← Book details Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 71

Sashe 44

Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hajja tace"to jeki dauka ki siyo, kudin bironki da'aka siyar ma mamuda fili yasiya miki dashi,Sai Dan gyare-gyare da'aka yi mana a gidan, yace idan aurenki da inusa yatashi Sai asiyar ayi hidimar biki dashi "

Dan qaramin bakinta ta turo gaba ta juya tana Hararar Hajja, cikin lallashi Hajja tace"to uwar masifa, tashi kije Dan Allah, kibiya gidan qawar ki Walida saita rakaki, tunda batasan kinzo Garin ba, kisiyo harda kayan miya, da kaji guda uku, yau Walima zamuyi, jikata tadawo gida"

Cikin murmushi Ummah ta Kalle su, cikin ranta kuwa dadi takeji yanda Hajjan tasaki ranta tadena maganar mutuwa.

******

Sunci tafiya sosai a hanya, Sai yamma suka shigo jigawa, suna kokarin shiga garinsu Aisha mama ta hangi wani Tsoho yana tafiya akan Keke, itace ya'iyo abayan gari, daqyar yake tuqa keken da alama yajigata dayawa,cikin sauri tace"driver tsaya"

Shahaab ya kalleta da mamaki, glass din ta sauke qasa ta kalli wannan tsohon tace"bawan Allah cikin Garin zaka qarasa ne?"

Cikin sauri ya tsaya ya kalleta yace"hakane Hajiya,ciki zan shiga"

Tace"toshigo mota saimu qarasa dakai"

Tsohon ya kalli motar yaga mota Sai sheqi takeyi tana daukar ido, yaji tsoro karyaje Yan yankan kaine, cikin tsoro yace"a a Hajiya, nagode, Aina qaraso ma, nagode sosai"

Murmushi tayi, ta bude Jakarta tad'auki kudi Yan dubu dubu tabashi tace"to ungo wannan kasai itacen dayawa kadena zuwa da kanka"

Jiki na rawa tsohon ya kar6i kudin hannunsa Sai rawa suke, cikin jin dadi tace"nagode Hajiya, Allah yasaka da alkhairi, Allah yahadamu a aljanna mafificiya, ubangiji yabiya miki buqatunki na alkhairi, Allah Yacika miki burinki"

Cikin jin dadi mama tace"Amin ya Allah, kasan ni wacece?"

Tsohon yace"a a Hajiya saikin fada"

Tace"amma ai kasan Mahmud Wakili ko?"

Cikin sauri yace"ranki ya dade duk qasar nan waye zaice baisan Mahmud Wakili ba? Ko baka sanshi a'ido ba ai zaka sanshi a suna"

Murmushi tasake yi tace"toni mahaifiyarsa ce, sunana Aysha Yakubu Sagagi, qawar Aysha Sulaiman Bompai"

Cikin sauri tsohon ya tsugunna yana zuba mata addu'ah, mama tarufe glass din motar suka cigaba da tafiya, Shahaab ya kalleta yayi murmushi tareda Sosa girarsa guda daya, mama kuwa tunanin qawarta Aysha Sulaiman ne yafado mata, rayuwa kenan, yaude gata acikin jigawa Amma batada Hali ko hanyar dazata hadu da qawarta, lokaci daya jikinta yayi Sanyi, tana wannan tunanin batasan har sun qaraso kofar gidan su Aisha ba, Shahaab ya kalleta sannan yace "mama ga gidan Nan munzo"

Kallonsa tayi tace"mekake nufi? Futowa zakayi muje tare dakai kabawa iyayen ta haquri akan abubuwan dasuka faru abaya, Nima nabawa Aisha haquri akan abinda yafaru"

Cikin kunya Shahaab yafuto daga cikin motar, securities sukazo da sauri suna gyara masa babbar rigar jikinsa, aka budewa mama kofa itama tafuto, manyan motocin dasuka tsaya a qofar gidanne suka dauki hankalin Yan qauyen, Wanda suka sanshi Nan da Nan suka fara qus-qus suna nuna shi da hannu anaso a tabbatar Mahmud wakilin daya ta6a aiko musu kayan abinci ne, kokuma wani ne daban?

Wani yaro ne dayazo wucewa mama ta tare tace"shiga Nan gidan kace Ana sallama Dame gidan"

Yaron yajuya yashiga gidan, Sai gashi sun futo daga gidan shida Abba.

Abba yana ganin Shahaab sai mamaki ya wanzu a fuskarsa, cikin mamakin yace"sannunku da zuwa, kamar yalla6ai Mahmud nake Gani ko?"

