← Book details Tarayya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 51

Sashe 48

Tarayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari bayan sallar asuba suka wuce bayan khaleefa yakarbi duk wani tarihi na asalinsu daga hannun anees mai haqqin tattara tarihin sarakunan masarauta Wanda aka ya karbi bayanan daga mamani ya rubuce a littafin tarihi kafin rasuwarta.

Bayan tafiyarsu takira Jakadiya ta miqa mata wani zungureren saqo a rubuce tace takaiwa harooun sarkin fada.

Lokacinda Jakadiya takaiwa harooun saqon yana gama karantawa jikinsa yayi matuqar sanyi da abinda ke rubucen saidai kuma yasan hakan datake shirin yi shine qarshen abinda yake bibiyar mineelik dan haka babu bata lokaci ya fita dakansa yaje gurin Negus sarkin qirar mineelik yayi masa bayani ya karbo littafin zanen karagar mulkin qarnikan baya yadawo yabawa jekadiya takai mata.

Lokacinda Jakadiya takawo mata shirgegen littafin mai nauyi ko budesa batayiba tace,

Kije na zabi lamba ta biyar.

Babu musu Jakadiya takoma ta mayar tana jinjina alamarin rumanah sbd idan Allah ya taimaka abinda take shirin yi shine daidai.

Acikin daren ranar Negus da yaransa suka fara aiwatarda aikin qera sabuwar karagar mulkin mineelik wadda basu ta6a qera abu mai kyau da darajartaba sbd abubuwan dasuka narka ana hadawa dasu gurin qirar.

Lokacinda Jakadiya ta sanarda ammy abinda yake shirin faruwa numfashi ammy tasauke cikin danne fargabarta dan batason tunanin faruwar wani abin saidai zataje tayi magana da sultan sbd shine yasan komai ciki da waje gameda komai na karagar fiyedasu.

Da daddare bayan ko ina yayi tsit sultana ta fito ta nufi sashen sultan kai tsaye aka barta tashiga sanin matsayinta gurin assultana.

Zaune yake hankali kwance yana karatun wani shirgegen littafin tarihi yana shan madara mai zafi da aka kawo masa kullum kafin ya kwanta sbd tana qara lafiyar qwaqwalwa.

Kallo daya yayi mata yasaki murmushi yana cigaba da abinda yakeyi.

Qarasowa tayi kusadashi ta zauna cikin girmamawa ta gaidasa tana kallon littafin dayake karatu tace,

Meyasa haryanxu bazaka sauke dukkanin wani tunani na sharrin shaidanba ka fuskanci gaskia ka bita,
Ka tubarwa ubangijinka ka ajiye duk wata niyya da qudirinda bana alkhairi ba wlh Allah zai karbi tubanka sbd shi mai yafiyane ga bayin dasuka tubarmasa.

Wani irin murmushi yasaki tareda rufe littafin ya ajiye gefe ya kalleta yace,

Baiwarki kuma matar 'danki tayi babban kuskure na aikata abinda ta aikata sbd kaf tarihin mineelik babu wani sultan da aka taba muzantawa saini sultan abdulshams jinin ajani....

Numfashi tasauke cikin takaici da baqin cikin halinda mijinta yasamu kansa idanuwanta na cikowa da hawaye tace,

Son zuciyar kakannin kakanninka shine yasamu ahalinda muka tsintsi kanmu aciki karka bari zuciya takaika aikata irin kuskurensu.....

Katseta yayi da cewa,

Meya kawoki ki fada kai tsaye sbd nasan akwai abinda yakawoki a wannan lokacin.

Kallonsa tayi ganin Sam idanuwansa da zuciyarsa sun rufe..
Cikin sanyin murya tace,

Assultana na shirin canza mineelik gabaki 'daya da wata......

Da sauri ya kalleta yana ajiye cup din hannunsa sbd girgiza da zuciyarsa tayi.

Cikin bayyanarda tsananin tashin hankalinsa yace,

Zata aikata wani babban kuskuren sbd rusa karagar gabaki 'daya na nufin rusa rayuwarta sbd zata rushene tareda jininsu jamal na qarshe daya hau karagar yayi mulki akanta......

Shiru yayi zufa na karyo masa sbd yasan dagashi sai itane suka rage aduniya wainda suka taba zauna karagar har sukai mulki akanta,
A bangaren jini kuwa shikadaine jininsu na qarshe dayayi mulki akan mineelik ita 'din ba jininsu bace akwai yiyuwar abin bazai shafetaba koya shafeta saidai ta nakasta amma shi babu tantama rayuwarsace ke rawa jinin qarshe nasu jamal.

