Sashe 26
Yar Zaman Wanka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Act details FA'IZA ABUBAKAR unity bank 0020281885
Whatsapp OR
Call 09033283375
Wannan littafin kuÉ—i ne 300
Za a tura ta wannan accaunt ɗin Fa'iza Abubakar 0020281885 Unity bank shaidar biya ta wannan no 09030283375 idan katin waya ne mtn Ƴan Niger su tuntuɓi wannan no +22785885134
3ï¸ 4ï¸âƒ£5ï¸âƒ£âž¡ï¸4ï¸âƒ£6ï¸âƒ£
Tun da suka saka ta a mota ta fara wurwurga idanu, mutum huɗu ne a cikin motar gabaɗaya suna sanye da kayan sojoji, ɗaya yana jan motar shi kaɗai ne bashi da kayan sojoji. Mutum biyu ne suka sanya Inna a tsakiya kallonsu take tana so ta ga ko ta taɓa ganin wani, amma babu wanda ta gane, baki ta buɗe za ta yi magana amma ɗayan ya ɗaga bindiga ya ɗora mata a kan ta hakan ne ya sanya Inna ta ja bakinta ta yi shiru dan duk abin ta bata wasa da rai da lafiyarta.
Gum ta yi da bakinta bata sake yinƙurin yin magana ba su ma kuma duk cikinsu tun da ta shigo motar bata ji wani daga cikinsu ya yi magana ba.
Wata unguwa suka nufa da babu hayaniya sosai a ƙofar wani get suka tsaya horn aka yi mai gadi ya zo ya buɗe ƙofar suka shiga ciki Inna kuwa sai rarraba ido take yi dan ta kasa gane dalilin da ya sa aka ɗakko ta. Tunani ta fara yi ko ƴan yankan kai ne suka ɗakkota, duk da dai ta gansu da kakin soja a jikinsu amma hakan ba zai hana ta zargesu ba saboda yanzu ƴan bindiga suna kashe sojoji su ɗauke kayansu suke sanyawa, dan dai ta san wancan karon da aka ɗakko ta daga gidan masu kuɗin wannan jeji aka nufa da ita saɓanin yau kuma da aka nufo cikin gari kuma ƙeraren gida na gani na faɗa.
Haka dai ta daure saboda bakin bindigar da ke kanta. Suna fitowa ita ma haka ta bi ayari ta fito bisa bin umarnin da aka bata, tun da suka fara tafiya zuwa ainihin cikin gidan take ta kalle -kalle har suka samu nasarar shiga cikin wani falo madaidaici mai shegen kyau. Su duka wuri suka samu suka ƙame babu wanda ya nemi wurin zama Inna kuwa ganin tsayuwar ba za ta mata ba sai ta zauna a ƙasan kafet gudun kar ta hau kujera a harbeta.
Suna nan, sai ga wata yarinya ta fito cikin wasu ƙananan kaya tana riƙe da abin wasanta, Tun da ta fito Inna ta ƙura mata ido tana mata kallon sani sai dai ta kasa tuna inda ta san yarinyar tana ta kiciniya da ƙwalƙwalwarta a kan ta barta ta tuna ina ta san yarinyar amma kafin hakan sai ganin mutum ta yi ya fito daga cikin wani ɗaki shi ma sanye da kaya amma ba na sojoji ba. Kallo ɗaya Inna ta masa ta gane shi a take ta tuna da inda ta san yarinyar ma.
"Sojojo kai ne dama nan gidan ka ne ina tsohuwar matarka mai shegen tsoron nan kamar farar kura, ko da yake ma ba ita kaÉ—ai ce matsoraciyar ba har da...
Wata uwar tsawa da ya daka mata ita ce ta hana Inna da ta washe baki tana ta kauɗi da karaɗi ƙarasa maganar, dan tun kan ya ƙaraso ma tsakiyar falon ta fara zuba.
Cikin ɓacin rai ya ƙaraso tsakiyar falon gabaɗaya suka shiga sara masa kujera ya nema ya zauna har lokacin ransa a matuƙar ɓace yana aikawa Inna wani mugun kallo. Ƴar tasa ce ta zauna a kusa da shi tana ta raɓewa a jikinsa da alama dai bata manta da inda ta ga Inna ba.
"Ke inyamura ina uwaki take, yo ina so in miki magana amma na san bakya jin hausa, ina so in ce ki kira min uwaki tsohuwa mu gaisa ko yau ma tana can tana kwalliyar tana shafa jambaki kamar akuya ta ci dusa sai...
