Sashe 13
Tarayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gashinta azube yake har bayanta yaji adon sarkokin zinari nakai har zuwa kafadunta hakama wuyanta sarkace har saman cikinta ta zinari,
Wani irin kyau da kyalli take fitarwa daidai hannuwanta a lalace suke kaca kaca da jini har jikin rigartama haka
kujerar karagar mulkin mineelik Wanda keta tsiyayar jini wasu irin samudawan guards suka ajiye mata tasaki wani irin qayataccen murmushi zata zauna......
Cikin wani matsanancin ihu takira sunanta da qarfi tana cewa,
Rumanahhhhhh karki zauna a wannan kujerar......rumanahhhhh
Zama tayi cikin wani irin iko da mulki nan gari yadauki ihun sunanta.
Amatuqar gigice sultana ta zabura daga baccinta tana tareda lalubar bedside lamp takunna da sauri jikinta na muguwar karkarwa tafara karanta innalillahi tana hada wani mugun gumi.,
Wannan mafarkin nata babu alkhairi acikinsa,
Meya hadata da wannan mummunan mafarkin?
Tsoro da fargaba taji yana shigarta tayi saurin saukowa tafada toilet tayo alwala tazo tafara jera nafiloli kafin asuba tayi.
Har gari ya waye bata sake ko kwanciyaba bare rintsawa,
Abinda tagani amafarki tamkar wani gargadine ga abinda suke shirin yiwa rumanah bata fatar ko acikin bacci tasake irin wannan mafarkin bare ya tabbata.
Dan haka ta yanke shawara komai zai faru shirye takeda daukar hukuncin sultan.
Qarfe goma sha 'daya na rana saqon kiran sultan yazo gareta babu bata lokaci ta miqe cikin shirinta da adonta ta nufi part dinsa kuyanginta na biyeda ita,
Duk inda ta gifta kafin ta qaraso anrabe anxube qasa ana gaidata cikin matuqar girmamawa harta isa tun a qofar palon farko suka dakata itada Jakadiya data fito tarbonta suka qarasa.
Tana isa jikinta yayi mugun sanyi sbd ganin yanda kowa ya dauke wuta sai mizurai akeyi sbd ran sultan ya baci kuma kowa yasan hukuncinsa ba sauqi ba kyau haka itama ta isa kujerar dake matsayin tata tazauna bayan ta kwashi gaisuwa.
Maheer ransa amatuqar bace yake sbd baisan hukuncinda sultan zai yankeba akan ammynsa.
Cikin kakkaisar murya yakalli Jakadiya yace,
Inason jin dalili qwaya 'daya daya daga yarima Wanda ya hanasa cika umarnin sultan dinsa.
Cikin rawar murya Jakadiya takalli yarima zata maimaita masa abinda sultan ya tambaya batareda yakalli ko dayansuba kai tsaye yace,
Banada sha'awar kowace mace bayan wadda igiyoyin aurena suke kanta.
Wani numfashin bacin rai sultan yafitar yana kallon yarima sbd yasan daga yau hukuncinda zai yanke akansa yagama da rayuwarsa gaba daya cikin isa da mulki yabude baki yace,
Jakadiya atambayesa yana buqatar qarin lokaci kokuwa shikenan......
Cikin tsananin dauriya da danne fargabarta da fargabar abinda zai biyo bayan abinda zatayi tabude baki tace,
Ina neman afuwar sultan amma baiwa rumanah ta haramta garesa daga yau sbd na 'yantata daga wannan lokacin harzuwa qarshen rayuwarta,
Daga yanxu ita ba baiwa bace sbd haka ta haramta ga kowane namiji idan ba mijin aurentaba.
Cikin wani irin mugun mamaki da 6acin rai dabai taba yiba yake kallonta jin abinda tafada,
Ta 'yanta baiwarda yabada umarnin yarima ya kwana da ita kenan 'danta takare daga aikata abinda baiso
Tabbas zasu 'dandani hukuncin sultan daga ita har 'danta.