Wannan rumanah gabaki 'daya rayuwarta ta zame masa masifa mai barazana bai taba tunanin ko namiji zai iya fuskantarsaba ya girgizasa bare 'yaya mata daya dauka marasa amfani saigashi ko acikin 'yaya matan ma baiwace take barazaga rayuwarsa,

Bazai Bari su aikata hakanba dole ya juya musu zancen..
Gyara nutsuwarsa yayi cikin vasarwa yace,

Karku bari ta aikata hakan sbd rayuwartace acikin hadari dan kuwa haqqine na qarshe zai fita akanta.....

Murmushin baqin ciki ammy tasaki tareda girgiza kai hawayenta suka sauko tace,

Yanayinka da kulawar daka nuna yasamin kokwanto akan amsarka dan haka mun dangana munbarwa Allah komai zamu barta takawo qarshen mineelik duk abinda Allah ya qaddaro zamu runguma mu dauki dangana.

Miqewa tsaye tayi zata fice ya riqo hannunta akaro na farko dayaji tsoro da fargaba sun ziyarci zuciyarsa ya bude baki daqyar yace,

Karki bari ta aikata sbd rayuwatace a hadari kuma tatama na cikin hadari.

Hawayenta suka qara gudu ta sunkuyar dakai tanajin zuciyarta na karyewa sbd qaunar mijinta uban yayanta saidai kuma kodan sbd 'yayanta da jikokinta zataso akawo qarshen masifar mineelik.

Zame hannunta tayi ahankali tace,

Allah yazaba mana abinda yafi zama alkhairi.

Ficewa tayi jiki asanyaye zuciyarta na sake karyewa saidai bazata bari ta karayaba hakan da rumanah zatayi shine daidai insha Allah.

Zaune yake bakin gadonsa yayi shiru tareda zurfi cikin tunani Sam bayajin nutsuwa a zuciyarsa wani irin rashin sukuni yakeji..

Ahankali tashigo dakin rungume da abeel jikinta amatuqar sanyaye sbd jikinta datake yana tsananta dan ko yanxu kafin tafito saidata yanke jiki ta fadi jini na fita hancinta saidai bata fita hayyacinta ba kuma ta hani Jakadiya fadawa kowa abin yafara tsanani.

Qarasowa tayi ahankali ta kwantarda abeel kan sofa tadawo gefensa ta zauna ahankali tareda dafa hannunsa takalli fuskarsa.

Shima ita ya kalla ta sakar masa murmushi ahankali tareda riqe hannunsa ta lumshe ido sbd abinda taji yana taso mata ta danne yanayin daqyar tasake qaqalo murmushi tana kallon hannunsa dake cikin nata ahankali tabude baki tace,

Karka saki hannuna har lokacinda zan shaqi numfashin qarshena a duniya,
Ka zamo jiqo kuma majingini arayuwata
Ka hanani 'daukar hanyarda zata batardani zuwa duniyar daba tawaba,
Qarfin soyyarka yaci qarfin abinda nakeji ajikina saidai bansaniba ko hakan zai jima shiyasa a yanxu nake roqonka da har abada karka rabu da suhailat sbd itace macen da soyayyarta bazata taba barin cuta ta kutso kai rayuwarkaba..ni tamkar baquwace a rayuwarku ba lallaine na qarasa rayuwa acikinkuba.......

Matse hannunta dake cikin nasa yayi yana rintse idanuwansa dasukai jajir..

Hawayen datake riqewane suka 6alle mata ta kalli fuskarsa datai jajir ya rintse idanuwansa ta shafi fuskarsa hawayenta na tsananta tace,

Maheer abdulshams nagode da soyayyarka gareni..

Bude jajayen idanuwansa yayi yana kallon hawayenta dake gudu sosai yakasa magana sbd radadi da nauyin da zuciyarsa tai masa sai kawai ya rungumota jikinsa.

Ahaka suka kwana cikin wani irin sanyin jiki dana zuciya.

Kwanansu khaleefa biyu a ruwa aranar na uku da yamma sosai suka isa saidai kuma sunsha wahala sosai sbd tuni bakin ruwan yazama border saida sukasha wata irin wuya kafin suka samu wucewa da taimakon wani 'dan asalin qauyensu mamani din.

Bayan wucewarsu duk yanda sukayiwa saurayin bayani bai ganeba sbd basajin hausa ko kadan har gwara nuratu tanaji kadan kadan sbd su mamani da umman rumanah sunayi musu tun suna qanana saidai ya jasu kan mashin dinsa sukayi wani irin mugun overload yajasu dan kaisu cikin qauyen daya samu canji ba laifi.