Ɗaya daga cikinsu ne ya ƙara yiwa Inna tsawar da ta sanya ta yi shiru sai dai yanzu tun da ta ga abokin Imran gaba yake da su, wato ogansu ne sai ta ji duk bata tsoronsu dan ta san dai duk tsiya ba lallai su harbe ta ba.
"Oh ni Azumi Allah ya tsaga min bakina amma ku hana ni magana, na rasa ma mai yasa kuka É—akko ni duk da dai na san ruwa ba ya tsami banza amma dai da walakin goro a miya"
Babu wanda ya mata magana dan abokin Imran ya É—aga musu hannu alamar dakatarwa.
Kallon su ya yi cikin bada umarni ya ce
"A kai ta wannan ɗakin" Da kallo Inna ta bishi tana mamakinsa amma sai ta miƙa hannunta ta taɓo saitin aljihun ɗan tofinta ta ji abin da ta ajiye yana nan hakan ya sanya ko gardama bata musu ba suka tafi da ita. Har sun je ƙofa za su fita ta juyo ta ce
"Gobe sunan Hassan dai mutuminka ina fatan za ku je" Wani haushi ne ya rufe shi yana ayyanawa a ransa tabbas tsohuwar nan yau sai ta banbance tsakanin aya da tsakuwa, dan sai ya tabbatar ta gane akwai banbanci tsakanin kiɗa da karatu. Ƙeyarta suka tisa har ɗakin da aka bada umarni a kai ta, ɗakin a can bayan gidan yake kuma a rufe yake sai da suka buɗe ɗakin suka shigar da ita ciki wani daga cikinsu wanda ya zo a kujerar mai zaman banza lokacin da suka taho a motar har ƙeya ya tallewa Inna, amma bata ce komai ba sai dai ta ayyana za ta rama ne.
Sai da suka gama harare -harare da wani tsawace -tswacensu sannan suka fito suka rufe Inna a cikin ɗakin suka sanya mukulli sai dai basu cire mukullin ba daga waje suka barshi a jikin ƙofar.
Sai da suka yi kamar minti goma da fita Inna ta tashi ta yi dibara ta ɗan buɗe windown sai da ta tabbatar babu kowa a kusa sannan ta buɗe windown duka, wani dogon icce da ta samu a ɗakin ta ɗauka ta sanyo shi ta windown a hankali cikin dibara ta saƙala iccen a jikin ƙarfen key holder na jikin mukullin, cikin dibara ta cire mukullan daga jikin ƙofar sai dai tana ƙoƙarin shigo da iccen ta windown sai mukullin ya zame daga jikin iccen ya faɗi ƙasa.
A haka ta rinƙa yin dibara har dai ta ci nasarar ɗakko shi a jikin iccen, daga ƙasan ta shigo da shi cikin ɗakin, jijjiga kai kawai take tana dariya ta ce
" Ta yaro kyau take bata ƙarko, tabbas yaro bai san wuta ba sai ya taka, lallai yau allura za ta tono garma, su a ganinsu sun garƙame ni, basu san na fisu wayo ba ko dan dogaye ne dan bashaushe ya ce dogo da hankali dace ne" Cewar Inna tana ta ƙoƙarin cire mukulli ɗaya daga jikin key holdern dan gabaɗaya mukullan iri ɗaya ne hakan ya nuna duka na ɗakin ne.
Bayan ta cire ɗaya sai ta sanya a cikin aljihunta, bayan ta ɗakko wata ƙaramar farar leda ƙulle da wani abu, tana gyaɗa kai alamar za ku gani. Sai da ta adana mukullin da ta cira ta yi murmushi ta ce
" Mu je zuwa da ni Azumi kuke zancen ai ni duk wanda ya ci tuwo da ni miya ya sha"
A hankali ta lallaɓa ta sake leƙawa har lokacin bata hango kowa ba kuma bata ji motsin kowa ba ga la'asar ta yi lis haka ta sanya mukullin ta buɗe ƙofar a hankali ta fito daga ɗakin, tana fitowa ta maida ƙofar a hankali ta rufe bayan ta rufe sai ta bar mukullin a jiki, cikin sanɗa ta fara tafiya tana ta waiwaye abinka da marar gaskiya ko cikin ruwa gumi yake. Cikin ikon Allah har ta ƙaraso ɓangaren da suka fara zuwa ita da sojojin nan wato inda ogan nasu yake abokin Imran. Shigewa ta yi dan a hankali ta tura ƙofar har ta ƙaraso falon babu wanda ya lura da ita. Laɓewa ta yi a jikin bango wani ɗan loko take leƙo falon yana zaune ya rungume ƴar sai matar ita ma daga ɗaya gefen nasa ta zauna ta kwantar da kanta a kafaɗarsa ta yi wani turum da tsohon cikinta.