'Dagowa yayi yakalli wazirinsa cikin wani irin yanayi na nuna rashin damuwa yace,
Ta 'yanta baiwarta sbd ta rahamtata ga 'danta sbd bayaso nikuma zan halasta masa ita ayau sbd umarnin sultan baya bin iska,
*_KUJE ABADA SANARWAR 'DAURIN AUREN YARIMA MAHEER IBN ABDULSHAMS ABDALLAH DA 'YANTACCIYAR BAIWA UMMU-RUMANAH BULAMA_* nanda awa biyar duk Wanda baizo ya shaida 'daurin aurenba nakoresa daga qasata sai bayan shekara biyar yadawo.,,
*_SULTANA ZAARAH BAYAN 'DAURIN AURE ZATA KOMA GURIN IYAYENTA BAZATA DAWOBA SAI MATAR YARIMA MAHEER RUMANAH TA HAIHU._*
#mamuhgee
[27/06, 06:14] 80k: *_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association💡_
*16*
Not edited.⚠
Wani irin kallo sultana ta 'dago tayi masa cikeda mamaki da takaicin abinda yake shirin yi kafin ta bude baki tayi magana cikeda nuna isarsa da matsayinsa yace,
Lij(sadaukin kuma amintaccen mayaqin meneelik) duk wanda ya nuna rashin gamsuwa da hukuncin sultan ko a fuskane ko wanene shi arabasa da abinda yafiso ajikinsa,
Idan nace ko wanene ina nufin kowanene,
Jakadiya kije ashirya sabuwar surukar sultan nanbada jimawaba zata zama uwar magajin meneelik.
Yana gama fada ya miqe yashige palonsa na hutawa tareda manyan masarauta dazasu tattauna wani abin,
Wasu majiya qarfin samudawa suka tsaya qofar Dan bata tsaro.
Kai tsaye ya miqe yabar palon batareda fuskarsa ta nuna meke cikin zuciyarsaba.
Sultana ma miqewa tayi jikinta amatuqar sanyaye zuciyarta cikeda takaici da tunanin rashin ganin amfanin 'yantawarda tayiwa rumanah tunda hakan baisa ta tsirar da ita daga masifar datake gudar mataba ta haihuwar namiji a wannan masarauta ta mineelik.
Jakadiya kuwa wani irin zufa take yarfewa Tana qoqarin ganin ancika umarnin sultan saidai itama damuwarta da tsoronta yahana farincikinta wanxuwa musamman idan taduba yanayin tsoro da fargabar dake yawan samunsu idan sukayi tunanin rabon dazai shiga tsananin yarima da rumanah.,
Wannan masarauta batada tarihi mai kyau,
Jinin mutanen da ake kashewa yananan yana bibiyar duk wani hakkinsa,
Masiface acikeda masarautar wadda babu Wanda yasanta saisu dasuka ginu acikinta
Har abada bazata ta6a yiwa rumanah fatar shiga cikin jerin wainda masifar zata cigaba da shigarsuba aqarshe tabasu qarshe mai matuqar tausayi da kokawa saidai tasan bawa baya wuce qaddararsa,
Duk dubararsu da qoqarin kubutarda ita idan Allah yace tana cikin masu wannan mummunan qaddarar saita shiga.
Zubewa sultana tayi kan daya daga cikin kujerun palonta na farko sbd bazata iya qarasawa na biyunba tareda 'dagawa kuyanginta hannu nan suka watse cikin girmamawa.
Dafe goshinta dake daukeda adon sarqar zinari tayi tareda rufe ido tarasa wane irin hali zuciyarta take ciki sbd takasa riqe tunani ''daya dazatayi cikin biyu auren maheer da rumanah kokuwa korarda sultan yamata gefe 'daya kuma tsoro ne fal yafi cika mata zuciya.
Ya Allah kadubi maraicin rumanah kazaba mata kyakkyawar rayuwa agaba.
