Sashe 39
Tarayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
yana kwance ya dunkukune a marufinshi yaji an tsaya abakin tantinsa ana cewa.
"Ajaniiiiiiiiiii"
D'auke numfashinsa yayi cak, tsabar tsoron, haka aka kewayasu ana razanasu.
Wasa wasa sai da suka kwashi fiyye da wata biyar ana tsoratasu da abubuwa a gurin tuni suka saba da rayuwa adajin sbd dama dukkaninsu sunsaba da rayuwa a daji dan haka yanzu gida suka dauki dajin sbd burinsu abune dazasu iya komai akansa.
lokacin da suka cika wata shida Ajani yaje ya faɗawa boka abinda ya faru, nan ya zauna ya faɗa mishi abinda zasuwa Mineelik dazaran ta faɗa soyayya da Jamal. Bokan ya cigaba da cewa,
" Matuƙar mukace muna son dukiyar baxata bamu cikin lumana ba. Karshe rabaku xatayi da ɗan uwanku amma idan mukayi haka toh babu wata damuwa sannan zan nema muku abubuwan da zakuyi amfani dashi, karka bari ɗan uwanka yaji labarin dan matukar yaji bazai yarda yayi aikin ba."
Gyaɗa kai ajani yayi sannan yabar garin ya koma dajin, nan suka cigaba da zama ga tsoratasu da ake ga kwanakin kamar baya tafiya, duk sun kaqu da faruwan haka,
Da zaran sun zauna hiransu kenan, akan yanda zasu juya dukiyarsu da suka samu, daga gareta, a hankali lokacin yana tafiya wasa wasa sai gashi har saura kwanaki bakwai zata bayyana,
......
Bayan kwana huɗu wata rana da safe suka tashi da mugun faɗa kaman zasu kashe junarsu, kaman dai yanda bokan ya faɗa musu, karshe rabuwa dasu Jamal yayi ya koma gefe dan ya hassaso wannan rigimar yana cikin alamomin bayyanarta nan yatunatar dasu nan kowa yayi nesa da 'dan uwansa suna fidda wani irin gumi najin wani irin qarfi mai razanarwa na son kashe dan uwansa.
rana tabiyu kuwa sun tashi da babu giftawar tsuntsaye ko ɗaya tareda wani irin tsoro mai firgitarwa dayake shigarsu wanda suka tabbarda natane amma haka suka dinga daurewa cikin wata irin jarumta.
Rana mafi tashin hankali shine ranar bayyanarta tsananin zafin da ake yaja sukaita fad'uwa, gashi sun shanye ruwansu, dakyar Jamal ya mike yace.
"Yaku Y'an uwana wannan itace rana mafi hadari ageremu saidai ina fatar mana samun nasara."
Daqyar su kojo suka rarrafo gurinsa suka rungume juna cikeda tsoron rabuwa da juna saidai burinsu ya zarce komai.
Daqyar suka rabu da juna yana rangaji yana faduwa yana tashi sbd yunwa,zafi da qishirwa dake neman lahantasu ya nausa dajin inda ranar suka fara ganinta baisan inama yake jefa qafafunsa ba sbd azabar dayake ji cikin hanjinsa da cikinsa.
Duhun dare nayi yana isa gurin saidai ba'a cikin hayyacinsa ba sbd tuni yafara ficewa hayyacinsa atake ya yanke jiki gurin yafadi yana fitarda numfashi daqyar.
Ahankali kunnuwansa suka fara jiyo amo da sautin sarqar zinarin qafarta sanye take cikin kaya ruwan makuba fuskarta na fitarda wani irin annuri duk da cikin duhune atake yaji wani sanyi na yaye masa yunwa da wahalarsa suna barinsa ahankali.
Cikin wani irin takun nutsuwa da wata irin haiba ta nufo hanyar taku kadan tayi ta tsaya cak tareda lumshe fararen kyawawan idanuwanta.
A hankali ta juyar da kanta tahangosa kwance ba alamar yana numfashi.
