← Book details Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 71

Sashe 42

Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mama tasaki wata irin ajiyar zuciya tace "Alhamdulillah, Allah abun Godia, to tashi kaje kabawa matarka haquri Dan itama anturo mata wannan vedion, kabata haquri ka fahimtar da'ita cewa videon hadawa akayi"

Cikin ladabi ya amsa mata, sannan yatashi yad'auki kayansa, yawuce part dinsa, yana zuwa falonsu yayi sallama tareda shigowa, tana zaune afalon saide ko kallon inda yake batayi ba, cikin zuciyar yace"fishi kan fishi kenan, Dama da fishin company yanzu Kuma ga wani ya qaru"

Murmushi yasakar mata, sannan yace"Bari inzo inyi lallashi"

Munirat ko kallon sa batayi ba,Shima Kai tsaye dakinsa yawuce yana tunanin irin lallashin dazai mata kozai samu yau tasakar masa jikinta yayi yanda yakeso da'ita, saboda a matse yake, kwana biyun Nan kawai yana daurewa ne,yana shiga Dakin yacire kayan jikinsa,dagashi Sai Dan qaramin towel a daure a qugunsa, murd'ad'd'an jikinsa yafuto fili, fatar jikinsa tayi wani irin fresh, lallausan gashi kwance akan faffad'an qirjinsa,yana shirin shiga wanka kenan wayarsa tad'auki qara, dawowa yayi ya zauna abakin gado tareda daukar wayar yayi sallama, daga dayan bangaren akace "Ranka yadad'e sunana Alhaji Umar Amare, nine mamallakin filayen Nan guda biyu danasa afara ginamin Kuma yanzu Yara sun kirani sun fadamin katuro a rushe ginin, shine nace ai babu Wanda baisanka ba a qasar, na bincika nasamu number ka awajan yaronka Auwali, nace Bari in kiraka inbaka haquri, Dan manzon Allah kayi hakuri, Nima wannan fili, siyarsa nayi, Kuma nadauki kudi nabawa wadda nasiya awajanta da shedu na dakomai, tasa hannu Nima nasa hannu, tabani takardun filaye Nima nadauki kudi nabata"

Cikin tsananin mamaki yace"wacece ta siyar Maka?"

Cikin tabbatar wa yace"Sunanta Munirat Abdul Salam,domin kuwa Alokacin ma ban sayi filayen ba saida ta tabbatar min cewa mijinta ne yabata su kyauta, saboda kasan harkar ciniki da mata"

Wani irin duhu duhu Shahaab yafara Gani, duk bayanin da mutumin yake masa kwata kwata baya jinsa, tun lokacin daya ce masa munirat Abdul Salam, tundaga lokacin yanemi nutsuwarsa yarasa, cikin tashin hankali yace"Kanaji na? Zanbaka kudin filayenka, da kudin daka kashe na aiki, saika Bani takardun filayen"

Cikin sauri Alhaji Umar yace"to yalla6ai babu damuwa godia nake"

Daga Nan yakashe wayar.

Wasu irin hawayene masu mutuqar zafi suka zubo daga idanun Shahaab, cikin ransa yace"munirat?"

Da alama zancen lallashi ya rushe 🤣🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️

Shahaab littafin kudi ne, idan kika karanta baki biyaba nabarki keda mahaliccin ki,inde ubangiji yana sakayya na tabbatar zai Sakamin

300
0164549488
Amina muhammad
GTbank

Ko katin mtn

Shedar biya ta wannan number 08033300034

Amnah El Yaqoub✍🏻

Page 37

Gaba daya saiya nemi 'yar sha'awar data addabeshi yarasa(😂)

Kansa yariqe da hannunsa guda biyu yafad'a Kan gadon tareda furta"innalillahi wa inna ilaihirraji'un"
Wani Hawayen ne suka sake zubo masa,yaji duniyar tayi masa zafi gaba daya, Dame yarage ta? Meta nema tarasa awajansa?meyasa zata masa haka? Har tasan tad'auki takardun filaye ta siyar, me zatayi da kudin? Meyasa mutumin daka daukakeshi fiyeda kowa yake cin amanarka daga baya?menene baiyiwa munirat ba? Haduwarsa da Aisha ne kad'ai yasan cewa yaraba soyaiyar dayake mata gida biyu yabawa Aisha d'aya,jin wayarsa tana ringing ne yasa yayi saurin goge Hawayen Idonsa, a fili ya furta, "dole zan dauki mataki akan munirat".

