inna ko fitarsa bata ji ba. Har lokacin gabanta bai daina faɗuwa ba jikinta kuma bai bar karkarwa ba, sai da ta kwashe tsawon awa guda sannan ta miƙa hannunta na dama ta taɓo hancinta jin iska na fita daga hancin ta tabbatar bata mutu ba a hankali ta shiga buɗe idanunta cike da tsoro tana so ta tashi Sadiya ta faɗa mata sai dai tana tsoro kuma an ce kar ta faɗawa kowa.
*IMRAN*
Tun da ya fito daga ɗakin ya dawo falo ya cire kayan ya maida wanda ya cire ya sanya su a ledarsu ya mayar ƙasan kujera ya ajiye yana so da asuba sai ya fice da su in zashi masallaci. Tun da ya kwanta yake ta dariya ƙasa-ƙasa ba abin da je bashi dariya irin yadda idanun Inna suka yi ƙulu-ƙulu ita ala dole za ta mutu, ga karkarwar da jikinta ke yi kamar mazari shi kaɗai ya isa ya sanya cikinka ya yi ciwo saboda dariya.
"Ko a ina ta taɓa jin mala'ikan mutuwa yana manta wa'adin mutum har ya zo ɗaukan ran mutum amma kuma ya fasa ya ce sai wani lokacin, har ya faɗa maka lokacin ka.
"Kai ruɗani bai yi ba wallahi" Ya faɗa yana ƙyalƙyala dariya a ɓoye.
Tun da ta buɗe idon nata ta ji wani fitsari ya cika mata mara, ga tsoro da fargaba duk sun tarar mata sai kuma karkarwar da take. Jin fitsarin na neman zubowa ta ƙoƙarta ta tashi zaune ta fara kiciniyar sakkowa daga kan gadon saboda gabaɗaya bata gama dawo wa dai dai ba. Da dibara ta sakko daga gadon amma ko ta kan ƙunshin ƙafarta bata bi ba dama tun lokacin da Imran ya ja ƙafarta ta haɗe ƙafafun waje ɗaya duk ta caɓe lallen amma ba ta shi take ba, ita dai yanzu burinta ta yi fitsarin. Haka ta tako da ƙafafunta tana jin yadda lallan ke mata santsi a ƙafarta duk ta take shi lallan da ta ci uban buri a kan sa za ta yi ƙunshin fita kunya da suna, lallan da ta taho da shi tun daga garinsu amma kuma gashi za ta ɓata shi a banza, lallan da ta yiwa mai ƙunshin nan kuri cewa ya fi wanda take ƙunsawa su Ashrof kyau amma sai gashi abu ya zo mata a hautsine, dan tun da ta ga mala'ikam mutuwa ya zo ɗaukan ranta duk da bai ɗaukan ba, sai ta ji duniyar ta fice mata a rai komai na duniyar ya ginshe ta. A haka ta taho ko fitilar ɗakin bata kunna ba saboda tana ƙiyasta, da an ɗauki ranta da gobe da safe za a sanya ta a kabari duhun kabari kuwa ya fi na duniya sai dai fatan Allah rabamu da shi.
Haka ta fito tana taka ƙafarta dakyar dan duk ta yi sanyi, ko kallon inda Imran yake kwance bata yi ba ta zo ta wuce, shi kuwa yana kallonta har wani ɗan doro ta yi. Inna kuwa ko takalmi bata tsaya sakawa ba dama ga ledar lallan a ƙafar sai kawai ta tafi bayin a haka tana gama fitsarin ta yi tsarki ta fito, ledar lallan ta fusge ta watsar ta ƙarasa ta kunna famfo ta wanke ƙafar bata damu da ganin ko ya kama ƙunshin nata ba ko kuma ganin ya caɓe ita ba wannan ne a gabanta ba ita da za ta bar duniyar ma baki ɗaya nan da sati biyu to menene na damuwa da ƙafar da ta kusa komawa cikin ƙasa.Imran yana kallonta ta dawo ta shige ɗaki abinta jim kaɗan sai ya ganta ta kunna fitilar wayarta ta fito ɗauke da bargonta tana sanɗa, haka ta zo ta cikuikuya bargon ta saka a jakarta ta ɗakko sallayarta da hijabi a kan kujera su ma ta cusa su a ciki ta ɗakko mayafinta a kan kujera ta cusa ta ɗakko takalminta a ƙofar ɗaki ta cusa ta zige jakar. Duk abin da take Imran na kallonta kuma ya fahimci mai take shirin yi.