Tana cikin wannan halin Jakadiya tashigo 'yan mata biyar na bayanta 'daukeda manyan trays suna qyalli kamar zinari suka jeru sanku sunkuye.
Kallo daya Jakadiya tayiwa sultana 'din tasan tana cikin tension murya asanyaye tace,
Allah taimaki sultana anshirya zuwa gurin shirya sabuwar amaryar yarima maheer sa albarki akazo karba.
'Dago fuskarta datai ja tayi takalli jakadiya batareda tace komaiba ta miqe tashiga bedroom dinta tafito da wani madaidaicin akwati yana kyalli.
Zama tayi tareda aje akwatin batareda takalli jakadiya ba murya ba kuzari tace,
Allah yasawa aure albarka.
Amin jakadiya tace tareda kai hannu tabude akwatin.
Sarqoqin zinari ne masu nauyi da marasa nauyi nakai dana qafafu taredana wuya da awarwaro har kusan basa qirguwa.
Hannu Jakadiya tasa tana zarosu tana zubawa acikin tray dinda suka shigo dasu harsaida tray din yacika suka fice,
Sashen adama suka isa tana zaune cikin royal kushins din dasuka qayata palonta cikeda girmamawa aka iso mata da saqon zuwansu Jakadiya tace sushigo.
'Yan matanda ke bayan Jakadiya 'daukeda manyan trays din takalla cikeda mamaki sbd alamu na sakawa aure albarka zaka bayar.,
Wane zaiyi aure kuma ayau batareda tasaniba?
Lallai ana wasa da ita amma karsu damu da zarar ta 'Dora mazaunanta akan kujerar mulkin mineelik tayi alqawarin bawa dabbobin dake zagaye da qasar naman wainda suke wasa da alamarinta.
Cikin girmamawa Jakadiya ta katseta da cewa,
Sultana zaarah ta 'yanta baiwarta ummu-rumanah ayau kuma ayau sultan zai aurawa yarima maheer ita akan sadaki tiren zinari,
Sultana ta bada nata tiren saka albarkar aure saurake gimbiya adama ina fatar ba'a shiga cikin lokacin hutawarkiba.
Cikin wani irin yanayi na mamaki ta kalli Jakadiya tace,
Aure tsakanin yarima da baiwa?
Kozansan dalilin wannan auren na gaggawa?
Allah yataimakeki maganar dai 'dayace.
Rintse ido tayi tareda Jan numfashi cikin takaici
Sam sultan bazai bari tashaqi numfashi mai dadi ba sbd wannan masifar tasa tason haihuwar magajin mineelik,
Meyasa koyaushe yake son 6ata mata aiki idan yayi nisa,
Tana qyalewane ta lafe sbd bokanta yace mata sa'arta ba yanxu takeba saizuwa gaba takwantarda hankali tajira sbd ba'a taba haihuwar namiji ba a masarautar yayi duba yaga tabbas mace ce zatayi mulkin mineelik bayan sultan takuma tabbatarda itace macenda zatayi mulki amma badan hakaba da tuni tasaka anbinne sultan da ransa takaiga cikar burinta.
Murmushi tasaki tana 'dauke gira 'daya tace,
Allah yayiwa aure albarka.
Sarkar jikinta data kanta taredata qafafunta tasa baiwarta nuratu ta cire ta daura akan tray din suka miqe suka fice.
Nuratu duk ilahirin jikinta rawa yakeyi gurin cire mata sbd tsananin farin cikin data shiga jin zancen,
Ta matsu tagama yiwa sarauniya adama yankan fruits taje tafadawa mamani sbd yau tun safe adama tasakata aikin abinci kusan kala biyar sbd 'yarta meenah zata zo hutun makaranta daga Sydney.
