Sashe 4
Tarayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk tsanani asma'u kadaki rabu da hannuna.
'Daga masa kai tayi hawaye na gangarowa idonta.
Dukkanin zuriar gidan sukabi ta qofar baya suka fara gudu suna waiwaye cikin tsoro da tashin hankali suna tsallake gawarwakin wainda aka kashe kwance cikin jini sai gudana yake
Ihun yara da mata tareda na maza saitashi yake ga huta da aka cinnawa wasu bukkokin.
Sun kusan isa bakin ruwa innaje tayi tuntu6e da wata gawa ta fadi tareda sakin wani razanannen ihu tana rawar jiki
Mamani dake bayansu da cikinta itama tayi saurin ra6esu da gudu zata wuce qafar innaje dake qoqarin tashi ta kifarda ita
Bulama cikin tsananin hanzari ya riqosu duka su biyun ya tayar suka wuce da gudu amma sai wani tashin hankalin sukayi arba dashi domin kuwa su kutti da sauran yan gidan sun 6ace musu.
Kallon mamani yayi cikin tsananin tashin hankali yace,
Inane hanyarda baabah yace wadda mu bamu saniba?
Tsabar musiba da tashin hankali ya rudata takasa ganewa sai rarraba idanu take tana tsima cikin kuka.
Fizgarsu yayi suka nufi wata hanya da gudu Dan tsira
Qaddara ta Riga fata sai gashi tsaye turus agaban shugaban qungiyar.
Saurin kallon qasa yayi gaban shirgegen mutumin idanuwansa suka sauka kan gawar baabah kwance cikin jini ga rigarsa harta faraci da wuta.
Bai ankaraba yaji saukar dukan gora atsakiyar kansa ya dafe kai idanuwansa suka rufe ya yanke jiki yafadi agurin.
Suna ganin yanada sauran rai suka jasa aka jefa cikin qaton jirginsu na ruwa hakama innaje da mamani.
Sun samu nasarar kamo mutane zama da sittin maza da mata banda yara suka gargada jirginsu na ruwa suka tafi.
#mamuhgee.
[20/06, 22:50] 80k: *_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_haske writers association_💡
*5*
Saida gari yayi haske sosai yayi tsit su kutti sukaji tsit suka fito daga ma6oyarsu cikeda tsoro da tashin hankalin rashin ganin mamani dasu bulama.
Dakatarda sauran yayi ya ringa bin cikin hakukuwa batareda yana dogon motsiba yaje ya leqo qauyen.
Tsit sai koke koken dake tashi gawarwaki kuwa gasunan kwance
Jini kuwa tuni yake gudana a qauyen dabbobinsuma ba'a bariba shiyasa gawarwakin bana mutumba bana dabba ba.
Saki jikinsa yayi sosai zuciyarsa tayi nauyi yasan tunda su bulama basa taredasu to kuwa sun mutu ko antafi dasu tafiyarda bar abada ba dawowa,
Tafiyarda gwara mutuwa da ita sbd a qasqantaccen bawa zaka qare wasuma kafin akai wahala da azaba tareda yunwa takashesu.
Komawa yayi yana daga qafa da qyar jiri na dibarsa yakirawo sauran suka shigo qauyen babu Mai nutsuwa nansuka fara tsallake gawarwaki suna birkito wainda ke kife suna duba sauran iyalan gidan dabaa ganiba.
Tuni suma wasu daga cikinsu suka fara ihun kuka sbd ganin mazansu wasu kuwa sauran matansu Dan duka iyalan gidan baabah din mazansu da matansu tareda 'yayansu su talatin da takwas ne amma su ashirin da 'daya suka tsira ankashe sha hudu antafi da uku.
Lokacinda suka arba da gawar baabah nan suka qara saddaqarwa nandai akayi kukan daza'ayi aka dangana
Mazan dasuka saura haka aka hada gawarwakin sukaje nesa da qauyen suka rufesu suka dawo kowa yacigaba da rayuwarsa amma kullum cikin fargaba duk da sunsan mutanen bazasu dawo yanxuba sai zuwa nanda shekaru masu Dan tsawo sun kwatanci qauyen yasake cika sosai an hayayyafa yara sungirma sunxama samari da yanmata saisu sake dawowa su kwashe.