" Wai da gaske an samo matar nan ta gidan abokin ka?" Cewar matar cikin gurɓayacciyar hausarta.
"Eh wallahi har nan aka shigo da ita amma saboda ƙarfin hali har tambayarki take tana miki wulaƙanci wai ko kina can kina shafa jambaki bakin ki kamar akuya...
" Haba wato kaima maimaita abin da ta ce za ka yi, tabbas yau bayan ka hukunta tsohuwar nan sai ni ma na mata hukunci mai tsanani za ta san da ni take magana"
"Ayyo to ke ma ashe shegiyar kan ki ce da ban yi niyyar miki komai ba shi kaɗai zan yiwa to tun da ke ma mummunan ƙudiri ne a ranki har ke zan haɗa, ƴar taku ce dai ba zan yiwa ba saboda ƙanƙantar ta, dan kar in ɗau alhaki" Cewar Inna a zuciyarta.
"Ayya ba dan na ɓata miki rai ba na yi baby, amma tabbas yau za ta karɓi hukunci dan kuwa zan ɗauke idanuna daga kallon tsufanta in manta alaƙarmu da Imran duk da shi ma ya ce min ta addabeshi, amma yau sai ta san wa ta yiwa abin da ta yiwa ranar nan wai dan wulaƙanci ni take cewa sojojo sai ka ce wani ɗan ƙwaya" Ya faɗa cikin gurɓatacciyar hausarsa.
"Ai kawai ka bari tsohuwar nan za ta gane kurenta, ai na gode Allah da ka aamu hutun sati biyun nan jiya gwara da ka sa aka É—akko ta mu ga tsiya" Cewar matar tana dariya.
"Za mu ga wanda zai gane kurensa ni da ku ai ni duk wanda ya ci tuwo da ni miya ya sha, kuma iya gani iya ƙyalewa ni Azumi zan nuna muku ɗan hakin da ka raina shi ke tsone maka idanu" Cewar Inna a zuciya.
Whatsapp OR
Call 09033283375
Wannan littafin kuÉ—i ne 300
Za a tura ta wannan accaunt ɗin Fa'iza Abubakar 0020281885 Unity bank shaidar biya ta wannan no 09030283375 idan katin waya ne mtn Ƴan Niger su tuntuɓi wannan no +22785885134
3ï¸ 4ï¸âƒ£5ï¸âƒ£âž¡ï¸4ï¸âƒ£6ï¸âƒ£
Tun da suka saka ta a mota ta fara wurwurga idanu, mutum huɗu ne a cikin motar gabaɗaya suna sanye da kayan sojoji, ɗaya yana jan motar shi kaɗai ne bashi da kayan sojoji. Mutum biyu ne suka sanya Inna a tsakiya kallonsu take tana so ta ga ko ta taɓa ganin wani, amma babu wanda ta gane, baki ta buɗe za ta yi magana amma ɗayan ya ɗaga bindiga ya ɗora mata a kan ta hakan ne ya sanya Inna ta ja bakinta ta yi shiru dan duk abin ta bata wasa da rai da lafiyarta.
Gum ta yi da bakinta bata sake yinƙurin yin magana ba su ma kuma duk cikinsu tun da ta shigo motar bata ji wani daga cikinsu ya yi magana ba.
Wata unguwa suka nufa da babu hayaniya sosai a ƙofar wani get suka tsaya horn aka yi mai gadi ya zo ya buɗe ƙofar suka shiga ciki Inna kuwa sai rarraba ido take yi dan ta kasa gane dalilin da ya sa aka ɗakko ta. Tunani ta fara yi ko ƴan yankan kai ne suka ɗakkota, duk da dai ta gansu da kakin soja a jikinsu amma hakan ba zai hana ta zargesu ba saboda yanzu ƴan bindiga suna kashe sojoji su ɗauke kayansu suke sanyawa, dan dai ta san wancan karon da aka ɗakko ta daga gidan masu kuɗin wannan jeji aka nufa da ita saɓanin yau kuma da aka nufo cikin gari kuma ƙeraren gida na gani na faɗa.