Wayar dake shirin katsewa yayi saurin dauka, daga dayan bangaren mama tace"Shahaab kaduba kagano inda Aishan take?"

Saida ya daidaita muryarsa yanda bazata gane yana cikin wani Hali ba, sannan yace"ban dubaba mama"

Cikin sauri Tace"A a, Tome kake nufi?shikkenan daga shiga wajan matarka harka manta da batun yarinya?yarinya qarama tafice tabar gidanka kacemin zaka duba Amma kayi biris harka samu munirat ka manta da Aisha,?Anya kuwa Shahaab zan'iya nema Maka auren yarinyar Nan? Tun yanzu ma kana shiga wajan matarka ka manta da batunta, tayaya za'a yi maganar aure tsakani da Allah?"

Duk da yana cikin halin damuwa saida ya danyi qaramar dariya yace"mama wanka zanyi saina duba nagani, karki damu mama, Aisha bazata 6ata acikin qasar nan nakasa dubo taba aduk inda take"

Cikin sauri tace"to hanzarta kayi wankan"

Wayar ya kashe, batareda tunanin komai ba ya lalubo number Hajja, wannan ne kiransa na farko wayar Hajja tun Bayan zuwan Aisha gidansa, kamar jira Hajja take, wayar tana shiga ta d'auka tareda sallama, cikin ladabi yace"Hajja barka da wannan lokaci"

Hajja tace"yawwa barkanmu dai, dawa nake magana?"

Murmushi yayi yace"Sunana Shahaab"

Cikin sauri Hajja tace"kacewa? Shahaab koba Shahaab ba?"

Cikin sauri Shima yace"eh haka nace, nine Shahaab, dama Ina neman Aisha ne"

Hajja tayi ajiyar zuciya tace"wacce Aisha?saida ka salwantar min da jika zaka debo jiki kana tambaya ta Ina Aisha? Nan kazo har gida ka hure mata kunne yarinya tayi tsalle ta dire tace Nan duniya saikai, kasa mamuda yaturata aiki har yau bansan inda jikata take ba, wallahi Shahaab idan Namutu bansake saka jikata a'idona ba hakuma ce zata rabani dakai...." daganan saita Fashe da Kuka

Runtse Idonsa yayi,cikin ransa yace"kuka!,kamar de Aishan"

Cikin nutsuwa yace"kinga, kiyi hakuri, insha Allah zata dawo gida lafiya, kiyi hakuri Dan Allah"

Cikin masifa Hajja tace"zaka rufemin baki ko saina wankeka da Mari? Kashe waya!"

Cikin sauri yakashe wayar yana Girgiza Kansa, da alama rikitacciya ce kamar mama, ajiyar zuciya yasauke, hakan yana nufin bataje gidaba kenan, dole zai bincika yagani, cikin sauri yatashi yashiga wanka

(idan kika karanta baki biyaba nabarki da mahaliccinki)
******

Bayan gwagwar mayar da Tasha, daqyar da d'an turancinta tasamu aka kaita inda zata shiga motar dazata kawo ta kano,suna cikin tafiya tana share hawaye daga idonta kad'an kad'an, waye yayi mata wannan sharrin? Abinda take tambayar kanta kenan, tun tana share hawaye harta Dena,tana addu'ah tana kallon garuruwa da dajujjukan dasuke wucewa har Allah yakawo su kano lafiya,yamma tayi sosai kasancewar hanyar akwai go slow, anan ma bata Sha wahala ba kawai napep ta tare tafada masa tana so yakaita inda zata hau motar dazata kaita dutse, yafada mata kudin, ta d'auka tabashi, sannan tashiga suka tafi, can ma tana zuwa tashar ake tambayar ta Ina zataje? Tafada musu dutse zataje, suka nuna mata wajan da ake lodin motocin dutse, taje tashiga, mutum biyu ne suka shiga Bayan shigar ta, aka kar6i kudin kowa, sannan driver yaja suka tafi, basu zo dutse ba Sai wajan karfe biyar da rabi, zuwa wannan lokacin duk ta gama galabaita, qafafunta sun dauki ciwo, ga yunwa, tunda tataho babu abinda tasaka acikin bakinta, ko tayi niyyar siyan wani abun idan ta tuna irin sharrin da aka mata saita ji duk duniyar ma tafita akanta, yanzu wannan vedio idan aka turawa wasu awaya shikkenan ita Kuma tagama watsuwa a duniya, lokaci daya, taji wani irin hawaye yasake zubo mata, cikin sauri tasaka hannu ta share, sannan ta nufi inda zata hau motar dazata kaita cikin garinsu, wato Garin CHAMO.