Tunda dai suna tsoro haka suka sake sakewa suka cigaba da rayuwa aka nada kutti amatsayin sabon shigaba Wanda wannan karon shi akan hada mugayen makamai na itace da dafin macizai da kunamu yamaida hankali sbd yadauki alqawarin angama satarsu ana siyardasu amatsayin bayi yaqi zasu shirya daga yanxu har ranarda mutanen zasu dawo.
*
Abincin dake cikin jirgin nasu ne iya sukadai suci su qoshi su kama wainda suka kamo suyita duka ba ruwansu da namiji ba ruwansu da mace ga yunwa sunbarsu da ita ga qishirwa tuni wasu daga cikinsu suka fara macewa sbd muguwar tafiyace mai nisa dazata kaisu nahiyar da
MENEELIK PALACE take
Duk Wanda ya mutu ruwa kawai suke jefasa ahaka mutanen suka rage da damansu.
Kwanansu goma sha bakwai ajirgin ruwar kafin suka isa da sassafe.
Cikin mutane sittin da 'yan kai dasuka kamo mutane arba'in kawai suka iso dasu daga qauyensu bulama sauran duk sun mutu ahanya.
Bayan 'yan qauyensu bulama dama sunsato wasu daga gurare da dama.
Kamar kayan wanki haka aka gargadosu dukkaninsu hannuwansu a 'daure kusan da igiya 'daya sbd ajere suke.
Babu Wanda zaka kalla kaga kamar baikusa mutuwaba sbd babu Wanda yake iya tsayuwa daidai sbd wahala da yunwa ga dau'da data canza musu kamanni mamani tuni kuka ya qare zuciya ta qafe banda tsanarsu asma'u ba abinda takeji sbd ganin sune sanadin zuwanta nan ga cikin jikinta haryafi na asma'u fitowa.
Bulama duk wuya da azaba asma'u yakeji itada mamani sbd ganin dukkaninsu juna biyune dasu gasu mata.
Kukansa da fargabarsa karsu mutu kafin a iso
Basu mutuba amma dai suna kusa sbd babu mai iya jan qwaqwaran numfashi acikinsu.
A inda suke baza hajar siyarda bayinsu suka xubesu nansuka rarrabu cikin mutanen dake cikeda kasuwar Dan kar agansu da yawa dakuma kalar marasa imani agane satosu sukayi ba bayi bane babbansu tareda manyan yaransa uku suka isa gurin wani mai siyarda 'yayan itatuwa suka zauna sunacin abinci cikin farin ciki da nutsuwa.
Asma'u ce ta yanke jiki ta fadi da 'dayansu ya lura yamiqe da sauri tareda yiwa ogan nuni da sauri shima ya miqe suka isa gurinta
Bulama tuni yafashe da wani irin kuka sbd yasan mutuwa tayi.
Ta6ata sukayi arikice 'dayan cikin wani yare mara dadin ji yace,
Tanada rai yunwa da wahalace muyi saurin bata abinci karta mutu kasan dokace anan duk mai siyarwa da masarauta bayi yazo dasu suka mutu aka gano wahalace kashesa shima akeyi musamman mu da satosu mukayi idan sultan dinsu yaji yankamu za'ayi abawa zakunansa namanmu.
Yawun tsoro ogan ya hadiye sbd yasan atarihin sarkin fiyedama hakan zai iyayi musu ba abin suqarasa kashetaba basuda gurin 6oye gawarta ko yarwa batareda angansuba sbd tsantsar tsaro da qa'idojin da sultan din nahiyar yake bayarwa.
Da ido yayiwa yaran alama suka kwanceta tareda fakar idanun mutane suka koma can baya da ita suka siyo mata abinci da ruwa kafin suka kelaya mata ruwa ta bude ido daqyar tanajan numfashin wahala.
Miqa mata abincin sukayi hannu na rawa ta kar6a daqyar take saita hannunta yashiga bakinta
Nan take ta cinye abincin tanashan ruwa sai amai.
Amai tayi sosai wainda yasata matuqar galabaita nantake zazzabi mai qarfi yafarasa jikinta karkarwa.
Damqo gashinta ogan yayi 6acin rai da takaicin sbd ita rayuwarsu na cikin ha'dari ya bude jajayen idanuwansa sosai yace,
Idan baki saki jiki kin nuna lafiyarki kalauba zan yanka mijinki agabanki na qona namansa nazuba tokarsa a takarda Nayi sigari dashi.
Marinta yayi da qarfi saidata kifa cikin qasa qasa da murya yace,
Kingane?