Sai da ta gama ta janyo jakarta a hankali.
"Wallahi guduwa zan yi daga gidan nan, na fasa ZAMAN WANKAN ƙwara in koma in mutu a ɗakina, na gwammace mutuwa ta ɗauke ni a ɗakin mijina a kan ta ɗauke ni a wani waje da ban, ƙwara in koma gida in roƙi yafiyar Malam dan dama ina zargin kamar ba da zuciya ɗaya ya barni na taho ba, dan tun da na zo birnin nan abubuwa suke faruwa da ni daga wannan sai wancan" Cewar Inna a zuciyarta tana sanya hannu ta share hawaye duk Imran yana kallonta. Sai da ta kai jakar ƙofar ɗaki ta dawo ta shige bedroom yana kallonta tana haske -haske a ɗakin da alama Sadiya da su Hassan take yiwa kallon ban kwana.
"Sa'adiyya ki yafe min na zo gidanki na hana ki sakat da sakewa da mijinki yau zan bar muku gidan ma baki ɗaya ko ma mai zai yi Imiranan ya je ya yi in ma kin samu wani cikin kin yi ciki da goyo Allah ne ya baki, kuma shi zai taya ki riƙonsu domin Allah ba ya ɗorawa bawa abin da ba zai iya ba Allah raya miki tagwayenki da ma wanda za su zo nan gaba na san wannan ne haɗuwarmu ta ƙarshe sai kuma in kin je jana'iza ta, ba zan iya tashinki daga bacci ba ki hana ni tafiya guduwa zan yi in ya so in kwana a tashar mota da asuba in samu mota in tafi gida. Kai ma Hassan ka yafe min saboda na maidaka abin zolayata kowa ya yafe min sai wata rana" Cewar Inna a hankali yadda ba za ta tashi Sadiya ba.
Duk abin da take faÉ—a Imran ya kasa kunne yana jiyo wa, sai da ta gama sai gata ta fito ta zo saitin katifarsa ta tsaya.
"To Imirana abokin karawata ka yafe min na tafi na bar maka gidanka da iyalinka Allah baku zama lafiya ya kaɗe fitina, in an samu labarin mutuwata nan da sati biyu a je jana'iza a min addu'ar samun dacewa mu tamu ta ƙare za mu tafi inda Baban Halima da su uwata mai daddawa da mai barkono suka tafi" Ta faɗa muryarta na karkarwa tare da juyawa ta nufi ƙofar ɗaki inda jakarta take duk Imran na ganinta.
Jakar tata ta kinkima dakyar ta ɗora a kan ta, sosai abin ya baiwa Imran dariya haka ta fara tafiya dakyar ga sanyin jikinta ga nauyin jakarta ga hawaye yana zuba ta nufi zauren ƙofar gida.
"Ai yadda kika hana ni tafiya lokacin da na tsinci kaina cikin tashin hankali zan bi Hajiyata haka ke ma za ki dawo ki zauna" Cewar Imran ya tashi da sauri ya kunna fitilar falo da ta tsakar gida, Inna da ta kama jamlock ta cire ta fara buɗe a hankali, ta ga hasken fitilar ya mamaye tsakar gidan, da sauri ta fasa buɗe ƙofar dan kar a ganta ta dakata dan ta sa wataƙila Imran ne ya tashi fitsari ƙwara idan ya koma ya kwanta bacci ya ɗauke shi sai ta tafi. Imran fitowa ya yi ya fara sa takalmi Inna tana jinsa, ƙofar da ta cirewa jamlock ta ja ta bata gama buɗewa ba ce ta yi ƙara.
"Shikenan Imirana zai ganni" Ta faÉ—a a zuciyarta.
"Waye a nan? Waye a zaure?" Cewar Imran cikin maida muryarsa irin ta masu bacci ya nufi zauren.
"To Imirana an falka" Cewar Inna tana wayancewa.
"Inna lafiya ina zaki da daren nan?" Cewar Imran yana haske Inna da fitilar wayarsa da ya fito da ita, ganinta ya yi ta yi hirim da uwar jaka a ka, wata dariya ce ta kusa kufce masa amma sai ya maje.
"Kai dai bari Imirana wai da yau kwanan tashar mota zan yi saboda murna"
"Murna kuma?"