Part dinsa ya isa cikin wani irin yanayi da babu mai iya gano maike zuciyarsa ya zauna kan sofa tareda rintse idanuwansa yana shafo sumar kansa.,
Miqewa yasakeyi ya nufi bathroom yashiga cikin bathtub bai tsaya bata lokaciba yayi wanka yafito ya zauna gaban mirror yana goge jikinsa,
Shiri yayi cikin Ethiopian royal kaftans black and golden wainda yasaka ranar daurin aurensa da suhailat.,
Turare yafesa tareda saka takalmi ya fesa turare tareda gyara gashinsa mai 'Dan tsawo ya 'daure tsakiyar kai yasaka hula batareda yakalli kansa a madubi ba ya nufi qofa ya fita inda guards kusan guda goma da fadawan sultan suke jiransa Dan masa rakiya har gurin daurin auren.
Zaune take kan kujerar mirror ita kadai kamar koyaushe shiru tayi nisa cikin tunani tareda qurawa kanta ido.
Qura mata ido Jakadiya tayi kafin tayi gyaran murya tareda yiwa 'yan matan alama da ido cikin nutsuwa suka zo gaban rumanah data miqe cikeda ladabi tana gaida Jakadiya suka Jere matansu.
Sam bata shiga ko saka kanta ga duk abinda tasan bai shafetaba shiyasa ko inda aka ajiye kayan bata kallaba ta sunkuyar dakanta tana jiran umarni daga jakadiya sbd tasan dole akwai abinda yakawota.
Fuskarta Jakadiya take kallo tace,
Ayau sultana zaarah matar sultan abdulshams sarkin masarautar mineelik ta 'yantaki ummu-rumanah bulama sbd ki auri 'danta 'yarima maheer Wanda za'a daura miki aure dashi yanxu nanda mintuna qalilan.
Kallon Jakadiya tayi da kyau taga fuskarta babu wasa ko raini yasa tayi qasa da kanta sbd tasan babu abinda zaisa Jakadiya tafadi abinda bahakaba sbd dokace a masarautar duk Wanda yayi kuskuren qarya aka ganosa allurar dabazai qara maganaba ake masa shikenan yazama kurma shiyasa duk tsanani duk wuya ba'a qarya a mineelik.
Wani irin kyau da kyalli take fitarwa daidai hannuwanta a lalace suke kaca kaca da jini har jikin rigartama haka
kujerar karagar mulkin mineelik Wanda keta tsiyayar jini wasu irin samudawan guards suka ajiye mata tasaki wani irin qayataccen murmushi zata zauna......
Cikin wani matsanancin ihu takira sunanta da qarfi tana cewa,
Rumanahhhhhh karki zauna a wannan kujerar......rumanahhhhh
Zama tayi cikin wani irin iko da mulki nan gari yadauki ihun sunanta.
Amatuqar gigice sultana ta zabura daga baccinta tana tareda lalubar bedside lamp takunna da sauri jikinta na muguwar karkarwa tafara karanta innalillahi tana hada wani mugun gumi.,
Wannan mafarkin nata babu alkhairi acikinsa,
Meya hadata da wannan mummunan mafarkin?
Tsoro da fargaba taji yana shigarta tayi saurin saukowa tafada toilet tayo alwala tazo tafara jera nafiloli kafin asuba tayi.
Har gari ya waye bata sake ko kwanciyaba bare rintsawa,
Abinda tagani amafarki tamkar wani gargadine ga abinda suke shirin yiwa rumanah bata fatar ko acikin bacci tasake irin wannan mafarkin bare ya tabbata.
Dan haka ta yanke shawara komai zai faru shirye takeda daukar hukuncin sultan.
Qarfe goma sha 'daya na rana saqon kiran sultan yazo gareta babu bata lokaci ta miqe cikin shirinta da adonta ta nufi part dinsa kuyanginta na biyeda ita,
Duk inda ta gifta kafin ta qaraso anrabe anxube qasa ana gaidata cikin matuqar girmamawa harta isa tun a qofar palon farko suka dakata itada Jakadiya data fito tarbonta suka qarasa.