A hankali takalli jikinta ahankali ta rikide ta sauya zuwa wata kyakkyawar bafulatar baqar Ethiopia sarqoqin jikinta na zinari suka koma duwatsun dandaye masu qaramin kyau ta nufosa numfashinta na wani irin sarqewa sbd wannan shine karo na farko data taba ganin wani biladama wadda take tabbarda shine Wanda ta dibi shekaru da qarnika tana jira.
A hankali ta durqusa gabansa tareda daga daga dogon hannunta ta ta6a goshinsa atake ya bude idanuwansa yana kallon fuskarta bai san lokacin da ya sume ba,
ruwan dake cikin goranta ta fulanin daji ta ɗauka ta watsa mishi, a hankali ya buɗe idanunshi sai akan fuskarta.
Cikin idanunta ya kalla kamar wanda aka ɗiga mishi ruwan gold, lumshe idanunshi yayi.
"Sannun ko" tace mishi...
Wani irin sauti yaji daga muryarta wanda yakusan sake sumar dashi yayi wani irin jarumtar daidaita numfashinsa da nutsuwarsa yayi kalar wanda ke cikin tsananin wuya ya daga mata kai daqyar alamar amsawa yana jan numfashin qarya daqyar.
Kasa wata maganar tayi tasauke kai tana kallon qafafunsa dake cikin takarmin fatar damisa.
Sunkuyar da kanshi yayi ahankali kwalla na zuba daga idanunshi cikin muryar tsananin damuwa da baqin ciki rayuwa yace.
"Me yasa kika taimakeni?
me yasa baki barni na mutu ba? na gaji da rayuwar duniya gwara na mutu nabar duniyar nan."
Kallonsa tayi cikin sauri da nutsuwa da laushin murya tace,
"Koma Ya-yane dai rayuwarka tana da amfani,
ka daina cire tsamani da rayuwa, dan ko badaɗe ko bajima zaka amfani rayuwarka tana da amfani."
Kuka ya fashe da shi yans kwaɗa kanshi da bishiya yana cewa,
"Kaicon rayuwa dan ina maraya shine bazanyi rayuwa kamar kowa, gwara mutuwata."
Duk ya jiwa kanshi ciwo,
tausayinshine da mamakin bil adamane ya kamata musamman ace yaganta mace cikin wannan dajin da tsakar dare amma bai nuna shakku ko tsoro da fargaba ba kodai yasan da fitowartane?
Satar kallonta yayi yaga alamar tunani da nazarinsa takeyi yasan dole yayi dubarar hanata zarginsa hadiye wani mugun yawu tareda zabura gefe jikinsa na wani irin mazari ya nunata da hannunsa dake mugun rawa a tsorace da rawar murya yace,
Ke...keee...ke wacece?
Me...mee kikeyi anan ke daya?
Kallonsa tayi ahankali cikin nutsuwa ganin yanda yarude yake neman zaucewa atake tasaki numfashi mai Sanyi tasaki murmushin daya sakasa zubewa kan gwiwoyinsa.
cikin sanyi murya tace.
"Nima marainiyace kiwo yakawoni kusadanan 6atan hanya yasakani shigowa nan hanyata nake nema amma nakasa ganewa.
Cikin dubara yayi baya alamar tsoro ya buga kansa da bishiya sosai nan take yafadi Jini na fita goshinsa.
Hannu ta daga ahankali zata shafa ciwon danya warke ta dakata sbd karya sake tsorata idan ya farko.
Tashi tayi ta fara niman ganyayyaki tashiga haɗa mishi magani, tasaka mishi a ciwon,
Sun ɗauki kwanaki biyu a gurin tana kula dashi, tun ranar da duka haɗu sukayi magana bata ce mishi kome ba, tsakaninta dashi ido duk abinda majinyaci ke bukata take mishi. Zaman kuramen da suke ba karamin, haifar musu da wani shakuwa yayi ba, dan zata zauna a fakaice tana kallonshi, ko shi yayita kallonta, da zaran sun kama juna take kowanensu zai shiga kame kame, ba yanayin da suke yana tafiya da wani irin tsari na musaman,
Jakarsa ta kaya ya bude ya buga tantin rumfarsa itace take kwana aciki shikuma yana kwanciya da wajen.
. . A hankali suke iya faɗawa junansu magana ko kuma hira sama sama, a wata safiya ya tashi ya zauna dake ciwon jikinshi ya warke yace mata.