"Eh mana murnar tarɓar aminiyata Tsahare shi ne zan je in kwana a tashar in jira zuwanta gobe dan na san da wuri za ta taho, sai mu taho tare duk da ta san gidan dan kar ta yi ɓatan kai"
"Kuma da tsohon daren nan sannan kuma har da jakarki za ki je taryen nata?"
"Eh, eh, eh mana"
"A'a Inna ki dai bari sai gobe kya je" Ya faɗa yana ƙarasawa ya rufe ƙofar ya maida jamlock ɗin, yana yaƙi da bakinsa kar ya kunya ta shi ta hanyar dariya dan gabaɗaya Inna tana cikin yanayin da dole sai ka yi dariya.
"Haba Imirana ya da haka kuma, ya za ka shiga tsakani na da burina, za ka shiga tsakani na da tuba na, ya za ka shiga tsakani na da mutuwa a É—akin mijina" Cewar Inna a zuciyarta tana jin kamar ta saki kuka ko ta samu sassauci.
"Ai fita cikin dare haɗari ne ga karnuka gashi baki san da wa za ki haɗu ba a hanya duniyar nan da ta ƙi daɗi ki je ma masu yankan kai su ɗauke ki su yi watanda da namanki" Cewar Imran yana kallon Inna da ta turɓune fuska.
"To, to, to, to" Cewar Inna a fili da ke ta furta to, har babu adadi dan ji take kawai Imran ya gama da ita.
"Ko ban samu masu yin watanda da namana ba ai sha huɗun rana i ta yau na daɗe a ƙiyama, un ma gudun mutuwa ake" Ta faɗa a zuciyarta.
"Yawwa ko ke fa, kawo jakar taki" Cewar Imran yana miƙa hannu ya saukewa Inna jakar daga kanta. Haka ta barshi ya sauke jakar ba dan ta so ba haka ya juyo cikin gidan da jakar a hannunsa tana jin kamar ta juya ta buɗe ƙofar ta gudu ta bar masa jakar.
"Allah na gode maka ai har na bayar sa wasiyya in nemi yafiyar jama'a" Cewar Inna a zuciyarta.
"Kuma ba a baiwa kowa labari ki ja bakin ki ki yi shiru".
"Bakina ƙanin ƙafata" Cewar Inna cikin rawar murya.
Ai Inna da ta rufe idanunta gam, ko alamar ɗagawa bata yi ba, har Imran ya lallaɓa ya tsugunna ya fice daga ɗakin da rarrafe amma Inna ko fitarsa bata ji ba. Har lokacin gabanta bai daina faɗuwa ba jikinta kuma bai bar karkarwa ba, sai da ta kwashe tsawon awa guda sannan ta miƙa hannunta na dama ta taɓo hancinta jin iska na fita daga hancin ta tabbatar bata mutu ba a hankali ta shiga buɗe idanunta cike da tsoro tana so ta tashi Sadiya ta faɗa mata sai dai tana tsoro kuma an ce kar ta faɗawa kowa.
*IMRAN*
Tun da ya fito daga ɗakin ya dawo falo ya cire kayan ya maida wanda ya cire ya sanya su a ledarsu ya mayar ƙasan kujera ya ajiye yana so da asuba sai ya fice da su in zashi masallaci. Tun da ya kwanta yake ta dariya ƙasa-ƙasa ba abin da je bashi dariya irin yadda idanun Inna suka yi ƙulu-ƙulu ita ala dole za ta mutu, ga karkarwar da jikinta ke yi kamar mazari shi kaɗai ya isa ya sanya cikinka ya yi ciwo saboda dariya.
"Ko a ina ta taɓa jin mala'ikan mutuwa yana manta wa'adin mutum har ya zo ɗaukan ran mutum amma kuma ya fasa ya ce sai wani lokacin, har ya faɗa maka lokacin ka.
"Kai ruɗani bai yi ba wallahi" Ya faɗa yana ƙyalƙyala dariya a ɓoye.