Tana isa jikinta yayi mugun sanyi sbd ganin yanda kowa ya dauke wuta sai mizurai akeyi sbd ran sultan ya baci kuma kowa yasan hukuncinsa ba sauqi ba kyau haka itama ta isa kujerar dake matsayin tata tazauna bayan ta kwashi gaisuwa.
Maheer ransa amatuqar bace yake sbd baisan hukuncinda sultan zai yankeba akan ammynsa.
Cikin kakkaisar murya yakalli Jakadiya yace,
Inason jin dalili qwaya 'daya daya daga yarima Wanda ya hanasa cika umarnin sultan dinsa.
Cikin rawar murya Jakadiya takalli yarima zata maimaita masa abinda sultan ya tambaya batareda yakalli ko dayansuba kai tsaye yace,
Banada sha'awar kowace mace bayan wadda igiyoyin aurena suke kanta.
Wani numfashin bacin rai sultan yafitar yana kallon yarima sbd yasan daga yau hukuncinda zai yanke akansa yagama da rayuwarsa gaba daya cikin isa da mulki yabude baki yace,
Jakadiya atambayesa yana buqatar qarin lokaci kokuwa shikenan......
Cikin tsananin dauriya da danne fargabarta da fargabar abinda zai biyo bayan abinda zatayi tabude baki tace,
Ina neman afuwar sultan amma baiwa rumanah ta haramta garesa daga yau sbd na 'yantata daga wannan lokacin harzuwa qarshen rayuwarta,
Daga yanxu ita ba baiwa bace sbd haka ta haramta ga kowane namiji idan ba mijin aurentaba.
Cikin wani irin mugun mamaki da 6acin rai dabai taba yiba yake kallonta jin abinda tafada,
Ta 'yanta baiwarda yabada umarnin yarima ya kwana da ita kenan 'danta takare daga aikata abinda baiso
Tabbas zasu 'dandani hukuncin sultan daga ita har 'danta.
'Dagowa yayi yakalli wazirinsa cikin wani irin yanayi na nuna rashin damuwa yace,
Ta 'yanta baiwarta sbd ta rahamtata ga 'danta sbd bayaso nikuma zan halasta masa ita ayau sbd umarnin sultan baya bin iska,
*_KUJE ABADA SANARWAR 'DAURIN AUREN YARIMA MAHEER IBN ABDULSHAMS ABDALLAH DA 'YANTACCIYAR BAIWA UMMU-RUMANAH BULAMA_* nanda awa biyar duk Wanda baizo ya shaida 'daurin aurenba nakoresa daga qasata sai bayan shekara biyar yadawo.,,
*_SULTANA ZAARAH BAYAN 'DAURIN AURE ZATA KOMA GURIN IYAYENTA BAZATA DAWOBA SAI MATAR YARIMA MAHEER RUMANAH TA HAIHU._*
#mamuhgee
[27/06, 06:14] 80k: *_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association💡_
*16*
Not edited.⚠
Wani irin kallo sultana ta 'dago tayi masa cikeda mamaki da takaicin abinda yake shirin yi kafin ta bude baki tayi magana cikeda nuna isarsa da matsayinsa yace,
Lij(sadaukin kuma amintaccen mayaqin meneelik) duk wanda ya nuna rashin gamsuwa da hukuncin sultan ko a fuskane ko wanene shi arabasa da abinda yafiso ajikinsa,
Idan nace ko wanene ina nufin kowanene,
Jakadiya kije ashirya sabuwar surukar sultan nanbada jimawaba zata zama uwar magajin meneelik.
Yana gama fada ya miqe yashige palonsa na hutawa tareda manyan masarauta dazasu tattauna wani abin,
Wasu majiya qarfin samudawa suka tsaya qofar Dan bata tsaro.
Kai tsaye ya miqe yabar palon batareda fuskarsa ta nuna meke cikin zuciyarsaba.