"Zan koma cikin gari, amma baki faɗa min sunanki ba, ni dai sunana Jamal ni maraya ne, zanje sake komawa gurin dangin iyayena dana gujewa.
Kura mishi ido tayi cikin nutsuwa tace,
"Nima marainiya ce bani da kowa,sai kai da na haɗu da kai gashi zaka tafi kabarni Sunana Mineelik."
Wani irin bugawa qirjinsa yayi sbd ambatar sunan kawai musamman duka kwanakin yayisu ne babu ko kyaftawar ido bare bacci sbd yasan rayuwarsa na tsakanin mutuwa da rayuwane idan yabari yayi kuskure dan qanqani taganosa.
Cikin tausayawa yace.
Bakyason nabarki cikin dajin nan ne na zauna?
"Zanyi fatar haka idan ta kasance amma bazan maka dole ba." tace mishi.
Shiru sukayi, suka cigaba da satar kallon juna, a hankali shakuwar da sukewa juna ta sake samun matsaya na musaman ma inda ta rikiɗe ta koma soyayya mai matukar ɗaukar hankali, tare suke farautar abinda zasu ci, idan zatayi wani abu zama yake ya kareta, gabaki ɗaya jamal ya sadaukar da lokacinsa sabida ita,, musaman suke zama suyita hira da zaran yaga ta fara alamun jin barci zai barta ta shiga ta kwanta yana gadinta.
Tausayinsa ne mai tsanani yashiga rayuwarta sbd kaf baida abinda yake sai kulada ita tamkar sarauniya duk da baisan wacece itaba tabbas zata taimaki rayuwarsa kodan soyayyarsa data ginu a zuciyarta.
#mamuhgee
_*TARAYYA*_
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association💡_
*37*
_Not edited_
_a gaggauce_
Haske writers association
Shiru tayi tana kallonshi cikin nutsuwa, ta rasa ta inda zata fara taimakonshi satar kallonta yayi cikin nutsuwa, sannan ya sauke numfashi yace.
Rayuwarsu a dajin wani irin rayuwa ce, mai ɗauke da soyayya da wani irin kulawa ba daga itaba har zuwa ita kanta. Mafi lokuta takan zauna tayita tunani anya ba wani kuskure bane yake shirin afkuwa na amincewa bil'adam, sai wani ɓangare na zuciyarta ya tuno mata tarin alkhairin da Jamal yake mata,
Wani lokaci suna zaune ta kalleshi, a nutse kafin tace,
"Menene silar barowarka daga gida ka shigo wannan dajin har kake tunanin kashe kanka da rayuwarka."
Kirjinshine ya bada wani irin sauti, kura mata ido yayi yana qoqarin qin barinta gano yanayin daya shiga cikin daidaita nutsuwa sai ya sunkuyar da kanshi cikin nuna baqin ciki yace,
Idan kika san abinda ya baroni da dangina sai kema kin gujeni, labarina ba labari bane sbd cike yake da bakin ciki.
Dafe goshinshi yayi yana dauke kai yana girgizawa cikin damuwa mai tsanani sannan ya cigaba da cewa,
"Idan kika san koni waye guduna zakiyi gwara mubar maganar haka dan babu alkhairi a ciki.
Wani irin qayataccen murmushi tasaki cikin qasaitar mulkinta dabatamasan tayiba tace,
Kayi min halacci zama tareda ni kana kula dani tamkar nauyina yana rataye akanka dan haka bazan gujekaba fadamin.
Girgiza kai ya cigaba dayi yana cewa,
Karki so jin waye ni, karki so jin waye ni, labarina cike yake da kayan haushi da bakin ciki.
"Ko baka yarda dani bane, dan idan ka yarda dani ai babu abin bakin ciki a jin kai waye saima karin amintaka a cikin zamanmu.
Gyara zama yayi zuciyarsa cike fal da farin ciki dan abinda zai fada mata shine matakin nasararsu.
"Kamar yanda na faɗa miki ni marayane bani da uwa bani da uba, amma akwai kawunaina, kasancewar iyayena sun mutu basu bar min ko 'dayaba koda kuwa kaza ce yasa na zama abin tsangwama a cikin mutane, sannu a hankali na fara niman nawa na kaina sai dai...
