Sashe 6
Ribar Kafa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kallan Baba tai tace "Baba kasan Yaya Kabir ba karfi shiyasa." Harara ya zabga mata yace "Kinfa gama rainani yarinyar nan in saurayinki yazo zance ki tambayeshi wa ke tare musu faɗa." Fuska ta tamke ta ɗau kayan shayar data wanke tana cewa "Kai ka sanshi ni ban sanshi ba."
Baba ne ya katseshi da cewa "Ka tashi ka goyashi ko sai ka tabbatar mana bakada karfin?" Tahowa Adda Yagana tai sum-sum ta durkusa ta gaida Alhaji Nuhu wanda ya amsa mata fuskarsa sam babu wargi dan hankalinshi ma nakan Kabir wanda yake jiranshi ya ɗaga saurayin, haka ya tashi da kanshi dakyar aka iya ɗau rawa Kabir shi a baya, wani uban kara ya sa yace "Baba shikenan baya na ya ɓalle." Dariya Umma tasa harda tsalle tana cewa "Kabiru kaima kanada yaro ne?" Kamar zaiyi kuka yace "Umma in wannan yaro na ne ai shikenan ni kuma ta kare min." Da kyar yake iya takawa yana yi yana nishi haka ya karasa dashi ɗaki kifawa sukai kan katifar ɗakin tare abin da ya bashi mamaki juyi kawai saurayin yai ya cigaba da baccinsa. Saitin kuncinsa Kabir yakai hannu yanaji kamar ya tsinkamai mari sai kuma ya fasa ya miƙe, Baba dake jikin ƙofa yace kalla yace "Baba wannan wallahi da badan naji yana abin bacci ba ɗauka zanyi suma yai, nidai yaran nan tsoron zamanshi nake a gidan nan kar yasa a kamamu muma."
Ƙarasa shiga cikin Alhaji Nuhu yai yace "Kabir ni kaina a tsorace nake, yaro mun ganshi sama ta ka, na koma inda akai hatsarin man tabbas babu motar, to naji in motar an sace wanene zai ɗauke wari ɗayan takalmins? Dan kuwa babu shi a gun nan, nifa wannan ciwon mantuwan ban taɓa haɗuwa da yaro mai yinsa ba nadai san tsofafi nayi." Shiru yai dan shi gaba ɗaya ya kasa tunanin abin yi.
"Shiyasa nace ma mu kaishi police station, Baba bamuda kuɗin kula da shi sannan in kuma yaki warkewa fa? Ko kuma daga baya aka gane yana gun mu akace saceshi mukai? Bamuda hujja tunda bamu kaishi police station ba." Jinjina kai yai alamun gamsuwa yace "Ka shirya inya tashi yaci abinci sai mu wuce, ni zan leka makaranta." Yana gama fadar haka ya juya ya fito, Kursum da sauri ta taho inda yake tace "Baba abinci, dumamenka na ɗaki a kula."
Kallanta yai ɗauke da murmushi yace "To Kursum Allah ya miki albarka, ya akai yau bakije makaranta ba? Ita dama Hasina nasan in har bana nan ba zuwa zatai ba."
Kanta na ƙasa tace "Kayi hakuri Baba wallahi tsoron barin Umma ita kaɗai nai, dama da Yaya Kabir na nan ne." Kallan inda Umma take yai tana ta wasanta da kafafuwanta kai kafe yarinyacw ƴar shekara 5, tausayin ta ya kara kamashi yace "Taci abinci ne?"
"A'a yanzu zatasha tea ruwan muke jira yai zafi." Yana jin haka yai ɗaki, yana shiga yace "Kursum zo." Ba musu ta mike ta shiga bayan ya amsa sallamarta, inda ta ajiye tuwon ta kalla ganin yatsarshi na nuna mata gun yace "Ki ɗauka ki bata ni in na fita zansha shayi, kinsani sarai bata iya rike yunwa yanzu sai kiga ta fara kuka."
Abinda ya faru ɗazu take san sanar mai sai dai sam batasan hankalinsa ya tashi, muryarta na rawa tace "Baba kaima bakaci komai ba tun jiya, sannan hannunka da alama ciwo kaji."
