Sashe 25
Yar Zaman Wanka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kai wannan tsohuwa da masifa take wato dan jaraba bata manta ba, bayan ni yanzu komai ma na manta a kan nan nawa bare har in tuna da cewa wai na ce zan basu addu,a" Cewar Malam a zuciyarsa.
"Cewa na yi addu'ar da ka ce za ka bayar wacce za a yi taro lafiya a gama lafiya, duk da ka ce ba sai an tuna maka ba amma dai na ga kana ƙoƙarin tafiya, babu niyya ango ya kwana da wando" Cewar Inna tana kallon Malam da kunya ta gama rufe shi.
" Da ku na cikin gidan, da duk wanda zai zo suna, ku karanta Qulhuwallahu ƙafa uku bayan kun gama sai ku ce Allah raba mu da mugun ji da mugun gani" Cewar Malam a fili a ransa kuma ya ce
"Ba dole in ce ku nemi tsari da mugun gani ba dan wannan micijin ai ganinsa kaÉ—ai tashin hankali ne"
"Haka za mu karanta to bari na mayar da kai ɗakin ku kwana da mugun ganin mu gani" Cewar Inna tana kallon Malam da har lokacin, carbunansa da hiraminsa suna wuyansa amma ba ta su yake ba, wannan magana da Inna ta yi ta, za ta maida shi ɗakin micijin nan ta sanya hankalinsa ya tashi dan haka ya yankewa kansa shawarar zabgawa a guje dan ya tsira da ransa. Kafin ƙiftawar ido Inna sai gani ta yi ya tattare babbar rigarsa gudun hantsilwa idan yana gudu ya zangaya a guje.
" Ka manta takalmanka da na almajiranka, da hular mai kayan aikinku da galan ɗin ruwan addu'arku, kuma baka karɓi kuɗin aikinka ba da sauran kayan aikin da ka ce za a baka" Cewar Inna da ta daddage tana faɗa masa.
"Na bar muku duka halal malak" Ya faɗa da ƙarfi har lokacin yana zabga gudu ko waiwaye ba ya yi gudun kar a samu matsala Inna ta biyo shi ta mayar da shi ɗakin miciji. Daga Inda Inna take tsaye daga ƙofar gidan da ta fito tana hango yadda ya sha wata uwar kwana a sukwane ko lanƙwasa babu.
Dariya Inna ta yi idanunta a kan motar Abid ta juyo ta dawo ciki tana ƙoƙarin rufe ƙofar sai gasu sun fito Imran da Abid.
"Innna har ya tafi baƙon naki?" Cewar Abid yana maida dariyarsa.
" Ya tafi mana amma dai ba baƙona bane baƙon Hassan ne kuma ya sallame su dan kuwa sun sha baƙar azaba kwakwa dai yau an sha ta a wajen miciji" Ta faɗa tana washe baki.
"Na gane Inna" Ya faÉ—a yana daria.
"Ba dai tafiya za ka yi ba?" Cewar Inna da mamaki.
"Ba tafiya zan yi ba kaya za mu É—akko a mota kin san kayan rabawa ne gobe muka siyo"
"Ikon Allah wato ka ji kaɗan ka ji da yawa, yanzu baƙin halin Imirana har ya kai haka, a ce zai tafi siyayyar amma ina garin nan muna gida ɗaya ɗaki ɗaya amma ya kasa gayyata ta na raka shi sai ya je ya ɗakko ka".
Wani kallo Imran ya jefa mata irin na kina kai kan ki inda Allah bai kai ki ba, kafin ya raɓa ta ya wuce wurin motar.
"Au Allah wato ina maganar ma ka wuce ka bar ni wato ga karya yo in ba karya ba waye ake bari yana haushi shi kaÉ—ai" Cewar Inna tana bin bayan Imran da harara.
"Rabu da shi Inna ba gani ba zan tsaya mu yi hira abin mu kuma kwantar da hankalinki indai kina nan to kuwa kafin ki tafi xan kai ki yawo a mota ta mu yi siyayya ki zaɓo abin da kike so in biya kuɗin" Cewar Abid yana kallon yadda fuskar Inna ta saki lokaci guda kamar an mata albishir da gidan aljanna.
"Allah Abida ka ce akwai zaɓar abubuwa masu yawa to aikuwa har sa kishiya kuka da sa kishiya tagumi zan ɗakko a wurin siyayyar"
Galala Abid ya yi jin furucin Inna dan shi dai ya ji ana cewa sa kishiya kuka ko tagumi maganin mata ne amma kuma mai Inna za ta yi da maganin mata.