Haka dai ta daure saboda bakin bindigar da ke kanta. Suna fitowa ita ma haka ta bi ayari ta fito bisa bin umarnin da aka bata, tun da suka fara tafiya zuwa ainihin cikin gidan take ta kalle -kalle har suka samu nasarar shiga cikin wani falo madaidaici mai shegen kyau. Su duka wuri suka samu suka ƙame babu wanda ya nemi wurin zama Inna kuwa ganin tsayuwar ba za ta mata ba sai ta zauna a ƙasan kafet gudun kar ta hau kujera a harbeta.
Suna nan, sai ga wata yarinya ta fito cikin wasu ƙananan kaya tana riƙe da abin wasanta, Tun da ta fito Inna ta ƙura mata ido tana mata kallon sani sai dai ta kasa tuna inda ta san yarinyar tana ta kiciniya da ƙwalƙwalwarta a kan ta barta ta tuna ina ta san yarinyar amma kafin hakan sai ganin mutum ta yi ya fito daga cikin wani ɗaki shi ma sanye da kaya amma ba na sojoji ba. Kallo ɗaya Inna ta masa ta gane shi a take ta tuna da inda ta san yarinyar ma.
"Sojojo kai ne dama nan gidan ka ne ina tsohuwar matarka mai shegen tsoron nan kamar farar kura, ko da yake ma ba ita kaÉ—ai ce matsoraciyar ba har da...
Wata uwar tsawa da ya daka mata ita ce ta hana Inna da ta washe baki tana ta kauɗi da karaɗi ƙarasa maganar, dan tun kan ya ƙaraso ma tsakiyar falon ta fara zuba.
Cikin ɓacin rai ya ƙaraso tsakiyar falon gabaɗaya suka shiga sara masa kujera ya nema ya zauna har lokacin ransa a matuƙar ɓace yana aikawa Inna wani mugun kallo. Ƴar tasa ce ta zauna a kusa da shi tana ta raɓewa a jikinsa da alama dai bata manta da inda ta ga Inna ba.
"Ke inyamura ina uwaki take, yo ina so in miki magana amma na san bakya jin hausa, ina so in ce ki kira min uwaki tsohuwa mu gaisa ko yau ma tana can tana kwalliyar tana shafa jambaki kamar akuya ta ci dusa sai...
Ɗaya daga cikinsu ne ya ƙara yiwa Inna tsawar da ta sanya ta yi shiru sai dai yanzu tun da ta ga abokin Imran gaba yake da su, wato ogansu ne sai ta ji duk bata tsoronsu dan ta san dai duk tsiya ba lallai su harbe ta ba.
"Oh ni Azumi Allah ya tsaga min bakina amma ku hana ni magana, na rasa ma mai yasa kuka É—akko ni duk da dai na san ruwa ba ya tsami banza amma dai da walakin goro a miya"
Babu wanda ya mata magana dan abokin Imran ya É—aga musu hannu alamar dakatarwa.
Kallon su ya yi cikin bada umarni ya ce
"A kai ta wannan ɗakin" Da kallo Inna ta bishi tana mamakinsa amma sai ta miƙa hannunta ta taɓo saitin aljihun ɗan tofinta ta ji abin da ta ajiye yana nan hakan ya sanya ko gardama bata musu ba suka tafi da ita. Har sun je ƙofa za su fita ta juyo ta ce
"Gobe sunan Hassan dai mutuminka ina fatan za ku je" Wani haushi ne ya rufe shi yana ayyanawa a ransa tabbas tsohuwar nan yau sai ta banbance tsakanin aya da tsakuwa, dan sai ya tabbatar ta gane akwai banbanci tsakanin kiɗa da karatu. Ƙeyarta suka tisa har ɗakin da aka bada umarni a kai ta, ɗakin a can bayan gidan yake kuma a rufe yake sai da suka buɗe ɗakin suka shigar da ita ciki wani daga cikinsu wanda ya zo a kujerar mai zaman banza lokacin da suka taho a motar har ƙeya ya tallewa Inna, amma bata ce komai ba sai dai ta ayyana za ta rama ne.
Sai da suka gama harare -harare da wani tsawace -tswacensu sannan suka fito suka rufe Inna a cikin ɗakin suka sanya mukulli sai dai basu cire mukullin ba daga waje suka barshi a jikin ƙofar.