"Ajaniiiiiiiiiii"
D'auke numfashinsa yayi cak, tsabar tsoron, haka aka kewayasu ana razanasu.
Wasa wasa sai da suka kwashi fiyye da wata biyar ana tsoratasu da abubuwa a gurin tuni suka saba da rayuwa adajin sbd dama dukkaninsu sunsaba da rayuwa a daji dan haka yanzu gida suka dauki dajin sbd burinsu abune dazasu iya komai akansa.
lokacin da suka cika wata shida Ajani yaje ya faɗawa boka abinda ya faru, nan ya zauna ya faɗa mishi abinda zasuwa Mineelik dazaran ta faɗa soyayya da Jamal. Bokan ya cigaba da cewa,
" Matuƙar mukace muna son dukiyar baxata bamu cikin lumana ba. Karshe rabaku xatayi da ɗan uwanku amma idan mukayi haka toh babu wata damuwa sannan zan nema muku abubuwan da zakuyi amfani dashi, karka bari ɗan uwanka yaji labarin dan matukar yaji bazai yarda yayi aikin ba."
Gyaɗa kai ajani yayi sannan yabar garin ya koma dajin, nan suka cigaba da zama ga tsoratasu da ake ga kwanakin kamar baya tafiya, duk sun kaqu da faruwan haka,
Da zaran sun zauna hiransu kenan, akan yanda zasu juya dukiyarsu da suka samu, daga gareta, a hankali lokacin yana tafiya wasa wasa sai gashi har saura kwanaki bakwai zata bayyana,
......
Bayan kwana huɗu wata rana da safe suka tashi da mugun faɗa kaman zasu kashe junarsu, kaman dai yanda bokan ya faɗa musu, karshe rabuwa dasu Jamal yayi ya koma gefe dan ya hassaso wannan rigimar yana cikin alamomin bayyanarta nan yatunatar dasu nan kowa yayi nesa da 'dan uwansa suna fidda wani irin gumi najin wani irin qarfi mai razanarwa na son kashe dan uwansa.
rana tabiyu kuwa sun tashi da babu giftawar tsuntsaye ko ɗaya tareda wani irin tsoro mai firgitarwa dayake shigarsu wanda suka tabbarda natane amma haka suka dinga daurewa cikin wata irin jarumta.
Rana mafi tashin hankali shine ranar bayyanarta tsananin zafin da ake yaja sukaita fad'uwa, gashi sun shanye ruwansu, dakyar Jamal ya mike yace.
"Yaku Y'an uwana wannan itace rana mafi hadari ageremu saidai ina fatar mana samun nasara."
Daqyar su kojo suka rarrafo gurinsa suka rungume juna cikeda tsoron rabuwa da juna saidai burinsu ya zarce komai.
Daqyar suka rabu da juna yana rangaji yana faduwa yana tashi sbd yunwa,zafi da qishirwa dake neman lahantasu ya nausa dajin inda ranar suka fara ganinta baisan inama yake jefa qafafunsa ba sbd azabar dayake ji cikin hanjinsa da cikinsa.
Duhun dare nayi yana isa gurin saidai ba'a cikin hayyacinsa ba sbd tuni yafara ficewa hayyacinsa atake ya yanke jiki gurin yafadi yana fitarda numfashi daqyar.
Ahankali kunnuwansa suka fara jiyo amo da sautin sarqar zinarin qafarta sanye take cikin kaya ruwan makuba fuskarta na fitarda wani irin annuri duk da cikin duhune atake yaji wani sanyi na yaye masa yunwa da wahalarsa suna barinsa ahankali.
Cikin wani irin takun nutsuwa da wata irin haiba ta nufo hanyar taku kadan tayi ta tsaya cak tareda lumshe fararen kyawawan idanuwanta.
A hankali ta juyar da kanta tahangosa kwance ba alamar yana numfashi.
A hankali takalli jikinta ahankali ta rikide ta sauya zuwa wata kyakkyawar bafulatar baqar Ethiopia sarqoqin jikinta na zinari suka koma duwatsun dandaye masu qaramin kyau ta nufosa numfashinta na wani irin sarqewa sbd wannan shine karo na farko data taba ganin wani biladama wadda take tabbarda shine Wanda ta dibi shekaru da qarnika tana jira.