"Inna sa kishiya kuka da tagumi za ki É—auka in mun je siyayya...
"Oh Abida rufani ka saya ni, dan Allah kuke bari sai mutane sun mutu kafin ku binne su.
, yo in ba fallasa auren bashi ba har na tsaya yin maganar maganin banza da kai(Maganin mata) Magano na ce magano, to indai abin da ka yi zato to Allah tsari gatari da saran shuka, to ni ina nufin kayan ƙwalam wato kayan ciye-ciyen ne zan ɗakko sa kishiya kuka da tagumi, abubuwa ne zan ɗakko masu daɗi wanda ba za su lalace ba har lokacin da zan gama ZAMAN WANKANA in tafi da kayana gidan Malam sai in ke ɗakkowa ina ci ina jefar da takardar ko ledar yadda Tasalla da ta gani za take rafka uban tagumi da hannu bibbiyu, idan ta shige ɗaki kuma ta yi ta rusar kuka saboda baƙinciki, shi na ce zan ɗakko kar ka kai ni inda Allah bai kai ni ba ka sa ni a bakin duniya" Ta kai ƙarshen maganar tana kallo Abid da ke ta faman dariyar maganar ta.
"Na gane manufarki Inna, sai Inna ta mu ta Malam bada kan ki a sare ki je gida ki ce ya faÉ—i"
"Rass kuwa Abida ai ni ce É—aya tamkar da miliyan a wajen Malam, kuma wallahi da ka ce Inna tamu sai ka sani wata Æ´ar bazawarar dariya dan ka tina min da daren jiya" Cewar Inna tana Æ´ar dariya tana kallon Imran ta gefen ido dama ganin ya kwaso kaya a mota ya taho ta faÉ—a.
"Mai kuma ya faru daren jiya Inna?" Cewar Abid yana dariyar shi ma
"Hummm kai dai bari Abida wallahi daren jiya ne abokin ka Imirana ya shiga wani hali na a zo a gani, sai ji ka yi Imirana yana, Innarmu, Inna ta" Ta faɗa tana sakin dariya irin mai ƙular da mutum ganin Imran ya zo wajensu zai fice, wani irin haɗe rai ya yi tare da wurga musu wata uwar harara. Abid kwa kawai dariya yake dan har ya hango abokinsa tabbas ya san Imran ba ƙaramar wuya ce za ta sa ya ce Innarsa ba.
"Hehehehe na dawo in ji ɗan yawon duniya, to wallahi ban san ana yi ba kunu a maƙota, kuma ban san harara ba sai ido ya faɗo ehe" Cewar Inna tana jefawa Imran hararar ita ma har da gatsi ne.
"Ƙyaleshi Inna" Cewar Abid dariya har kasa magana yake.
"Yo dama ai ba biya shi zan yi ba da ina biya Imirana ai da zamana a gidan nan bai kawo yanzu ba, ni kuwa na faɗa masa zama daram, kuma nan gani nan bari farar tunfafiya, labari kwa dole na bayar tun da ya yi abin da za a faɗa dan labari sai ma na koma ƙauyenmu in samu abin da za mu ke maimaitawa ni da aminiyata Tsahare muna darawa yo labarin abubuwan da Imirana ya yi daga zuwana zuwa yau ai abin a bayar da labari ne, dan ba tsoronsa nake ba, bada labari kuwa farillah ne tusa a masallaci, dan wallahi ina sane wai karuwa ta taka matar aure, dan kuwa ni na san karambanin akuya yasa ta leƙa ɗakin kura" Ta kai ƙarshen maganar tana wani juya ido tare da gatsine kamar wata matashiyar budurwa.
Abid kawai dariya yake a haka ya je ya buɗe motar ya ɗakko wasu kayan da wata leda mai ɗauke da apple mai yawa fari da kore ya miƙawa Inna, ta karɓa tana ta godiya kamar ta ari baki, a haka suka baro zauren dan dama a can ne tun da ya same ta za ta rufe ƙofa suka tsaya suke maganar. Ko da suka dawo ma haka ta zauna tana ta baiwa Abid labari dan haka kuwa ya zauna yana ta dariya har da riƙe ciki, amma kuwa saboda soyayya da kuma kyautatawar da Abid ke mata, Inna bata bari Abid ya ga miciji ba, dan ƙofar ma ta kulle bayan ta maida Hassan ɗin kan gadonsa dan kar Abid ya gani ya firgita dama hausawa sun ce zuciya na son mai kyautata mata.