Sai da suka yi kamar minti goma da fita Inna ta tashi ta yi dibara ta ɗan buɗe windown sai da ta tabbatar babu kowa a kusa sannan ta buɗe windown duka, wani dogon icce da ta samu a ɗakin ta ɗauka ta sanyo shi ta windown a hankali cikin dibara ta saƙala iccen a jikin ƙarfen key holder na jikin mukullin, cikin dibara ta cire mukullan daga jikin ƙofar sai dai tana ƙoƙarin shigo da iccen ta windown sai mukullin ya zame daga jikin iccen ya faɗi ƙasa.
A haka ta rinƙa yin dibara har dai ta ci nasarar ɗakko shi a jikin iccen, daga ƙasan ta shigo da shi cikin ɗakin, jijjiga kai kawai take tana dariya ta ce
" Ta yaro kyau take bata ƙarko, tabbas yaro bai san wuta ba sai ya taka, lallai yau allura za ta tono garma, su a ganinsu sun garƙame ni, basu san na fisu wayo ba ko dan dogaye ne dan bashaushe ya ce dogo da hankali dace ne" Cewar Inna tana ta ƙoƙarin cire mukulli ɗaya daga jikin key holdern dan gabaɗaya mukullan iri ɗaya ne hakan ya nuna duka na ɗakin ne.
Bayan ta cire ɗaya sai ta sanya a cikin aljihunta, bayan ta ɗakko wata ƙaramar farar leda ƙulle da wani abu, tana gyaɗa kai alamar za ku gani. Sai da ta adana mukullin da ta cira ta yi murmushi ta ce
" Mu je zuwa da ni Azumi kuke zancen ai ni duk wanda ya ci tuwo da ni miya ya sha"
A hankali ta lallaɓa ta sake leƙawa har lokacin bata hango kowa ba kuma bata ji motsin kowa ba ga la'asar ta yi lis haka ta sanya mukullin ta buɗe ƙofar a hankali ta fito daga ɗakin, tana fitowa ta maida ƙofar a hankali ta rufe bayan ta rufe sai ta bar mukullin a jiki, cikin sanɗa ta fara tafiya tana ta waiwaye abinka da marar gaskiya ko cikin ruwa gumi yake. Cikin ikon Allah har ta ƙaraso ɓangaren da suka fara zuwa ita da sojojin nan wato inda ogan nasu yake abokin Imran. Shigewa ta yi dan a hankali ta tura ƙofar har ta ƙaraso falon babu wanda ya lura da ita. Laɓewa ta yi a jikin bango wani ɗan loko take leƙo falon yana zaune ya rungume ƴar sai matar ita ma daga ɗaya gefen nasa ta zauna ta kwantar da kanta a kafaɗarsa ta yi wani turum da tsohon cikinta.
" Wai da gaske an samo matar nan ta gidan abokin ka?" Cewar matar cikin gurɓayacciyar hausarta.
"Eh wallahi har nan aka shigo da ita amma saboda ƙarfin hali har tambayarki take tana miki wulaƙanci wai ko kina can kina shafa jambaki bakin ki kamar akuya...
" Haba wato kaima maimaita abin da ta ce za ka yi, tabbas yau bayan ka hukunta tsohuwar nan sai ni ma na mata hukunci mai tsanani za ta san da ni take magana"
"Ayyo to ke ma ashe shegiyar kan ki ce da ban yi niyyar miki komai ba shi kaɗai zan yiwa to tun da ke ma mummunan ƙudiri ne a ranki har ke zan haɗa, ƴar taku ce dai ba zan yiwa ba saboda ƙanƙantar ta, dan kar in ɗau alhaki" Cewar Inna a zuciyarta.
"Ayya ba dan na ɓata miki rai ba na yi baby, amma tabbas yau za ta karɓi hukunci dan kuwa zan ɗauke idanuna daga kallon tsufanta in manta alaƙarmu da Imran duk da shi ma ya ce min ta addabeshi, amma yau sai ta san wa ta yiwa abin da ta yiwa ranar nan wai dan wulaƙanci ni take cewa sojojo sai ka ce wani ɗan ƙwaya" Ya faɗa cikin gurɓatacciyar hausarsa.
"Ai kawai ka bari tsohuwar nan za ta gane kurenta, ai na gode Allah da ka aamu hutun sati biyun nan jiya gwara da ka sa aka É—akko ta mu ga tsiya" Cewar matar tana dariya.
"Za mu ga wanda zai gane kurensa ni da ku ai ni duk wanda ya ci tuwo da ni miya ya sha, kuma iya gani iya ƙyalewa ni Azumi zan nuna muku ɗan hakin da ka raina shi ke tsone maka idanu" Cewar Inna a zuciya.