A hankali ta durqusa gabansa tareda daga daga dogon hannunta ta ta6a goshinsa atake ya bude idanuwansa yana kallon fuskarta bai san lokacin da ya sume ba,
ruwan dake cikin goranta ta fulanin daji ta ɗauka ta watsa mishi, a hankali ya buɗe idanunshi sai akan fuskarta.
Cikin idanunta ya kalla kamar wanda aka ɗiga mishi ruwan gold, lumshe idanunshi yayi.
"Sannun ko" tace mishi...
Wani irin sauti yaji daga muryarta wanda yakusan sake sumar dashi yayi wani irin jarumtar daidaita numfashinsa da nutsuwarsa yayi kalar wanda ke cikin tsananin wuya ya daga mata kai daqyar alamar amsawa yana jan numfashin qarya daqyar.
Kasa wata maganar tayi tasauke kai tana kallon qafafunsa dake cikin takarmin fatar damisa.
Sunkuyar da kanshi yayi ahankali kwalla na zuba daga idanunshi cikin muryar tsananin damuwa da baqin ciki rayuwa yace.
"Me yasa kika taimakeni?
me yasa baki barni na mutu ba? na gaji da rayuwar duniya gwara na mutu nabar duniyar nan."
Kallonsa tayi cikin sauri da nutsuwa da laushin murya tace,
"Koma Ya-yane dai rayuwarka tana da amfani,
ka daina cire tsamani da rayuwa, dan ko badaɗe ko bajima zaka amfani rayuwarka tana da amfani."
Kuka ya fashe da shi yans kwaɗa kanshi da bishiya yana cewa,
"Kaicon rayuwa dan ina maraya shine bazanyi rayuwa kamar kowa, gwara mutuwata."
Duk ya jiwa kanshi ciwo,
tausayinshine da mamakin bil adamane ya kamata musamman ace yaganta mace cikin wannan dajin da tsakar dare amma bai nuna shakku ko tsoro da fargaba ba kodai yasan da fitowartane?
Satar kallonta yayi yaga alamar tunani da nazarinsa takeyi yasan dole yayi dubarar hanata zarginsa hadiye wani mugun yawu tareda zabura gefe jikinsa na wani irin mazari ya nunata da hannunsa dake mugun rawa a tsorace da rawar murya yace,
Ke...keee...ke wacece?
Me...mee kikeyi anan ke daya?
Kallonsa tayi ahankali cikin nutsuwa ganin yanda yarude yake neman zaucewa atake tasaki numfashi mai Sanyi tasaki murmushin daya sakasa zubewa kan gwiwoyinsa.
cikin sanyi murya tace.
"Nima marainiyace kiwo yakawoni kusadanan 6atan hanya yasakani shigowa nan hanyata nake nema amma nakasa ganewa.
Cikin dubara yayi baya alamar tsoro ya buga kansa da bishiya sosai nan take yafadi Jini na fita goshinsa.
Hannu ta daga ahankali zata shafa ciwon danya warke ta dakata sbd karya sake tsorata idan ya farko.
Tashi tayi ta fara niman ganyayyaki tashiga haɗa mishi magani, tasaka mishi a ciwon,
Sun ɗauki kwanaki biyu a gurin tana kula dashi, tun ranar da duka haɗu sukayi magana bata ce mishi kome ba, tsakaninta dashi ido duk abinda majinyaci ke bukata take mishi. Zaman kuramen da suke ba karamin, haifar musu da wani shakuwa yayi ba, dan zata zauna a fakaice tana kallonshi, ko shi yayita kallonta, da zaran sun kama juna take kowanensu zai shiga kame kame, ba yanayin da suke yana tafiya da wani irin tsari na musaman,
Jakarsa ta kaya ya bude ya buga tantin rumfarsa itace take kwana aciki shikuma yana kwanciya da wajen.
. . A hankali suke iya faɗawa junansu magana ko kuma hira sama sama, a wata safiya ya tashi ya zauna dake ciwon jikinshi ya warke yace mata.