******

Bayan yagama wanka ya shirya, yad'auki computer sa, Adede lokacin munirat tashigo Dakin nasa, fuskarta babu walwala ta Wulla masa wayarta wadda ta kunna vedion da aka turo mata itada mama,wayar ya kalla yaga de irin vedion da mama ta nuna masa ne dazu, yasake kallon vedion ya kalleta, sannan ya Ta6e bakinsa yara6a ta gefenta yawuce, har yanzu idan ya tuna irin ta'asar data masa, wani irin qullutun baqin ciki yakeji a ransa, tabashi mamaki yanda baya zato, ko kadan bayason sake ganin ta, hakanne yasa daya futo zuwa falon su ma bai tsaya anan ba, Kai tsaye yafice zuwa compound din gidan cikin yar qaramar rumfarsu ta hutawa, wadda aka gama qwatata da tsari Mai kyau, ya zauna, sannan ya ajiye computer sa a gabansa yafara binciken location din da Aisha take, fuskar Nan tasa ahad'e, babu alamun farinciki ko walwala atare dashi, fatansa daya, Allah yasa bata cire agogon daga hannun taba, ko minti uku baiyi da zama awajan ba, Mai aiki tazo da sauri ta ajiye masa fruit da Kuma gorar ruwa tareda glass cup a gabansa ta juya cikin sauri.

Munirat kuwa mamaki da taqaicinsa ne suka sake kamata, tunani take a ranta me Mahmud yataka dayake mata wannan abubuwan?tana tunanin ai ayau din ta cancanci yayi mata komai domin ya lallashe ta saboda wannan vedio din, Amma sai gashi yagani, Amma yawuce yarabu da'ita, harda cewa zaizo ya lallashe ta ashe duk qarya ce Da yaudara, dama tariga tasan muddin yafara shiga wajan waccan tsohuwar, to Sai abinda ta kitsa masa, dama can ai itace tabashi lasisin iskanci da yarinyar, tunda itada kanta ta kama yarinyar ta riqe masa, yake ta6a mata nono, to yanzu kuwa dan ya aikata Zina da'ita ai ba zatayi masa fada ba, lokaci daya tasake jin tsanar mama acikin zuciyar ta, Fata take Dama ace ta mutu, kowama ya huta, tunanin da munirat ta dinga yi kenan Bayan fitar Shahaab daga cikin dakinsa.

Acan compound kuwa Shahaab baima kalli abinda aka gabatar masa ba, nutsuwa yayi yakafa Idonsa a computer yana aikin bincike, wata irin ajiyar zuciya yasauke Mai karfi, cikin tsananin farinciki ya furta"Alhamdulillah"sannan ne yad'auki inab guda daya yafara Sha ahankali, saida yasha fruit din sosai, sannan yatashi yanufi part din mama.

******

Lokacin datazo Garin duk mutane sun shiga sallar magrib, kasancewar Adede lokacin ta sauka, Garin take kallo kamar wanda tayi shekara bata cikin sa, wani irin farinciki ne ya kamata, jitake kamar tayi ihu, har gudu-gudu take hadawa dashi domin tayi sauri ta qarasa gida, tana shiga gidan kuwa ta kwasa a guje, Adede lokacin Hajja tana Zaman tahiya a sallarta, Ummah Kuma ta idar da alwala kenan ta miqe zata shige daki, cikin wani irin ihun murna ta daka tsalle ta d'ane umman ta, cikin jin dadi tace"Ummah...."

Cikin sauri Ummah ta juyo tana kallon ta baki bude, mamaki ya hanata yin magana, dariya tayi ta ce"ummah nadawo"

Hajja datayi sallama cikin tsananin mamaki tace"me sunan qawa?"

Cikin sauri tasaki Ummah tafada jikin Hajja tace"Hajja nah"

Sai a lokacin Ummah tayi magana tace"Wai kece Anya kuwa kokwade mafarkin Dana saba ne?"

Cikin sauri tace"Ummah nice mana, Zona mintsine ki kiji" taqarasa maganar cikin sigar tsokana.

Ummah tayi dariya ta Girgiza Kanta,tad'auki hijab tatada kabbarar sallah.
Hajja kuwa hannu ta daga sama ta kalli gabas tace"Alhamdulillah....Allah nagode Maka daka dawomin da jikata gida lafiya,su jummai Yan baqin ciki saide su mutu"(🤭😂)

******
Chapter 42 · 0% Book details