Bakinta dake jini ta goge hannu na rawa ta 'daga kai idanuwanta na qara rinewa da Jan axaba.
Ingiza qeyarta yayi ta fadi ta lalaba ta miqe da qyar suka koma gurin sauran bayin.
Bulama na hangota gabansa yayi mummunan faduwa ya sunkuyar dakai tareda sakin sabbin hawayen baqin ciki sbd hango jini abakinta duk da tana gogewa
Tafiyarma sai ha'da hanya takeyi a wahalce amma haka take daurewa sbd bin umarninsu karsu kashe bulama.
Sai da rana ta fadi suna aje cikin rana baci hargwara ruwa yau anbasu ganin mutane akasuwar gashi suna tsoron akwai 'yan rahoton sultan
yamma tayi sosai suntabbatarda lokacin sultan ke shaqatawa tareda 'dansa namiji qwaya 'daya tal a gurin shan iskansa dake cikin masarautarsa kuma alokacin ake bada damar kai bayi sbd kullum masarautar bata gajiya da siyan bayi sbd girma da ikonta.
Isarsu masarautar yayi daidai da fitowar yarima MAHEER IBN ABDULSHAMS tareda abokinsa KHALEEFA ABDALLAH 'Dan wazirin sultan 'yan kimanin shekaru goma sha biyu biyu sun fito daga sassan hutawar sultan fadawan hudu na bayansu zasu gurin baturen malaminsu dayazo koyardasu karatu.
Kallo 'daya yarima yayiwa sashen daduke ana gargadasu zuwa sashen koyarda bayi aiki ya 'dauke kai
Khaleefa kuwa tsayawa yayi yana kallonsu yace,
Idan nagirma zansiyawa ummyna bayinda harsu mutu suna kularmin da ita.
Tsayawa yarima yayi cak tareda juyowa jin abinda khaleefa yace yasa yatuno da alqawarin dayayiwa ammynsa yauda safe cewar zai mata kyautarda mutuwace kawai zata rabata da ita sai kawai yace atsayar masa sa bayin.
Cikin hanxari aka tsayar dasu batareda ya kalli gefensuba yace abashi namijin qarshe da macen qarshe ya siya amafi tsadar farashi.
Jiki na rawa aka janyo bulama da asma'u dake baya aka kawosu gabansa amma daga nesa sbd warin dau'da.
Still basu yake kalloba sbd iko da mulki na jinin mahaifinsa dake yawo jikinsa yace,
Akaisu ke6antaccen guri a tsaftacesu abasu abinci da suturu kyautace zanyiwa mahaifina da ammynah akaro na farko.
Yana fada ta wuce khaleefa yabisa yana tunanin siyawa nasa iyayen amma zaibari sai ansake kawo wasu bayin.
Sukuwa dasuka kawo bayin maqudan kudaden qasar akabasu cikeda jaka suka karbe abinsu suka juya suna isa kasuwa suka siya guzurin abinci mai yawanda zai ishesu suyi wata qasar safaro wasu sudawo su sake siyarwa.
Lokacinda aka ke6esu bulama aka tsaftacesu tsaf aka basu watadaccen abinci mai kyau sukaci nantake suka 'Dan murmure sukai fasali aka fito dasu aka nufi Sashen da sultan da iyalensa kowa keda part.
Kallonta bulama yayi idanuwansa taf da halayen tausayin gararinda rayuwarsu da abinda zasu haifa sbd tasake shiga,
Tasu qaddarar ahaka take daga 'yaya masu gata da dukiya sunkoma wasu mutane masu wani yaren dabam agarinsu baabah yanxu kuwa zasu zamo wasu bayi masu bauta kuma iyayenda zasu haihu su haifarwa iyayen gidansu wani bawan ko wata baiwar.
Itama kallonsa take da ido jajir sbd sanin daganan rayuwarsu amatsayin ma'aurata ta tsaya takuma wargaje sbd ikon ganin junaba basudashi yanxu bare kebewa kosunga juna iyakarsu satar kallo ko ikon magana basudashi.
Ahankali aka jasa aka shige dashi babban palon sultan cikin tsananin biyayya 'Dan Aiken yarima ya zube yace,
Allah yaqarawa sultan yawan rai da lafiya tareda qarfin mulki,
Ga babbar kyauta ta musamman daga yarima.
Kallon bawan yayi tareda sakin wani kyakkyawan qasaitaccen murmushi kafin yakalli 'dan aiken yakalli saikin gida yace,
'Daga masa kai tayi hawaye na gangarowa idonta.