Kallan hannun yai ya akai ta gane? Dan ya riga ya kunce ɗaurin da aka mai saboda baisan su damu, kanta ta sunkuyar tace "Dazu da kana taimakawa abokin Yaya Kabiru naga sanda ka dan yarfe hannunka alamun zafi daga nan kuma kasa hannunka a baya shiyasa nake zargin bigewa kai."
Fuskarta ya kalla cike da tausayi yace "Allah ya miki albarka Kursum nagode da kulawa."
Har zata mike sai kuma ta koma tace "Baba nace maganar Inna dan......" yanda ya kalleta ne yasa tai shiru ta ɗau kwanan ta fita dashi, zama yai a bakin gadan ɗakin yai shiru, sai kuma ya mike ya shiga bandaki ya watsa ruwa sannan ya zura wasu kayan ya fito ya nufi makarantar islamiyar sa dake nan bayan gidanshi. Zama yai da wakilin makaranta ya tambayeshi ko akwai kuɗi a rantamai zai kai yaro asibiti, nan yace dubu ɗari kawai garesu a asusu, haka ya turamai ya fito yana tafe yana tunanin yanda zaiyi ya maida yaran nan cikin danginshi.
A gida kuwa Hasina da Raheena haka suka dafa tea aka siyo bread aka sha, suna ci suna hararar Kursum wacce abubuwansu basa damunta itadai kar su taɓa Umma kawai shine magana.
Adda Yagana ce ta kalleta tana taunar bread a bakinta tace "Kursum shi wancan saurayin da aka shiga dashi ɗaki wanene shi?" Kallan ɗakin Kabir tai ta girgiza kai alamar rashin sani kafin tace "Oho! Inaji abokin Ya Kabir ne kinsanshi da kwashe-kwashe."
Baki ta taɓe tace "Haka kawai suyi ta kawo mana kutane gida kamar gidan haya."
Itadai Kursum batace komai ba dan yau tun abinda ya faru da Umma taji batasan magana dayawa. Raheena ta kalli shanyar datai tace "Shine dan munafurci kikai wanki baki ce na kawo nawa ba?"
"Dadinta dai kinada hannun nan sannan kina da ƴan kudinki kinga kuwa in bakisan yi sai ki biya na miki dan ba dalilin da zai sani yi miki wanki baki biya ba."
Wata harara Raheena ta zabga mata tace "Kefa yanzu bakida kunya gaba ɗaya tunda Inna tabar gidan nan kika feɗare na rantse da Allah duka zan miki kuma na da ki banza dan yanda kike a bushen nan in na makeki kila sai na balla ki." Dariya ce ta kwace mata ba tare da tace komai ba, mikewa tai bayan ta gama ta wanke kwanukan da suka ci abinci tasa ruwan abincin rana tanayi Umma na zaune tana wasa a gefenta.
Alhaji Nuhu Danbatta ne ya dawo kallo ɗaya zakamai kasan a wahale yake dan tunda ya fita har wannan lokacin kudin daya samu ɗazu kawai shi ne a hanunsa ya rasa motar da zai samu suje su dawo, shi kuma nauyin tambayar aro yake dan a rayuwarshi ba abinda ya tsana irin ya ɗau rawa wani nauyi, da sallama ya shigo kafin ya fara kwallawa Kabiru ƙira. Tunda Kabiru ya fito ya saki baki yana kallanshi, mamaki gaba ɗaya ya cikashi ganinsa sanye da kayan saurayin nan, ya kwama trainers dinshi wanda gefenshi duk ya cinye, sai wani bouncing yake shi a dole ɗan gaye. Hannu Alhaji Nuhu Danbatta ya ware alamun zagi yace “Ungo nan, kai ni meke damunka? Taya zaka ɗau ki kayan yaro ya ka saka? Ko kunya ma bakaji? In kuma kayan dashi iyayensa zasu ganeshi fa?” Bayan kansa ya shafa yace “Baba indai da kayan zasu ganeshi to alamu ne na masu hali kaga shikenan sai nai fuska nace nine.” Fuska a tamke yace “Ka wuce ka bashi kayansa ko sai nazo na kifama mari? Shashasha kawai.”