Bayan tafiyar Abid Inna ta buɗe jakar kayanta ta ɗakko wani abu ta saka a cikin ɗan tofinta (Siket da tsofaffi suke sakawa daga ciki wand ake ɗinka musu har da aljihu a jiki) Bayan ta sanya a aljihun ɗan tofin nata ta cewa Sadiya za ta fita ta ɗan zaga ƙafarta dan ita ta gaji da zama wuri ɗaya, Sadiya kwa ta ce a dawo lafiya dan ita ma so take Innar ta fita saboda ko kaɗan in tana gidan sai an samu wani akasin. Baki ta taɓe ta ɗauki mayafinta ta yafa sannan ta ɗauki goro guda ɗaya take ci abinta ta fita. Tun da ta fito hanyar da Malam Isuhu ya bi ta nan ta bi tana yi tana kallon sawun ƙafarsa da ya yi ta sheƙa gudu ɗazu dan sawun har wani nitsewa yake a cikin ƙasa saboda yadda ake taka shi da ƙarfi, kalla kawai ta yi tana dariya wai mai sittin wata kan wata sai gashi ko izifi ɗaya bai karanta ba a ɗakin Hassan. Tafiya take abinta hankali kwance, tana cikin tafiyar, wata mota mai baƙin gilashi da wasu ke ciki suna kallon hoto a waya ɗayan ya kalli ɗayan ya ce
"Ita ce"
Aikuwa da uban gudu motar nan ta sha gaban Inna dama wajen duk ba mutane Inna da ta tsaya kallon ikon Allah ganin mota ta sha gabanta kafin ta gama tunani sai gani ta yi an fito daga ciki an fisgeta an shiga da ita motar an banke ƙofa an kwasa da uban gudu...
Masu fitar min littafi ki sani haƙƙina ne, dan haka ke ma da kike karantawa haƙƙina ne kuma baki biya ni ba.
09030283375
[24/03, 5:14 AM] Mom Mashkur First class: *MAMAN AFRAH DATA SERVICES*
*BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*
*I selling MTN data with this cheap price*
*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===150
1GB@=====250
2GB@=====500
3GB@====850
5GB@====1,400
Dial *312*4*7*4# to check Data balance.
*Validity 1 month*
*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
"Cewa na yi addu'ar da ka ce za ka bayar wacce za a yi taro lafiya a gama lafiya, duk da ka ce ba sai an tuna maka ba amma dai na ga kana ƙoƙarin tafiya, babu niyya ango ya kwana da wando" Cewar Inna tana kallon Malam da kunya ta gama rufe shi.
" Da ku na cikin gidan, da duk wanda zai zo suna, ku karanta Qulhuwallahu ƙafa uku bayan kun gama sai ku ce Allah raba mu da mugun ji da mugun gani" Cewar Malam a fili a ransa kuma ya ce
"Ba dole in ce ku nemi tsari da mugun gani ba dan wannan micijin ai ganinsa kaÉ—ai tashin hankali ne"
"Haka za mu karanta to bari na mayar da kai ɗakin ku kwana da mugun ganin mu gani" Cewar Inna tana kallon Malam da har lokacin, carbunansa da hiraminsa suna wuyansa amma ba ta su yake ba, wannan magana da Inna ta yi ta, za ta maida shi ɗakin micijin nan ta sanya hankalinsa ya tashi dan haka ya yankewa kansa shawarar zabgawa a guje dan ya tsira da ransa. Kafin ƙiftawar ido Inna sai gani ta yi ya tattare babbar rigarsa gudun hantsilwa idan yana gudu ya zangaya a guje.
" Ka manta takalmanka da na almajiranka, da hular mai kayan aikinku da galan ɗin ruwan addu'arku, kuma baka karɓi kuɗin aikinka ba da sauran kayan aikin da ka ce za a baka" Cewar Inna da ta daddage tana faɗa masa.
"Na bar muku duka halal malak" Ya faɗa da ƙarfi har lokacin yana zabga gudu ko waiwaye ba ya yi gudun kar a samu matsala Inna ta biyo shi ta mayar da shi ɗakin miciji. Daga Inda Inna take tsaye daga ƙofar gidan da ta fito tana hango yadda ya sha wata uwar kwana a sukwane ko lanƙwasa babu.