Dukkanin zuriar gidan sukabi ta qofar baya suka fara gudu suna waiwaye cikin tsoro da tashin hankali suna tsallake gawarwakin wainda aka kashe kwance cikin jini sai gudana yake
Ihun yara da mata tareda na maza saitashi yake ga huta da aka cinnawa wasu bukkokin.
Sun kusan isa bakin ruwa innaje tayi tuntu6e da wata gawa ta fadi tareda sakin wani razanannen ihu tana rawar jiki
Mamani dake bayansu da cikinta itama tayi saurin ra6esu da gudu zata wuce qafar innaje dake qoqarin tashi ta kifarda ita
Bulama cikin tsananin hanzari ya riqosu duka su biyun ya tayar suka wuce da gudu amma sai wani tashin hankalin sukayi arba dashi domin kuwa su kutti da sauran yan gidan sun 6ace musu.
Kallon mamani yayi cikin tsananin tashin hankali yace,
Inane hanyarda baabah yace wadda mu bamu saniba?
Tsabar musiba da tashin hankali ya rudata takasa ganewa sai rarraba idanu take tana tsima cikin kuka.
Fizgarsu yayi suka nufi wata hanya da gudu Dan tsira
Qaddara ta Riga fata sai gashi tsaye turus agaban shugaban qungiyar.
Saurin kallon qasa yayi gaban shirgegen mutumin idanuwansa suka sauka kan gawar baabah kwance cikin jini ga rigarsa harta faraci da wuta.
Bai ankaraba yaji saukar dukan gora atsakiyar kansa ya dafe kai idanuwansa suka rufe ya yanke jiki yafadi agurin.
Suna ganin yanada sauran rai suka jasa aka jefa cikin qaton jirginsu na ruwa hakama innaje da mamani.
Sun samu nasarar kamo mutane zama da sittin maza da mata banda yara suka gargada jirginsu na ruwa suka tafi.
#mamuhgee.
[20/06, 22:50] 80k: *_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_haske writers association_💡
*5*
Saida gari yayi haske sosai yayi tsit su kutti sukaji tsit suka fito daga ma6oyarsu cikeda tsoro da tashin hankalin rashin ganin mamani dasu bulama.
Dakatarda sauran yayi ya ringa bin cikin hakukuwa batareda yana dogon motsiba yaje ya leqo qauyen.
Tsit sai koke koken dake tashi gawarwaki kuwa gasunan kwance
Jini kuwa tuni yake gudana a qauyen dabbobinsuma ba'a bariba shiyasa gawarwakin bana mutumba bana dabba ba.
Saki jikinsa yayi sosai zuciyarsa tayi nauyi yasan tunda su bulama basa taredasu to kuwa sun mutu ko antafi dasu tafiyarda bar abada ba dawowa,
Tafiyarda gwara mutuwa da ita sbd a qasqantaccen bawa zaka qare wasuma kafin akai wahala da azaba tareda yunwa takashesu.
Komawa yayi yana daga qafa da qyar jiri na dibarsa yakirawo sauran suka shigo qauyen babu Mai nutsuwa nansuka fara tsallake gawarwaki suna birkito wainda ke kife suna duba sauran iyalan gidan dabaa ganiba.
Tuni suma wasu daga cikinsu suka fara ihun kuka sbd ganin mazansu wasu kuwa sauran matansu Dan duka iyalan gidan baabah din mazansu da matansu tareda 'yayansu su talatin da takwas ne amma su ashirin da 'daya suka tsira ankashe sha hudu antafi da uku.
Lokacinda suka arba da gawar baabah nan suka qara saddaqarwa nandai akayi kukan daza'ayi aka dangana
Mazan dasuka saura haka aka hada gawarwakin sukaje nesa da qauyen suka rufesu suka dawo kowa yacigaba da rayuwarsa amma kullum cikin fargaba duk da sunsan mutanen bazasu dawo yanxuba sai zuwa nanda shekaru masu Dan tsawo sun kwatanci qauyen yasake cika sosai an hayayyafa yara sungirma sunxama samari da yanmata saisu sake dawowa su kwashe.