Tun da ta buɗe idon nata ta ji wani fitsari ya cika mata mara, ga tsoro da fargaba duk sun tarar mata sai kuma karkarwar da take. Jin fitsarin na neman zubowa ta ƙoƙarta ta tashi zaune ta fara kiciniyar sakkowa daga kan gadon saboda gabaɗaya bata gama dawo wa dai dai ba. Da dibara ta sakko daga gadon amma ko ta kan ƙunshin ƙafarta bata bi ba dama tun lokacin da Imran ya ja ƙafarta ta haɗe ƙafafun waje ɗaya duk ta caɓe lallen amma ba ta shi take ba, ita dai yanzu burinta ta yi fitsarin. Haka ta tako da ƙafafunta tana jin yadda lallan ke mata santsi a ƙafarta duk ta take shi lallan da ta ci uban buri a kan sa za ta yi ƙunshin fita kunya da suna, lallan da ta taho da shi tun daga garinsu amma kuma gashi za ta ɓata shi a banza, lallan da ta yiwa mai ƙunshin nan kuri cewa ya fi wanda take ƙunsawa su Ashrof kyau amma sai gashi abu ya zo mata a hautsine, dan tun da ta ga mala'ikam mutuwa ya zo ɗaukan ranta duk da bai ɗaukan ba, sai ta ji duniyar ta fice mata a rai komai na duniyar ya ginshe ta. A haka ta taho ko fitilar ɗakin bata kunna ba saboda tana ƙiyasta, da an ɗauki ranta da gobe da safe za a sanya ta a kabari duhun kabari kuwa ya fi na duniya sai dai fatan Allah rabamu da shi.
Haka ta fito tana taka ƙafarta dakyar dan duk ta yi sanyi, ko kallon inda Imran yake kwance bata yi ba ta zo ta wuce, shi kuwa yana kallonta har wani ɗan doro ta yi. Inna kuwa ko takalmi bata tsaya sakawa ba dama ga ledar lallan a ƙafar sai kawai ta tafi bayin a haka tana gama fitsarin ta yi tsarki ta fito, ledar lallan ta fusge ta watsar ta ƙarasa ta kunna famfo ta wanke ƙafar bata damu da ganin ko ya kama ƙunshin nata ba ko kuma ganin ya caɓe ita ba wannan ne a gabanta ba ita da za ta bar duniyar ma baki ɗaya nan da sati biyu to menene na damuwa da ƙafar da ta kusa komawa cikin ƙasa.Imran yana kallonta ta dawo ta shige ɗaki abinta jim kaɗan sai ya ganta ta kunna fitilar wayarta ta fito ɗauke da bargonta tana sanɗa, haka ta zo ta cikuikuya bargon ta saka a jakarta ta ɗakko sallayarta da hijabi a kan kujera su ma ta cusa su a ciki ta ɗakko mayafinta a kan kujera ta cusa ta ɗakko takalminta a ƙofar ɗaki ta cusa ta zige jakar. Duk abin da take Imran na kallonta kuma ya fahimci mai take shirin yi.
Sai da ta gama ta janyo jakarta a hankali.
"Wallahi guduwa zan yi daga gidan nan, na fasa ZAMAN WANKAN ƙwara in koma in mutu a ɗakina, na gwammace mutuwa ta ɗauke ni a ɗakin mijina a kan ta ɗauke ni a wani waje da ban, ƙwara in koma gida in roƙi yafiyar Malam dan dama ina zargin kamar ba da zuciya ɗaya ya barni na taho ba, dan tun da na zo birnin nan abubuwa suke faruwa da ni daga wannan sai wancan" Cewar Inna a zuciyarta tana sanya hannu ta share hawaye duk Imran yana kallonta. Sai da ta kai jakar ƙofar ɗaki ta dawo ta shige bedroom yana kallonta tana haske -haske a ɗakin da alama Sadiya da su Hassan take yiwa kallon ban kwana.
"Sa'adiyya ki yafe min na zo gidanki na hana ki sakat da sakewa da mijinki yau zan bar muku gidan ma baki ɗaya ko ma mai zai yi Imiranan ya je ya yi in ma kin samu wani cikin kin yi ciki da goyo Allah ne ya baki, kuma shi zai taya ki riƙonsu domin Allah ba ya ɗorawa bawa abin da ba zai iya ba Allah raya miki tagwayenki da ma wanda za su zo nan gaba na san wannan ne haɗuwarmu ta ƙarshe sai kuma in kin je jana'iza ta, ba zan iya tashinki daga bacci ba ki hana ni tafiya guduwa zan yi in ya so in kwana a tashar mota da asuba in samu mota in tafi gida. Kai ma Hassan ka yafe min saboda na maidaka abin zolayata kowa ya yafe min sai wata rana" Cewar Inna a hankali yadda ba za ta tashi Sadiya ba.
