Sashe 7
Ribar Kafa Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Bangaren imaging suka nufa suka hau layin CT sai da sukai awa ɗaya da rabi sannan aka ƙirasu, har lokacin yaran nan sai dai ya zauna shiru sai yatsun sa da yake ta matsawa, sunshiga akace su jira shikuma aka bashi wani kayan, sai daya canza sannan aka shiga dashi, Likitan abokin wanda ya turosu daga Danbatta ne, bayan ya gama ya sa aka ƙira su kallan Alhaji Nuhu yai bayan ya nuna mishi hoton yace “Zaka iya faɗa min meya faru?” Nan ya kwashe kaf abinda ya faru ya sanar mai, shiru yai kafin ya juyo da computer ɗinshi saitinsu yace “Alzheimer’s disease baya nunawa ta CT scan, sai dai zamu iya detecting shrinkage daga ciki wanda sign ne na memory loss, wanda muke zargin tsoro da trauma na abinda ya faru shine yasa memory ɗinshi tafiya, sai dai da alama bazai daɗe ba zai dawo, ku samu ku nemi family ɗinshi ku maidashi dan zama cikin gurin daya saba rayuwa yana daga cikin abinda zai dawo da memory ɗinshi da sauri, b ciwo bane da za’asha magani a warke, ciwo ne wanda sai anyi hakuri.” Alhaji Nuhu Danbatta ya kalleshi yace “Muna tunanin kaishi police station daga nan, tsorona kar muryarsa ma ta ɓace dan ni haryanzu banji yayi magana ba.”
Kabiru da sauri yace “Baba yayiwa Kursum ɗazu na faɗa ma.”
Dr ɗin ya waiga yace “Tana ina? Tazo da alama zata taimaka gun buɗe bakinsa wanda shi zai taimakawa kwakwalwarsa.”
“Mun barta a gida, yanzu zamuje police station ɗin mungode.” Nan suka fito suka biya kuɗi sannan suka nufi police station lokacin har yamma tayi.
Shidai yaran nan binsu kawai yakeyi, police station ɗin unguwa Uku sukaje dan kuwa Dr ne ya basu wannan shawarar, ya kuma basu number DPO ɗin police station ɗin akan yantai maka musu. Suna sanarwa sune wanda aka turo aka kaisu gunshi, nan ya ɗau ki hoton yaran ya kuma sake musu tambayoyi, sai daya tabbatar da komai sannan yace “Yanzu zamu sa shi a cigiya amma bazamu barshi a gunmu ba dan bamuda inda zamu ajiyeshi amma ku koma dashi kubar numberku in muka baza cigiya aka samu wanda ya sanshi sai kuzo dashi.” Da sauri Kabir ya mike yace “Sorry DPO amma gwara ya zauna a gunku dan mu muna tsoro bamusan wanene shi ba wasu halaye yake dashi da zamu….” Jan bayan rigarsa Alhaji Nuhu Danbatta yai ya koma ya zauna kafin shia yai gyaran murya yace “Babu wata hanya data wuce wannan? Muna tsoron kar wani abu ya sameshi a gun mu.”
“Maganar gaskiya yaran nan yanzu dole ya zauna a gunku, har sai munsan su waye danginshi, zamusa cigiya gidan radio da tv zakuma mu samar da ragowar police station dan na tabbatar ko sati baza’ai ba zamu ji daga garesu indai suna raye.”
Alhaji Nuhu Danbatta ya jinjina kai yace “Shikenan mungode.” Numbersa ya bada daga Kabir wanda takaici duk ya hanashi magana.” Haka suka fito shidai yana binsu daga gefe, suna ɗan yin nisa Kabir ya waigo ya zare mai ido yace “Malan kama gabanka wallahi kaji na faɗa ma.”
Yana gamawa ya fara tafiya, waigowa yai ga mamakinsa yaran na binshi yana ganin zai waigo ya tsaya, kallan Alhaji Nuhu Danbatta yai yace “Baba kasan Allah mu gudu ya zamu ɗau ki yaran da bamusan ko dan fashi bane mukai gida?”
“Kai yanzu in akace ka tafi ka barshi anan tafiya zakai?”
“Da gudu ma kuwa, kana ganin fa yaran nan kasurgumin dan iska ne, haryanzu yaki mana magana ko likita yaki kulawa amma yawa Kursum magana.”