Tunda dai suna tsoro haka suka sake sakewa suka cigaba da rayuwa aka nada kutti amatsayin sabon shigaba Wanda wannan karon shi akan hada mugayen makamai na itace da dafin macizai da kunamu yamaida hankali sbd yadauki alqawarin angama satarsu ana siyardasu amatsayin bayi yaqi zasu shirya daga yanxu har ranarda mutanen zasu dawo.
*
Abincin dake cikin jirgin nasu ne iya sukadai suci su qoshi su kama wainda suka kamo suyita duka ba ruwansu da namiji ba ruwansu da mace ga yunwa sunbarsu da ita ga qishirwa tuni wasu daga cikinsu suka fara macewa sbd muguwar tafiyace mai nisa dazata kaisu nahiyar da
MENEELIK PALACE take
Duk Wanda ya mutu ruwa kawai suke jefasa ahaka mutanen suka rage da damansu.
Kwanansu goma sha bakwai ajirgin ruwar kafin suka isa da sassafe.
Cikin mutane sittin da 'yan kai dasuka kamo mutane arba'in kawai suka iso dasu daga qauyensu bulama sauran duk sun mutu ahanya.
Bayan 'yan qauyensu bulama dama sunsato wasu daga gurare da dama.
Kamar kayan wanki haka aka gargadosu dukkaninsu hannuwansu a 'daure kusan da igiya 'daya sbd ajere suke.
Babu Wanda zaka kalla kaga kamar baikusa mutuwaba sbd babu Wanda yake iya tsayuwa daidai sbd wahala da yunwa ga dau'da data canza musu kamanni mamani tuni kuka ya qare zuciya ta qafe banda tsanarsu asma'u ba abinda takeji sbd ganin sune sanadin zuwanta nan ga cikin jikinta haryafi na asma'u fitowa.
Bulama duk wuya da azaba asma'u yakeji itada mamani sbd ganin dukkaninsu juna biyune dasu gasu mata.
Kukansa da fargabarsa karsu mutu kafin a iso
Basu mutuba amma dai suna kusa sbd babu mai iya jan qwaqwaran numfashi acikinsu.
A inda suke baza hajar siyarda bayinsu suka xubesu nansuka rarrabu cikin mutanen dake cikeda kasuwar Dan kar agansu da yawa dakuma kalar marasa imani agane satosu sukayi ba bayi bane babbansu tareda manyan yaransa uku suka isa gurin wani mai siyarda 'yayan itatuwa suka zauna sunacin abinci cikin farin ciki da nutsuwa.
Asma'u ce ta yanke jiki ta fadi da 'dayansu ya lura yamiqe da sauri tareda yiwa ogan nuni da sauri shima ya miqe suka isa gurinta
Bulama tuni yafashe da wani irin kuka sbd yasan mutuwa tayi.
Ta6ata sukayi arikice 'dayan cikin wani yare mara dadin ji yace,
Tanada rai yunwa da wahalace muyi saurin bata abinci karta mutu kasan dokace anan duk mai siyarwa da masarauta bayi yazo dasu suka mutu aka gano wahalace kashesa shima akeyi musamman mu da satosu mukayi idan sultan dinsu yaji yankamu za'ayi abawa zakunansa namanmu.
Yawun tsoro ogan ya hadiye sbd yasan atarihin sarkin fiyedama hakan zai iyayi musu ba abin suqarasa kashetaba basuda gurin 6oye gawarta ko yarwa batareda angansuba sbd tsantsar tsaro da qa'idojin da sultan din nahiyar yake bayarwa.
Da ido yayiwa yaran alama suka kwanceta tareda fakar idanun mutane suka koma can baya da ita suka siyo mata abinci da ruwa kafin suka kelaya mata ruwa ta bude ido daqyar tanajan numfashin wahala.
Miqa mata abincin sukayi hannu na rawa ta kar6a daqyar take saita hannunta yashiga bakinta
Nan take ta cinye abincin tanashan ruwa sai amai.
Amai tayi sosai wainda yasata matuqar galabaita nantake zazzabi mai qarfi yafarasa jikinta karkarwa.
Damqo gashinta ogan yayi 6acin rai da takaicin sbd ita rayuwarsu na cikin ha'dari ya bude jajayen idanuwansa sosai yace,
Idan baki saki jiki kin nuna lafiyarki kalauba zan yanka mijinki agabanki na qona namansa nazuba tokarsa a takarda Nayi sigari dashi.
Marinta yayi da qarfi saidata kifa cikin qasa qasa da murya yace,
Kingane?