Sultana ma miqewa tayi jikinta amatuqar sanyaye zuciyarta cikeda takaici da tunanin rashin ganin amfanin 'yantawarda tayiwa rumanah tunda hakan baisa ta tsirar da ita daga masifar datake gudar mataba ta haihuwar namiji a wannan masarauta ta mineelik.
Jakadiya kuwa wani irin zufa take yarfewa Tana qoqarin ganin ancika umarnin sultan saidai itama damuwarta da tsoronta yahana farincikinta wanxuwa musamman idan taduba yanayin tsoro da fargabar dake yawan samunsu idan sukayi tunanin rabon dazai shiga tsananin yarima da rumanah.,
Wannan masarauta batada tarihi mai kyau,
Jinin mutanen da ake kashewa yananan yana bibiyar duk wani hakkinsa,
Masiface acikeda masarautar wadda babu Wanda yasanta saisu dasuka ginu acikinta
Har abada bazata ta6a yiwa rumanah fatar shiga cikin jerin wainda masifar zata cigaba da shigarsuba aqarshe tabasu qarshe mai matuqar tausayi da kokawa saidai tasan bawa baya wuce qaddararsa,
Duk dubararsu da qoqarin kubutarda ita idan Allah yace tana cikin masu wannan mummunan qaddarar saita shiga.
Zubewa sultana tayi kan daya daga cikin kujerun palonta na farko sbd bazata iya qarasawa na biyunba tareda 'dagawa kuyanginta hannu nan suka watse cikin girmamawa.
Dafe goshinta dake daukeda adon sarqar zinari tayi tareda rufe ido tarasa wane irin hali zuciyarta take ciki sbd takasa riqe tunani ''daya dazatayi cikin biyu auren maheer da rumanah kokuwa korarda sultan yamata gefe 'daya kuma tsoro ne fal yafi cika mata zuciya.
Ya Allah kadubi maraicin rumanah kazaba mata kyakkyawar rayuwa agaba.
Tana cikin wannan halin Jakadiya tashigo 'yan mata biyar na bayanta 'daukeda manyan trays suna qyalli kamar zinari suka jeru sanku sunkuye.
Kallo daya Jakadiya tayiwa sultana 'din tasan tana cikin tension murya asanyaye tace,
Allah taimaki sultana anshirya zuwa gurin shirya sabuwar amaryar yarima maheer sa albarki akazo karba.
'Dago fuskarta datai ja tayi takalli jakadiya batareda tace komaiba ta miqe tashiga bedroom dinta tafito da wani madaidaicin akwati yana kyalli.
Zama tayi tareda aje akwatin batareda takalli jakadiya ba murya ba kuzari tace,
Allah yasawa aure albarka.
Amin jakadiya tace tareda kai hannu tabude akwatin.
Sarqoqin zinari ne masu nauyi da marasa nauyi nakai dana qafafu taredana wuya da awarwaro har kusan basa qirguwa.
Hannu Jakadiya tasa tana zarosu tana zubawa acikin tray dinda suka shigo dasu harsaida tray din yacika suka fice,
Sashen adama suka isa tana zaune cikin royal kushins din dasuka qayata palonta cikeda girmamawa aka iso mata da saqon zuwansu Jakadiya tace sushigo.
'Yan matanda ke bayan Jakadiya 'daukeda manyan trays din takalla cikeda mamaki sbd alamu na sakawa aure albarka zaka bayar.,
Wane zaiyi aure kuma ayau batareda tasaniba?
Lallai ana wasa da ita amma karsu damu da zarar ta 'Dora mazaunanta akan kujerar mulkin mineelik tayi alqawarin bawa dabbobin dake zagaye da qasar naman wainda suke wasa da alamarinta.
Cikin girmamawa Jakadiya ta katseta da cewa,
Sultana zaarah ta 'yanta baiwarta ummu-rumanah ayau kuma ayau sultan zai aurawa yarima maheer ita akan sadaki tiren zinari,
Sultana ta bada nata tiren saka albarkar aure saurake gimbiya adama ina fatar ba'a shiga cikin lokacin hutawarkiba.