Baki Kabiru ya turo ya koma ɗaki inda saurayin ke zaune sanye da kayan Kabirun na ɗazu kallansa yai ya kalli shinkafa da waken da aka kawomai wanda haryanzu baici ba yace “Kaga in ba yunwa kake ji ba cire kayan nan ka bani mu wuce.” Kallansa yai kamar bai gama gane abinda yake nufi ba, Kabir ya ɗaga shi yace “Kayana zakaban, zan amshi wannan in zamu barka a police station.” Kai kawai ya ɗaga alamun to sannan ya canza kaya, tare suka fito dan shidai ya koshi shi wannan tunda baisan cin abinci shiya sani.
A waje ya tadda Baba na jiransu kallan saurayin yai yace “Yaro ka tashi? Ba inda ke ma ciwo?” Murmushi ne a fuskarsa ya girgiza kai alamun babu. Kabir yace “Kai magana mana sai ai ta tambayarka kana ɗaga kai kamar wani kurma.”
“Kai dai ka fiya neman magana ai dai baka taɓa ji yayi magana ba sai ka bari muji ko ma yana magana.”
Da sauri ya dawo gaban saurayin yace “Baba yaran nan wallahi yana magana, kai ɗazu bakawa Kursum magana ba? Harda wani guntun turancinka.”
Jin haka Alhaji Nuhu ya kalleshi yace “Kana magana?” Kai ya ɗaga alamun eh “Sunan ka fa? Ka tuna?” Kai ya sunkuyar tare da girgiza kai alamar a’a, baki Kabir ya taɓe yace “To meya hanaka magana yanzu? Baba dan Allah muje ni wallahi kaina ya fara ciwo.”
Fitowa sukai suka nufi tasha, mota suka hau golf suka zauna a baya su uku aka samu ciko mai kota yaja suka tafi, ana fara tafiya ko minti goma ba’ai ba saurayin nan ya fara bacci. Mamaki ya kama Kabir yace “Baba wannan baccin nashi anya na lafiya ne? Yini fa yai yana bacci.”
“Kabir ba wannan ba, Aminu Kano ya kamata mu fara zuwa a tabbatar dame ke damunshi kafin muje police station.” Zaiyi magana Alhaji Nuhu ya katseshi da cewa “Hakkin mu me mu tabbatar munyi duk abinda ya kamata, kada ka manta hatsari mukai kuma ni ke da laifi.” Shiru yai dan yasan bashida amsar maganaa. Shiru sukai kowa da abinda yake sakawanhar suka iso Aminu Kano.
Baba ne ya katseshi da cewa "Ka tashi ka goyashi ko sai ka tabbatar mana bakada karfin?" Tahowa Adda Yagana tai sum-sum ta durkusa ta gaida Alhaji Nuhu wanda ya amsa mata fuskarsa sam babu wargi dan hankalinshi ma nakan Kabir wanda yake jiranshi ya ɗaga saurayin, haka ya tashi da kanshi dakyar aka iya ɗau rawa Kabir shi a baya, wani uban kara ya sa yace "Baba shikenan baya na ya ɓalle." Dariya Umma tasa harda tsalle tana cewa "Kabiru kaima kanada yaro ne?" Kamar zaiyi kuka yace "Umma in wannan yaro na ne ai shikenan ni kuma ta kare min." Da kyar yake iya takawa yana yi yana nishi haka ya karasa dashi ɗaki kifawa sukai kan katifar ɗakin tare abin da ya bashi mamaki juyi kawai saurayin yai ya cigaba da baccinsa. Saitin kuncinsa Kabir yakai hannu yanaji kamar ya tsinkamai mari sai kuma ya fasa ya miƙe, Baba dake jikin ƙofa yace kalla yace "Baba wannan wallahi da badan naji yana abin bacci ba ɗauka zanyi suma yai, nidai yaran nan tsoron zamanshi nake a gidan nan kar yasa a kamamu muma."
Ƙarasa shiga cikin Alhaji Nuhu yai yace "Kabir ni kaina a tsorace nake, yaro mun ganshi sama ta ka, na koma inda akai hatsarin man tabbas babu motar, to naji in motar an sace wanene zai ɗauke wari ɗayan takalmins? Dan kuwa babu shi a gun nan, nifa wannan ciwon mantuwan ban taɓa haɗuwa da yaro mai yinsa ba nadai san tsofafi nayi." Shiru yai dan shi gaba ɗaya ya kasa tunanin abin yi.