Dariya Inna ta yi idanunta a kan motar Abid ta juyo ta dawo ciki tana ƙoƙarin rufe ƙofar sai gasu sun fito Imran da Abid.
"Innna har ya tafi baƙon naki?" Cewar Abid yana maida dariyarsa.
" Ya tafi mana amma dai ba baƙona bane baƙon Hassan ne kuma ya sallame su dan kuwa sun sha baƙar azaba kwakwa dai yau an sha ta a wajen miciji" Ta faɗa tana washe baki.
"Na gane Inna" Ya faÉ—a yana daria.
"Ba dai tafiya za ka yi ba?" Cewar Inna da mamaki.
"Ba tafiya zan yi ba kaya za mu É—akko a mota kin san kayan rabawa ne gobe muka siyo"
"Ikon Allah wato ka ji kaɗan ka ji da yawa, yanzu baƙin halin Imirana har ya kai haka, a ce zai tafi siyayyar amma ina garin nan muna gida ɗaya ɗaki ɗaya amma ya kasa gayyata ta na raka shi sai ya je ya ɗakko ka".
Wani kallo Imran ya jefa mata irin na kina kai kan ki inda Allah bai kai ki ba, kafin ya raɓa ta ya wuce wurin motar.
"Au Allah wato ina maganar ma ka wuce ka bar ni wato ga karya yo in ba karya ba waye ake bari yana haushi shi kaÉ—ai" Cewar Inna tana bin bayan Imran da harara.
"Rabu da shi Inna ba gani ba zan tsaya mu yi hira abin mu kuma kwantar da hankalinki indai kina nan to kuwa kafin ki tafi xan kai ki yawo a mota ta mu yi siyayya ki zaɓo abin da kike so in biya kuɗin" Cewar Abid yana kallon yadda fuskar Inna ta saki lokaci guda kamar an mata albishir da gidan aljanna.
"Allah Abida ka ce akwai zaɓar abubuwa masu yawa to aikuwa har sa kishiya kuka da sa kishiya tagumi zan ɗakko a wurin siyayyar"
Galala Abid ya yi jin furucin Inna dan shi dai ya ji ana cewa sa kishiya kuka ko tagumi maganin mata ne amma kuma mai Inna za ta yi da maganin mata.
"Inna sa kishiya kuka da tagumi za ki É—auka in mun je siyayya...
"Oh Abida rufani ka saya ni, dan Allah kuke bari sai mutane sun mutu kafin ku binne su.
, yo in ba fallasa auren bashi ba har na tsaya yin maganar maganin banza da kai(Maganin mata) Magano na ce magano, to indai abin da ka yi zato to Allah tsari gatari da saran shuka, to ni ina nufin kayan ƙwalam wato kayan ciye-ciyen ne zan ɗakko sa kishiya kuka da tagumi, abubuwa ne zan ɗakko masu daɗi wanda ba za su lalace ba har lokacin da zan gama ZAMAN WANKANA in tafi da kayana gidan Malam sai in ke ɗakkowa ina ci ina jefar da takardar ko ledar yadda Tasalla da ta gani za take rafka uban tagumi da hannu bibbiyu, idan ta shige ɗaki kuma ta yi ta rusar kuka saboda baƙinciki, shi na ce zan ɗakko kar ka kai ni inda Allah bai kai ni ba ka sa ni a bakin duniya" Ta kai ƙarshen maganar tana kallo Abid da ke ta faman dariyar maganar ta.
"Na gane manufarki Inna, sai Inna ta mu ta Malam bada kan ki a sare ki je gida ki ce ya faÉ—i"
"Rass kuwa Abida ai ni ce É—aya tamkar da miliyan a wajen Malam, kuma wallahi da ka ce Inna tamu sai ka sani wata Æ´ar bazawarar dariya dan ka tina min da daren jiya" Cewar Inna tana Æ´ar dariya tana kallon Imran ta gefen ido dama ganin ya kwaso kaya a mota ya taho ta faÉ—a.
"Mai kuma ya faru daren jiya Inna?" Cewar Abid yana dariyar shi ma
"Hummm kai dai bari Abida wallahi daren jiya ne abokin ka Imirana ya shiga wani hali na a zo a gani, sai ji ka yi Imirana yana, Innarmu, Inna ta" Ta faɗa tana sakin dariya irin mai ƙular da mutum ganin Imran ya zo wajensu zai fice, wani irin haɗe rai ya yi tare da wurga musu wata uwar harara. Abid kwa kawai dariya yake dan har ya hango abokinsa tabbas ya san Imran ba ƙaramar wuya ce za ta sa ya ce Innarsa ba.