Shahaab yayi murmushi tareda sunkuyar da Kansa qasa cikin kunya irinta surukai, cikin ransa yana mamakin mahaifin na Aisha ashe ma yaro ne kamar shi,Mama tayi murmushi ganin yanda Shahaab yake sunkuyar dakai tace"kaine mahaifin Aisha?"

Cikin sauri Abba yace"Eh nine Hajiya, sannunku da hanya, nace Allah yasa de ba wani laifin tayi muku tataho gida ba?, mu munata qoqarin zuwa har gida muyi godia akan abun alkhairin da yalla6ai yayi mana Kuma saina ganku kunzo?"

Mama tayi murmushi Tace"A a Aisha batayi laifin komai ba, mune ma mukai laifi mukazo bada haquri, Yaya sunan Kane?"

Cikin murmushi Abba yace"sunana Mamuda Hajiya"

Cikin farinciki mama tace"Mahmud de ko?"
Tanuna masa Shahaab da Kansa yake qasa tace"shima wannan danane, kamar yanda kasani Mahmud Wakili sunansa, Amma Ina kiransa da SHAHAAB..."

gaban Abba ya yanke yafadi, cikin sauri ya kalli Shahaab, cikin daburcewa Shahaab ya russina tareda Bawa Abba hannu yace"Barka da yammah"

Kan Abba gaba daya saiya kulle, dama Shahaab shine Mahmud Wakili? Wannan shi ake kira an yanka tatashi....,kenan shine yake zuwa wajan Aisha? Kuma shine yasake tura Aisha gidansa aiki? Shine yakaishi Umarah, yakai jabir qasar waje karatu?cikin son sake tabbatar wa Yace"Shahaab-shahaab de Danakeji awajan Aisha?"

Shahaab yayi shiru ganin lokaci daya surukin nasa ya d'agoshi, Dan haka yayi saurin yin qasa da Kansa yana 'Dan Sosa qeyarsa.
Mama tayi murmushi tace"shide,idan babu damuwa ka bamu wajan zama Dan maganganu muke tafe dasu dayawa"

Cikin sauri jikin Abba yad'auki rawa, Wai yau Mahmud Wakili ne da Kansa a kofar gidansa, Mahmud Wakili ne yake zuwa wajan 'yarsa,cikeda mamaki yace"a a, to hajiya ku qaraso ciki mana, ku shigo daga ciki kawai..."

Mama Tace"toshikkenan Takwaran Mahmud mushiga"

Abba yajuya cikin gidan da sauri, mama da Shahaab suka doru abayansa.

Hajja tana sunkuye tana gyara hadaddan kunun ayar data zuba acikin fridge, Aisha tana zaune da abinci agabanta tanaci kamar bataso, Ummah tana Gefe da pure water ahannunta tanasha,saiji sukai Abba yana cewa "kushigo Hajiya, ku qaraso, sannunku da zuwa"

Shahaab yana daga Kansa Idonsa ya sauka akan Aisha, tana hada ido dashi gabanta yayanke yafadi, ta tsaya cak tadena cin abincin, yayinda gaban mama ya yanke yafadi ganin fuskar da bazata ta6a mantawa da'itaba a tarihin rayuwar ta,lokaci daya handbag din data riqe a hannun ta tafadi qasa, qaran faduwar jakar ne yasa Hajja tarufe fridge din ta d'ago kanta, gabanta ne yafadi, hannunta yana karkarwa tafara nuna mama,cikin rawar murya tace"Aysha Yakubu?"

Jin sunan data kirane yasa gaba d'ayansu suka maida kallon su ga Hajiya Mama.

Masha Allah, mutara zuwa gobe🙏

Littafin kudi ne, nera 300 kibiya ki karanta kada ki karanta abun Allah ya'isa

0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN

Shedar biya ta wannan number 08033300034

Mutara zuwa gobe🙏🏻

Mrs Usman ce✍🏻

Page 24

Wani Irin hawaye ne yazubo daga idon mama,cikin rawar murya tace"Aysha Sulaiman? Aysha kenake Gani haka kokuma idonane?Dan Allah kifadamin kode irin mafarkan danake yi ne?"
ta qarasa maganar hawaye na gudu daga idanuwanta.

Ahankali Hajja tatako tazo gaban mama, tace"nice Aysha"

Cikin sauri mama ta rungume ta,kuka Hajja tasaki mecin rai, mama kuka, Hajja kuka, cikin kukan Hajja tace"Aysha, ashe da Rabon zan sake ganinki a doron duniya?"