Duk abin da take faÉ—a Imran ya kasa kunne yana jiyo wa, sai da ta gama sai gata ta fito ta zo saitin katifarsa ta tsaya.
"To Imirana abokin karawata ka yafe min na tafi na bar maka gidanka da iyalinka Allah baku zama lafiya ya kaɗe fitina, in an samu labarin mutuwata nan da sati biyu a je jana'iza a min addu'ar samun dacewa mu tamu ta ƙare za mu tafi inda Baban Halima da su uwata mai daddawa da mai barkono suka tafi" Ta faɗa muryarta na karkarwa tare da juyawa ta nufi ƙofar ɗaki inda jakarta take duk Imran na ganinta.
Jakar tata ta kinkima dakyar ta ɗora a kan ta, sosai abin ya baiwa Imran dariya haka ta fara tafiya dakyar ga sanyin jikinta ga nauyin jakarta ga hawaye yana zuba ta nufi zauren ƙofar gida.
"Ai yadda kika hana ni tafiya lokacin da na tsinci kaina cikin tashin hankali zan bi Hajiyata haka ke ma za ki dawo ki zauna" Cewar Imran ya tashi da sauri ya kunna fitilar falo da ta tsakar gida, Inna da ta kama jamlock ta cire ta fara buɗe a hankali, ta ga hasken fitilar ya mamaye tsakar gidan, da sauri ta fasa buɗe ƙofar dan kar a ganta ta dakata dan ta sa wataƙila Imran ne ya tashi fitsari ƙwara idan ya koma ya kwanta bacci ya ɗauke shi sai ta tafi. Imran fitowa ya yi ya fara sa takalmi Inna tana jinsa, ƙofar da ta cirewa jamlock ta ja ta bata gama buɗewa ba ce ta yi ƙara.
"Shikenan Imirana zai ganni" Ta faÉ—a a zuciyarta.
"Waye a nan? Waye a zaure?" Cewar Imran cikin maida muryarsa irin ta masu bacci ya nufi zauren.
"To Imirana an falka" Cewar Inna tana wayancewa.
"Inna lafiya ina zaki da daren nan?" Cewar Imran yana haske Inna da fitilar wayarsa da ya fito da ita, ganinta ya yi ta yi hirim da uwar jaka a ka, wata dariya ce ta kusa kufce masa amma sai ya maje.
"Kai dai bari Imirana wai da yau kwanan tashar mota zan yi saboda murna"
"Murna kuma?"
"Eh mana murnar tarɓar aminiyata Tsahare shi ne zan je in kwana a tashar in jira zuwanta gobe dan na san da wuri za ta taho, sai mu taho tare duk da ta san gidan dan kar ta yi ɓatan kai"
"Kuma da tsohon daren nan sannan kuma har da jakarki za ki je taryen nata?"
"Eh, eh, eh mana"
"A'a Inna ki dai bari sai gobe kya je" Ya faɗa yana ƙarasawa ya rufe ƙofar ya maida jamlock ɗin, yana yaƙi da bakinsa kar ya kunya ta shi ta hanyar dariya dan gabaɗaya Inna tana cikin yanayin da dole sai ka yi dariya.
"Haba Imirana ya da haka kuma, ya za ka shiga tsakani na da burina, za ka shiga tsakani na da tuba na, ya za ka shiga tsakani na da mutuwa a É—akin mijina" Cewar Inna a zuciyarta tana jin kamar ta saki kuka ko ta samu sassauci.
"Ai fita cikin dare haɗari ne ga karnuka gashi baki san da wa za ki haɗu ba a hanya duniyar nan da ta ƙi daɗi ki je ma masu yankan kai su ɗauke ki su yi watanda da namanki" Cewar Imran yana kallon Inna da ta turɓune fuska.
"To, to, to, to" Cewar Inna a fili da ke ta furta to, har babu adadi dan ji take kawai Imran ya gama da ita.
"Ko ban samu masu yin watanda da namana ba ai sha huɗun rana i ta yau na daɗe a ƙiyama, un ma gudun mutuwa ake" Ta faɗa a zuciyarta.
"Yawwa ko ke fa, kawo jakar taki" Cewar Imran yana miƙa hannu ya saukewa Inna jakar daga kanta. Haka ta barshi ya sauke jakar ba dan ta so ba haka ya juyo cikin gidan da jakar a hannunsa tana jin kamar ta juya ta buɗe ƙofar ta gudu ta bar masa jakar.