Alhaji Nuhu Danbatta ya kalli inda yake tausayin yaran ya ratsashi yace “Kai ka sani nidai haryanzu banjishi yana maganar dakace ba dan haka ka wuce mu tafi mu munyi iya namu sai muyi addu’ar Allah ya kawo iyayensa nan kusa.
(Anya DPO nada gaskiya kuwa? Shi kanshi yaran ko dai ta Kabiru ne dan fashi ne? )
7065283730
Opay
khadija Abdullahi shehu.
Katin waya MTN ta 07065283730
Shaidar biya ta 07065283730 or +447894142004
Bonanza ki biya 500 daga yau zuwa 12th ga wannan watan kunsani ni da ku 5&6🥰
Ayusher Ce🏌🏻♀️
RIBAR ƘAFA
NA
Wattpad :-AyusherMohd
Arewabook:- Ayushermuhd
ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀️
Paid Book
Shafi na Biyar
Kabiru da sauri yace “Baba yayiwa Kursum ɗazu na faɗa ma.”
Dr ɗin ya waiga yace “Tana ina? Tazo da alama zata taimaka gun buɗe bakinsa wanda shi zai taimakawa kwakwalwarsa.”
“Mun barta a gida, yanzu zamuje police station ɗin mungode.” Nan suka fito suka biya kuɗi sannan suka nufi police station lokacin har yamma tayi.
Shidai yaran nan binsu kawai yakeyi, police station ɗin unguwa Uku sukaje dan kuwa Dr ne ya basu wannan shawarar, ya kuma basu number DPO ɗin police station ɗin akan yantai maka musu. Suna sanarwa sune wanda aka turo aka kaisu gunshi, nan ya ɗau ki hoton yaran ya kuma sake musu tambayoyi, sai daya tabbatar da komai sannan yace “Yanzu zamu sa shi a cigiya amma bazamu barshi a gunmu ba dan bamuda inda zamu ajiyeshi amma ku koma dashi kubar numberku in muka baza cigiya aka samu wanda ya sanshi sai kuzo dashi.” Da sauri Kabir ya mike yace “Sorry DPO amma gwara ya zauna a gunku dan mu muna tsoro bamusan wanene shi ba wasu halaye yake dashi da zamu….” Jan bayan rigarsa Alhaji Nuhu Danbatta yai ya koma ya zauna kafin shia yai gyaran murya yace “Babu wata hanya data wuce wannan? Muna tsoron kar wani abu ya sameshi a gun mu.”
“Maganar gaskiya yaran nan yanzu dole ya zauna a gunku, har sai munsan su waye danginshi, zamusa cigiya gidan radio da tv zakuma mu samar da ragowar police station dan na tabbatar ko sati baza’ai ba zamu ji daga garesu indai suna raye.”
Alhaji Nuhu Danbatta ya jinjina kai yace “Shikenan mungode.” Numbersa ya bada daga Kabir wanda takaici duk ya hanashi magana.” Haka suka fito shidai yana binsu daga gefe, suna ɗan yin nisa Kabir ya waigo ya zare mai ido yace “Malan kama gabanka wallahi kaji na faɗa ma.”
Yana gamawa ya fara tafiya, waigowa yai ga mamakinsa yaran na binshi yana ganin zai waigo ya tsaya, kallan Alhaji Nuhu Danbatta yai yace “Baba kasan Allah mu gudu ya zamu ɗau ki yaran da bamusan ko dan fashi bane mukai gida?”
“Kai yanzu in akace ka tafi ka barshi anan tafiya zakai?”
“Da gudu ma kuwa, kana ganin fa yaran nan kasurgumin dan iska ne, haryanzu yaki mana magana ko likita yaki kulawa amma yawa Kursum magana.”
Alhaji Nuhu Danbatta ya kalli inda yake tausayin yaran ya ratsashi yace “Kai ka sani nidai haryanzu banjishi yana maganar dakace ba dan haka ka wuce mu tafi mu munyi iya namu sai muyi addu’ar Allah ya kawo iyayensa nan kusa.
(Anya DPO nada gaskiya kuwa? Shi kanshi yaran ko dai ta Kabiru ne dan fashi ne? )
7065283730
Opay
khadija Abdullahi shehu.
Katin waya MTN ta 07065283730
Shaidar biya ta 07065283730 or +447894142004
Bonanza ki biya 500 daga yau zuwa 12th ga wannan watan kunsani ni da ku 5&6🥰
Ayusher Ce🏌🏻♀️
RIBAR ƘAFA
NA
Wattpad :-AyusherMohd
Arewabook:- Ayushermuhd
ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀️
Paid Book
Shafi na Biyar