Cikin sauri tasaki mama ta daga hannunta sama tace"ya Allah nagode Maka, Allah Ina qara yima Godiya bisa nunamin qawata dakayi wadda na Dade Ina nema tsawon shekaru masu yawa"

Hajiya Mama ma Hawayen ta share, itama ta daga hannunta kamar de yanda Hajja tayi tace"ubangiji na gode Maka, yau Naga Aysha Sulaiman bompai,Babban burinmu guda daya Yacika, saura Kuma d'ayan, Allah nagode maka"

Cikin sauri Ummah ta goge qwallar idonta, itade batasan wannan baqi ba, Amma duk da babu bayani tariga tasan cewa wannan matar itace qawar Hajja, yaude ga qawar Hajja tazo har gida, ikon Allah kenan, kullum labari-labari yau gashi Allah yahadasu.

Aisha kuwa gabanta ne yafadi, duk wannan dramar dasuke idonta yana kan mama, Tun lokacin da Hajja tace
Aysha Yakubu, daga Nan wani irin shock yakamata, yanzu dama Hajiya Mama itace qawar Hajja?.

Shikuwa Shahaab wata irin wawuyar ajiyar zuciya yasauke Mai karfi,domin kuwa abinda ya lura dashi shine Abban Aisha bashida qanwa mace bare Mama tace dole saiya aure ta Yacika mata burinta, dama abinda yake gudu kenan, mama tadage muddin taga Aysha Sulaiman Tofa Sai sun hada yayansu aure, Kuma Alhamdulillah shi bai taba jin Aisha tace abban ta yanada qanwa ba bare abashi, Gara de ita Aishan, ahakan ma tunda gashinan Allah ya hadashi da Aishan cikin hikimar sa ai shikkenan Shima de dan'uwan burin maman ne, tunda jikar qawarta ce.

Abba kuwa ajiyar zuciya yasaki ahankali, cikin sauri ya goge qwallar Idonsa,sannan yayi gyaran murya yace"Alhamdulillah....,Hajja kuyi hakuri kudena kukan Nan haka, ku qaraso ku zauna"
Yajuya ya kalli Aisha da abincinta ke gabanta ta gagara ci, cikin fada yace"ke tashi ki Dauko babbar tabarmar Nan ki shimfida mana, kinfi awa daya kina cin wannan abincin, ga baqi sunzo ko abun zama baki shimfida musu ba"

Cikin sauri Shahaab yayi qasa da Kansa tareda Sosa qeyarsa
Ummah ta kalli Aisha Tace"Ai inta fara dora abinci a harshe saikace basarakiya, na hanata irin wannan cin abincin taqi ji "

Cikin sauri tatashi ta wuce Dakin Ummah tad'auko babbar tabarmar ta shimfida musu.

Ummah ta kalli su Hajja tace"ku qaraso ku zauna"
Tajuya ta kalli Shahaab da batasan waye shi dinba, ita de taga Sai sunkuyar dakai yake yaqi kallon idon kowa, tace"bawan Allah qaraso mana"

Cikin sauri Shima Abba yace"bissmillah yalla6ai"

Yanda yace yalla6ai dinnan Sai abun yayiwa Shahaab nauyi, ahankali yace"to nagode"

Suka qaraso suka zazzauna a tabarma,Aisha tana daga Gefe, duk jinta take a takure, saboda yanda Shahaab yazuba mata mayun Idonsa, ko tsoron su Ummah su kamashi yana kallon ta ba yayi, duk motsin datayi akan Idonsa.

Hajja ta kalli mama, sannan ta nuna Aisha da hannu tace"kinganta Nan,? Babu abinda tabari naki,masifa,rashin kunya, yanga saikace yar wani, wannan cin abinci dakike a makaranta haka itama takeyinsa kamar kin zauna da'ita kin Koya mata yanda kike yi, lokacin da aka haife ta uban yadage sunana zai saka, nikuma nace a a, munyi alkawarin zamu sakawa Yayanmu Aisha, idan Kuma maza muka haifawa to zamu saka musu suna Mahmud, to Alhamdulillah, Dana guda daya ne a duniya gashinan mamuda, ban haifi mace ba bare nasaka mata sunanki, shiyasa Ana haifar ta daya ce sunana zaisaka nadage nace a a, saide yasaka sunanki, to daqyar de mamuda ya yarda, saboda kallon ta6a66iya sukemim Alokacin, tayaya qawar daban masan inda take ba, bansan a'ina zan ganta ba, zan dage ince sunanta zan saka? To dayake de sunan naki duk irin nawa ne, shine yasa mamuda yasaka mata sunanki,idan masifar ta tatashi fada mukeyi akan wannan suna Nata, fada takeyi tana min sababi kawai natashi nasa mata sunan qawata qilama ta mutu, ban'isa ince tanada masifa ba saitacemin ai nice nace asaka mata sunan qawata, danhaka halin qawata ta Dauko..."
Chapter 44 · 0% Book details