"Shiyasa nace ma mu kaishi police station, Baba bamuda kuɗin kula da shi sannan in kuma yaki warkewa fa? Ko kuma daga baya aka gane yana gun mu akace saceshi mukai? Bamuda hujja tunda bamu kaishi police station ba." Jinjina kai yai alamun gamsuwa yace "Ka shirya inya tashi yaci abinci sai mu wuce, ni zan leka makaranta." Yana gama fadar haka ya juya ya fito, Kursum da sauri ta taho inda yake tace "Baba abinci, dumamenka na ɗaki a kula."
Kallanta yai ɗauke da murmushi yace "To Kursum Allah ya miki albarka, ya akai yau bakije makaranta ba? Ita dama Hasina nasan in har bana nan ba zuwa zatai ba."
Kanta na ƙasa tace "Kayi hakuri Baba wallahi tsoron barin Umma ita kaɗai nai, dama da Yaya Kabir na nan ne." Kallan inda Umma take yai tana ta wasanta da kafafuwanta kai kafe yarinyacw ƴar shekara 5, tausayin ta ya kara kamashi yace "Taci abinci ne?"
"A'a yanzu zatasha tea ruwan muke jira yai zafi." Yana jin haka yai ɗaki, yana shiga yace "Kursum zo." Ba musu ta mike ta shiga bayan ya amsa sallamarta, inda ta ajiye tuwon ta kalla ganin yatsarshi na nuna mata gun yace "Ki ɗauka ki bata ni in na fita zansha shayi, kinsani sarai bata iya rike yunwa yanzu sai kiga ta fara kuka."
Abinda ya faru ɗazu take san sanar mai sai dai sam batasan hankalinsa ya tashi, muryarta na rawa tace "Baba kaima bakaci komai ba tun jiya, sannan hannunka da alama ciwo kaji."
Kallan hannun yai ya akai ta gane? Dan ya riga ya kunce ɗaurin da aka mai saboda baisan su damu, kanta ta sunkuyar tace "Dazu da kana taimakawa abokin Yaya Kabiru naga sanda ka dan yarfe hannunka alamun zafi daga nan kuma kasa hannunka a baya shiyasa nake zargin bigewa kai."
Fuskarta ya kalla cike da tausayi yace "Allah ya miki albarka Kursum nagode da kulawa."
Har zata mike sai kuma ta koma tace "Baba nace maganar Inna dan......" yanda ya kalleta ne yasa tai shiru ta ɗau kwanan ta fita dashi, zama yai a bakin gadan ɗakin yai shiru, sai kuma ya mike ya shiga bandaki ya watsa ruwa sannan ya zura wasu kayan ya fito ya nufi makarantar islamiyar sa dake nan bayan gidanshi. Zama yai da wakilin makaranta ya tambayeshi ko akwai kuɗi a rantamai zai kai yaro asibiti, nan yace dubu ɗari kawai garesu a asusu, haka ya turamai ya fito yana tafe yana tunanin yanda zaiyi ya maida yaran nan cikin danginshi.
A gida kuwa Hasina da Raheena haka suka dafa tea aka siyo bread aka sha, suna ci suna hararar Kursum wacce abubuwansu basa damunta itadai kar su taɓa Umma kawai shine magana.
Adda Yagana ce ta kalleta tana taunar bread a bakinta tace "Kursum shi wancan saurayin da aka shiga dashi ɗaki wanene shi?" Kallan ɗakin Kabir tai ta girgiza kai alamar rashin sani kafin tace "Oho! Inaji abokin Ya Kabir ne kinsanshi da kwashe-kwashe."
Baki ta taɓe tace "Haka kawai suyi ta kawo mana kutane gida kamar gidan haya."
Itadai Kursum batace komai ba dan yau tun abinda ya faru da Umma taji batasan magana dayawa. Raheena ta kalli shanyar datai tace "Shine dan munafurci kikai wanki baki ce na kawo nawa ba?"
"Dadinta dai kinada hannun nan sannan kina da ƴan kudinki kinga kuwa in bakisan yi sai ki biya na miki dan ba dalilin da zai sani yi miki wanki baki biya ba."