"Zan koma cikin gari, amma baki faɗa min sunanki ba, ni dai sunana Jamal ni maraya ne, zanje sake komawa gurin dangin iyayena dana gujewa.
Kura mishi ido tayi cikin nutsuwa tace,
"Nima marainiya ce bani da kowa,sai kai da na haɗu da kai gashi zaka tafi kabarni Sunana Mineelik."
Wani irin bugawa qirjinsa yayi sbd ambatar sunan kawai musamman duka kwanakin yayisu ne babu ko kyaftawar ido bare bacci sbd yasan rayuwarsa na tsakanin mutuwa da rayuwane idan yabari yayi kuskure dan qanqani taganosa.
Cikin tausayawa yace.
Bakyason nabarki cikin dajin nan ne na zauna?
"Zanyi fatar haka idan ta kasance amma bazan maka dole ba." tace mishi.
Shiru sukayi, suka cigaba da satar kallon juna, a hankali shakuwar da sukewa juna ta sake samun matsaya na musaman ma inda ta rikiɗe ta koma soyayya mai matukar ɗaukar hankali, tare suke farautar abinda zasu ci, idan zatayi wani abu zama yake ya kareta, gabaki ɗaya jamal ya sadaukar da lokacinsa sabida ita,, musaman suke zama suyita hira da zaran yaga ta fara alamun jin barci zai barta ta shiga ta kwanta yana gadinta.
Tausayinsa ne mai tsanani yashiga rayuwarta sbd kaf baida abinda yake sai kulada ita tamkar sarauniya duk da baisan wacece itaba tabbas zata taimaki rayuwarsa kodan soyayyarsa data ginu a zuciyarta.
#mamuhgee
_*TARAYYA*_
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association💡_
*37*
_Not edited_
_a gaggauce_
Haske writers association
Shiru tayi tana kallonshi cikin nutsuwa, ta rasa ta inda zata fara taimakonshi satar kallonta yayi cikin nutsuwa, sannan ya sauke numfashi yace.
Rayuwarsu a dajin wani irin rayuwa ce, mai ɗauke da soyayya da wani irin kulawa ba daga itaba har zuwa ita kanta. Mafi lokuta takan zauna tayita tunani anya ba wani kuskure bane yake shirin afkuwa na amincewa bil'adam, sai wani ɓangare na zuciyarta ya tuno mata tarin alkhairin da Jamal yake mata,
Wani lokaci suna zaune ta kalleshi, a nutse kafin tace,
"Menene silar barowarka daga gida ka shigo wannan dajin har kake tunanin kashe kanka da rayuwarka."
Kirjinshine ya bada wani irin sauti, kura mata ido yayi yana qoqarin qin barinta gano yanayin daya shiga cikin daidaita nutsuwa sai ya sunkuyar da kanshi cikin nuna baqin ciki yace,
Idan kika san abinda ya baroni da dangina sai kema kin gujeni, labarina ba labari bane sbd cike yake da bakin ciki.
Dafe goshinshi yayi yana dauke kai yana girgizawa cikin damuwa mai tsanani sannan ya cigaba da cewa,
"Idan kika san koni waye guduna zakiyi gwara mubar maganar haka dan babu alkhairi a ciki.
Wani irin qayataccen murmushi tasaki cikin qasaitar mulkinta dabatamasan tayiba tace,
Kayi min halacci zama tareda ni kana kula dani tamkar nauyina yana rataye akanka dan haka bazan gujekaba fadamin.
Girgiza kai ya cigaba dayi yana cewa,
Karki so jin waye ni, karki so jin waye ni, labarina cike yake da kayan haushi da bakin ciki.
"Ko baka yarda dani bane, dan idan ka yarda dani ai babu abin bakin ciki a jin kai waye saima karin amintaka a cikin zamanmu.
Gyara zama yayi zuciyarsa cike fal da farin ciki dan abinda zai fada mata shine matakin nasararsu.
"Kamar yanda na faɗa miki ni marayane bani da uwa bani da uba, amma akwai kawunaina, kasancewar iyayena sun mutu basu bar min ko 'dayaba koda kuwa kaza ce yasa na zama abin tsangwama a cikin mutane, sannu a hankali na fara niman nawa na kaina sai dai...