Cikin wani irin yanayi na mamaki ta kalli Jakadiya tace,
Aure tsakanin yarima da baiwa?
Kozansan dalilin wannan auren na gaggawa?
Allah yataimakeki maganar dai 'dayace.
Rintse ido tayi tareda Jan numfashi cikin takaici
Sam sultan bazai bari tashaqi numfashi mai dadi ba sbd wannan masifar tasa tason haihuwar magajin mineelik,
Meyasa koyaushe yake son 6ata mata aiki idan yayi nisa,
Tana qyalewane ta lafe sbd bokanta yace mata sa'arta ba yanxu takeba saizuwa gaba takwantarda hankali tajira sbd ba'a taba haihuwar namiji ba a masarautar yayi duba yaga tabbas mace ce zatayi mulkin mineelik bayan sultan takuma tabbatarda itace macenda zatayi mulki amma badan hakaba da tuni tasaka anbinne sultan da ransa takaiga cikar burinta.
Murmushi tasaki tana 'dauke gira 'daya tace,
Allah yayiwa aure albarka.
Sarkar jikinta data kanta taredata qafafunta tasa baiwarta nuratu ta cire ta daura akan tray din suka miqe suka fice.
Nuratu duk ilahirin jikinta rawa yakeyi gurin cire mata sbd tsananin farin cikin data shiga jin zancen,
Ta matsu tagama yiwa sarauniya adama yankan fruits taje tafadawa mamani sbd yau tun safe adama tasakata aikin abinci kusan kala biyar sbd 'yarta meenah zata zo hutun makaranta daga Sydney.
Part dinsa ya isa cikin wani irin yanayi da babu mai iya gano maike zuciyarsa ya zauna kan sofa tareda rintse idanuwansa yana shafo sumar kansa.,
Miqewa yasakeyi ya nufi bathroom yashiga cikin bathtub bai tsaya bata lokaciba yayi wanka yafito ya zauna gaban mirror yana goge jikinsa,
Shiri yayi cikin Ethiopian royal kaftans black and golden wainda yasaka ranar daurin aurensa da suhailat.,
Turare yafesa tareda saka takalmi ya fesa turare tareda gyara gashinsa mai 'Dan tsawo ya 'daure tsakiyar kai yasaka hula batareda yakalli kansa a madubi ba ya nufi qofa ya fita inda guards kusan guda goma da fadawan sultan suke jiransa Dan masa rakiya har gurin daurin auren.
Zaune take kan kujerar mirror ita kadai kamar koyaushe shiru tayi nisa cikin tunani tareda qurawa kanta ido.
Qura mata ido Jakadiya tayi kafin tayi gyaran murya tareda yiwa 'yan matan alama da ido cikin nutsuwa suka zo gaban rumanah data miqe cikeda ladabi tana gaida Jakadiya suka Jere matansu.
Sam bata shiga ko saka kanta ga duk abinda tasan bai shafetaba shiyasa ko inda aka ajiye kayan bata kallaba ta sunkuyar dakanta tana jiran umarni daga jakadiya sbd tasan dole akwai abinda yakawota.
Fuskarta Jakadiya take kallo tace,
Ayau sultana zaarah matar sultan abdulshams sarkin masarautar mineelik ta 'yantaki ummu-rumanah bulama sbd ki auri 'danta 'yarima maheer Wanda za'a daura miki aure dashi yanxu nanda mintuna qalilan.
Kallon Jakadiya tayi da kyau taga fuskarta babu wasa ko raini yasa tayi qasa da kanta sbd tasan babu abinda zaisa Jakadiya tafadi abinda bahakaba sbd dokace a masarautar duk Wanda yayi kuskuren qarya aka ganosa allurar dabazai qara maganaba ake masa shikenan yazama kurma shiyasa duk tsanani duk wuya ba'a qarya a mineelik.