"Hehehehe na dawo in ji ɗan yawon duniya, to wallahi ban san ana yi ba kunu a maƙota, kuma ban san harara ba sai ido ya faɗo ehe" Cewar Inna tana jefawa Imran hararar ita ma har da gatsi ne.
"Ƙyaleshi Inna" Cewar Abid dariya har kasa magana yake.
"Yo dama ai ba biya shi zan yi ba da ina biya Imirana ai da zamana a gidan nan bai kawo yanzu ba, ni kuwa na faɗa masa zama daram, kuma nan gani nan bari farar tunfafiya, labari kwa dole na bayar tun da ya yi abin da za a faɗa dan labari sai ma na koma ƙauyenmu in samu abin da za mu ke maimaitawa ni da aminiyata Tsahare muna darawa yo labarin abubuwan da Imirana ya yi daga zuwana zuwa yau ai abin a bayar da labari ne, dan ba tsoronsa nake ba, bada labari kuwa farillah ne tusa a masallaci, dan wallahi ina sane wai karuwa ta taka matar aure, dan kuwa ni na san karambanin akuya yasa ta leƙa ɗakin kura" Ta kai ƙarshen maganar tana wani juya ido tare da gatsine kamar wata matashiyar budurwa.
Abid kawai dariya yake a haka ya je ya buɗe motar ya ɗakko wasu kayan da wata leda mai ɗauke da apple mai yawa fari da kore ya miƙawa Inna, ta karɓa tana ta godiya kamar ta ari baki, a haka suka baro zauren dan dama a can ne tun da ya same ta za ta rufe ƙofa suka tsaya suke maganar. Ko da suka dawo ma haka ta zauna tana ta baiwa Abid labari dan haka kuwa ya zauna yana ta dariya har da riƙe ciki, amma kuwa saboda soyayya da kuma kyautatawar da Abid ke mata, Inna bata bari Abid ya ga miciji ba, dan ƙofar ma ta kulle bayan ta maida Hassan ɗin kan gadonsa dan kar Abid ya gani ya firgita dama hausawa sun ce zuciya na son mai kyautata mata.
Bayan tafiyar Abid Inna ta buɗe jakar kayanta ta ɗakko wani abu ta saka a cikin ɗan tofinta (Siket da tsofaffi suke sakawa daga ciki wand ake ɗinka musu har da aljihu a jiki) Bayan ta sanya a aljihun ɗan tofin nata ta cewa Sadiya za ta fita ta ɗan zaga ƙafarta dan ita ta gaji da zama wuri ɗaya, Sadiya kwa ta ce a dawo lafiya dan ita ma so take Innar ta fita saboda ko kaɗan in tana gidan sai an samu wani akasin. Baki ta taɓe ta ɗauki mayafinta ta yafa sannan ta ɗauki goro guda ɗaya take ci abinta ta fita. Tun da ta fito hanyar da Malam Isuhu ya bi ta nan ta bi tana yi tana kallon sawun ƙafarsa da ya yi ta sheƙa gudu ɗazu dan sawun har wani nitsewa yake a cikin ƙasa saboda yadda ake taka shi da ƙarfi, kalla kawai ta yi tana dariya wai mai sittin wata kan wata sai gashi ko izifi ɗaya bai karanta ba a ɗakin Hassan. Tafiya take abinta hankali kwance, tana cikin tafiyar, wata mota mai baƙin gilashi da wasu ke ciki suna kallon hoto a waya ɗayan ya kalli ɗayan ya ce
"Ita ce"
Aikuwa da uban gudu motar nan ta sha gaban Inna dama wajen duk ba mutane Inna da ta tsaya kallon ikon Allah ganin mota ta sha gabanta kafin ta gama tunani sai gani ta yi an fito daga ciki an fisgeta an shiga da ita motar an banke ƙofa an kwasa da uban gudu...
Masu fitar min littafi ki sani haƙƙina ne, dan haka ke ma da kike karantawa haƙƙina ne kuma baki biya ni ba.
09030283375
[24/03, 5:14 AM] Mom Mashkur First class: *MAMAN AFRAH DATA SERVICES*
*BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*
*I selling MTN data with this cheap price*
*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===150
1GB@=====250
2GB@=====500
3GB@====850
5GB@====1,400
Dial *312*4*7*4# to check Data balance.
*Validity 1 month*
*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*