Tafiya mai tsawo sukayi kafin suka isa qauyen mai tsananin girma da cikar mutane.

Gidan shugaban qauyen yakaisu cikin sa'a lokacinda suka isa yana gida.

Kallonsu aka taru anayi sbd ganin baqaqen labarawa musamman khaleefa dayake cikakken dan Ethiopian asali.

Bayan anbasu guri sun zauna ya fidda tambarin masarautar dasuka fito ya miqawa shugaban ya kalli nuratu yayi mata magana yace,

Kiyi musu bayaninmu yanda zasu gane ko yayane.

Gyara zama tayi muryarta na rawa tace,

Munfito daga qasar Ethiopia ne qarqashin masarautarsu,
Sun siya bayin dasuka fito daga wannan nahiyar tsawon shekara ashirin da biyar yanxu.,
Acikinsu akwai mamani da asma'u dasuka tafi da juna biyu acan suka haifi 'yaya mata dukkaninsu Wanda 'daya daga cikin 'yayan itace ni 'dayar kuma a yanxu itace sarauniyar qasar.

Da wani irin mugun mamaki suke kallonta musamman shugaban garin daya zamto kutti mijin mamani yasake kallon nuratu da gabaki 'daya take kamar yar asalin Ethiopia itama.

Cikin nutsuwa yace,

Ke 'yar wacece acikinsu?

Ni 'yar mamani ce.

Wata irin kabbara tsoffin gurin suka dauka cikeda murna da mamakin wannan alamari kutti yace,

Ina iyayenku?

Dukkaninsu Allah yayi musu rasuwa mamani ko sati batayiba yanxu haka.

Sake daukar kabbara sukayi cikin jimami da tsananin girmama wannan alamari.

Ahankali ta zayyane musu komai gameda rayuwarsu kafin ta gabatarda khaleefa amatsayin Wanda zai karbi takardun dukiyar asma'u da bulama dan neman asalin sarauniya ummu-rumanah.

Bayan dogon koke koken saduwa da baqin cikin rashinsu mamani dasu bulama nan kutti yagabatarwa da su nuratu kansa amatsayin mahaifinta.

Duk wani zuriar gidan antaru an karbi nuratu da hannu Bibbiyu da zuciya daya da wainda suka San faruwar abin da wainda ma ko haihuwarsu baayiba nan dai kowa yataru ana farin ciki.

Ganin yanayin garin yasa khaleefa yanke shawarar wucewa dan sake kutsawa cikin Nigeria dan gabatarda abinda yakawosa.

Kutti ya basa takardun dasuka tsufa sosai ga sanyin ruwa daya soma lalatasu tun wancan lokacin saidai ba laifi yana iya ganin rubutun dake jikinsu atake ya karancesu daganan ya roqi alfarmar tafiya da wani yaron kuttin dayake jin yarensu kadan kadan sbd aiki dayakeyi a border dinsu.

Da mashin din salee suka isa inda zasu samu mota bayan sunyi tafiyar awowi akan mashin din.

Motar dazata kaisu Maiduguri kai tsaye suka hau inda duk hankalin khaleefa yatashi sbd ganin inda yasamu kansa dakuma wata irin azabar wuyar tafiya data fara gigitasa.

Gaf da asuba suka isa Maiduguri kai tsaye wani lafiyayyan babban hotel suka sauka anan yayi baccin wahala ga zazzabin dakeson kamasa na baqar wuyar dabai taba shaba.
#mamuhgee

*_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association💡_

*44*

Not edited.
Duk yanda yaso yayi komai cikin lokaci yakoma hakan bai samuba sbd zazzabi mai qarfi daya kwantar dashi tsawon kwana biyu
Qarshe dai dole ya daure suka tafi kai tsaye companyn dake rubuce a jikin takardun da taimakon wani ma'aikacin hotel din suka isa.

Da farko sunsha wahala kafin suka samu ganin shugaban companyn alhaji babaye salmanu bulama.

Kai tsaye khaleefa yafitarda takardun dayazo dasu ya ajiye gaban alhaji babaye.

Kallo daya yayi musu harzai dauke kai yayi magana yaga sunan dake jikinsu yayi musu wata irin damqa yana dubawa sbd basuyi masa kama dana yanxuba wannan rubutu da sunan company dinne tunna iyayensu na shekarun dasuka wuce.

Budesu yaringayi daya bayan daya haryakai qarshe ya miqe tsaye sbd tabbarda sune asalin takardun da 'yayansa da matarsa suka tafi dasu.
Chapter 48 · 0% Book details