Wata harara Raheena ta zabga mata tace "Kefa yanzu bakida kunya gaba ɗaya tunda Inna tabar gidan nan kika feɗare na rantse da Allah duka zan miki kuma na da ki banza dan yanda kike a bushen nan in na makeki kila sai na balla ki." Dariya ce ta kwace mata ba tare da tace komai ba, mikewa tai bayan ta gama ta wanke kwanukan da suka ci abinci tasa ruwan abincin rana tanayi Umma na zaune tana wasa a gefenta.
Alhaji Nuhu Danbatta ne ya dawo kallo ɗaya zakamai kasan a wahale yake dan tunda ya fita har wannan lokacin kudin daya samu ɗazu kawai shi ne a hanunsa ya rasa motar da zai samu suje su dawo, shi kuma nauyin tambayar aro yake dan a rayuwarshi ba abinda ya tsana irin ya ɗau rawa wani nauyi, da sallama ya shigo kafin ya fara kwallawa Kabiru ƙira. Tunda Kabiru ya fito ya saki baki yana kallanshi, mamaki gaba ɗaya ya cikashi ganinsa sanye da kayan saurayin nan, ya kwama trainers dinshi wanda gefenshi duk ya cinye, sai wani bouncing yake shi a dole ɗan gaye. Hannu Alhaji Nuhu Danbatta ya ware alamun zagi yace “Ungo nan, kai ni meke damunka? Taya zaka ɗau ki kayan yaro ya ka saka? Ko kunya ma bakaji? In kuma kayan dashi iyayensa zasu ganeshi fa?” Bayan kansa ya shafa yace “Baba indai da kayan zasu ganeshi to alamu ne na masu hali kaga shikenan sai nai fuska nace nine.” Fuska a tamke yace “Ka wuce ka bashi kayansa ko sai nazo na kifama mari? Shashasha kawai.”
Baki Kabiru ya turo ya koma ɗaki inda saurayin ke zaune sanye da kayan Kabirun na ɗazu kallansa yai ya kalli shinkafa da waken da aka kawomai wanda haryanzu baici ba yace “Kaga in ba yunwa kake ji ba cire kayan nan ka bani mu wuce.” Kallansa yai kamar bai gama gane abinda yake nufi ba, Kabir ya ɗaga shi yace “Kayana zakaban, zan amshi wannan in zamu barka a police station.” Kai kawai ya ɗaga alamun to sannan ya canza kaya, tare suka fito dan shidai ya koshi shi wannan tunda baisan cin abinci shiya sani.
A waje ya tadda Baba na jiransu kallan saurayin yai yace “Yaro ka tashi? Ba inda ke ma ciwo?” Murmushi ne a fuskarsa ya girgiza kai alamun babu. Kabir yace “Kai magana mana sai ai ta tambayarka kana ɗaga kai kamar wani kurma.”
“Kai dai ka fiya neman magana ai dai baka taɓa ji yayi magana ba sai ka bari muji ko ma yana magana.”
Da sauri ya dawo gaban saurayin yace “Baba yaran nan wallahi yana magana, kai ɗazu bakawa Kursum magana ba? Harda wani guntun turancinka.”
Jin haka Alhaji Nuhu ya kalleshi yace “Kana magana?” Kai ya ɗaga alamun eh “Sunan ka fa? Ka tuna?” Kai ya sunkuyar tare da girgiza kai alamar a’a, baki Kabir ya taɓe yace “To meya hanaka magana yanzu? Baba dan Allah muje ni wallahi kaina ya fara ciwo.”
Fitowa sukai suka nufi tasha, mota suka hau golf suka zauna a baya su uku aka samu ciko mai kota yaja suka tafi, ana fara tafiya ko minti goma ba’ai ba saurayin nan ya fara bacci. Mamaki ya kama Kabir yace “Baba wannan baccin nashi anya na lafiya ne? Yini fa yai yana bacci.”
“Kabir ba wannan ba, Aminu Kano ya kamata mu fara zuwa a tabbatar dame ke damunshi kafin muje police station.” Zaiyi magana Alhaji Nuhu ya katseshi da cewa “Hakkin mu me mu tabbatar munyi duk abinda ya kamata, kada ka manta hatsari mukai kuma ni ke da laifi.” Shiru yai dan yasan bashida amsar maganaa. Shiru sukai kowa da abinda yake sakawanhar suka iso Aminu Kano.