Bakinta dake jini ta goge hannu na rawa ta 'daga kai idanuwanta na qara rinewa da Jan axaba.
Ingiza qeyarta yayi ta fadi ta lalaba ta miqe da qyar suka koma gurin sauran bayin.
Bulama na hangota gabansa yayi mummunan faduwa ya sunkuyar dakai tareda sakin sabbin hawayen baqin ciki sbd hango jini abakinta duk da tana gogewa
Tafiyarma sai ha'da hanya takeyi a wahalce amma haka take daurewa sbd bin umarninsu karsu kashe bulama.
Sai da rana ta fadi suna aje cikin rana baci hargwara ruwa yau anbasu ganin mutane akasuwar gashi suna tsoron akwai 'yan rahoton sultan
yamma tayi sosai suntabbatarda lokacin sultan ke shaqatawa tareda 'dansa namiji qwaya 'daya tal a gurin shan iskansa dake cikin masarautarsa kuma alokacin ake bada damar kai bayi sbd kullum masarautar bata gajiya da siyan bayi sbd girma da ikonta.
Isarsu masarautar yayi daidai da fitowar yarima MAHEER IBN ABDULSHAMS tareda abokinsa KHALEEFA ABDALLAH 'Dan wazirin sultan 'yan kimanin shekaru goma sha biyu biyu sun fito daga sassan hutawar sultan fadawan hudu na bayansu zasu gurin baturen malaminsu dayazo koyardasu karatu.
Kallo 'daya yarima yayiwa sashen daduke ana gargadasu zuwa sashen koyarda bayi aiki ya 'dauke kai
Khaleefa kuwa tsayawa yayi yana kallonsu yace,
Idan nagirma zansiyawa ummyna bayinda harsu mutu suna kularmin da ita.
Tsayawa yarima yayi cak tareda juyowa jin abinda khaleefa yace yasa yatuno da alqawarin dayayiwa ammynsa yauda safe cewar zai mata kyautarda mutuwace kawai zata rabata da ita sai kawai yace atsayar masa sa bayin.
Cikin hanxari aka tsayar dasu batareda ya kalli gefensuba yace abashi namijin qarshe da macen qarshe ya siya amafi tsadar farashi.
Jiki na rawa aka janyo bulama da asma'u dake baya aka kawosu gabansa amma daga nesa sbd warin dau'da.
Still basu yake kalloba sbd iko da mulki na jinin mahaifinsa dake yawo jikinsa yace,
Akaisu ke6antaccen guri a tsaftacesu abasu abinci da suturu kyautace zanyiwa mahaifina da ammynah akaro na farko.
Yana fada ta wuce khaleefa yabisa yana tunanin siyawa nasa iyayen amma zaibari sai ansake kawo wasu bayin.
Sukuwa dasuka kawo bayin maqudan kudaden qasar akabasu cikeda jaka suka karbe abinsu suka juya suna isa kasuwa suka siya guzurin abinci mai yawanda zai ishesu suyi wata qasar safaro wasu sudawo su sake siyarwa.
Lokacinda aka ke6esu bulama aka tsaftacesu tsaf aka basu watadaccen abinci mai kyau sukaci nantake suka 'Dan murmure sukai fasali aka fito dasu aka nufi Sashen da sultan da iyalensa kowa keda part.
Kallonta bulama yayi idanuwansa taf da halayen tausayin gararinda rayuwarsu da abinda zasu haifa sbd tasake shiga,
Tasu qaddarar ahaka take daga 'yaya masu gata da dukiya sunkoma wasu mutane masu wani yaren dabam agarinsu baabah yanxu kuwa zasu zamo wasu bayi masu bauta kuma iyayenda zasu haihu su haifarwa iyayen gidansu wani bawan ko wata baiwar.
Itama kallonsa take da ido jajir sbd sanin daganan rayuwarsu amatsayin ma'aurata ta tsaya takuma wargaje sbd ikon ganin junaba basudashi yanxu bare kebewa kosunga juna iyakarsu satar kallo ko ikon magana basudashi.
Ahankali aka jasa aka shige dashi babban palon sultan cikin tsananin biyayya 'Dan Aiken yarima ya zube yace,
Allah yaqarawa sultan yawan rai da lafiya tareda qarfin mulki,
Ga babbar kyauta ta musamman daga yarima.
Kallon bawan yayi tareda sakin wani kyakkyawan qasaitaccen murmushi kafin yakalli 'dan aiken yakalli saikin gida yace,