Sashe 5
Raina Kama Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
.............Cikeda tsantsar mamaki Galadima ya jujjuya wayar a hannunsa, kai kace itace zata fassara masa ma'anar sak'on, kuma komawa yay yana karanta sak'on a karo na biyu, a fili yace, *“SURIKI! SURIKI!.* to nikam wanenen sirikina?”.
A take zuciyarsa tabashi amsa da *Baban matarka ta contract*. wata fad'uwar gabace ta samesa lokaci guda, wadda ALLAH ya tak'aita bata buga da bugun zuciyarsa ba, cikin tsitstsinkewar tunani dana zuciya yashiga bitar message d'in kamar mai haddar karatu, idan ya fahimci sak'onan dai akwai mummunan al'amari daya faru akan mahaifin munaya kenan? “ya salam”. ‘ya furta a fili, cikin dafe kansa yakuma fad'in “to adalilin mi wani abu zai samesa kuma yazam kamar yashafeni?”. gabansa yakuma fad'uwa, mutuwar Alhaji Abdussalam Abba mahaifinsu Samha ta dawo masa a rai, (mijin aunty Mimi). dafe kansa dake shirin sara masa yayi, to mizai kawo Abban munaya cikin case d'insa kuma? Sam bazai yuwuba ma, koma dai by mistake wani yaturo masa sak'on ne?. “mtoww! K'ilama hakane”. ‘yay maganar a fili yanajan guntun tsaki, tareda jefa wayar kan gado yacigaba da shirinsa.
Shiri yake amma yakasa fidda abin a ransa, koyayi k'ok'arin ture tunanin gefe sai yakasa, dukda zuciyarsa tak'i yarda ta gaskata sak'on nasane. shiri ya kammala cikin Ash color d'in shadda gizna dakakkiya, tamasa k'yau ainun, komai nasa saiya saka Ash, Takalminsa helf cover, agogo da hula duk ash, ya kwashi phones nashi a hannu, ya fesa turare da gyara zaman hularsa sannan ya ciro wayarsa d'aya a aljihu, dan yakasa daurewa, number yaa marwan ya lalubo ya kirasa.
A time d'in yaa marwan nata lallashin Munubiya tasha shayi sutafi asibitin amma tak'i, ta gardame akan ta k'oshi itadai su tafi kawai, mama Rabi'a dasu Ayusher sunyi lallashi amma tak'i yin shiru tasha, sai kuka take, hakan yasaka feena zuwa d'akin yaa marwan takirasa, shine yaketa lalla6ata amma tak'i kar6a, sai kawai ya had'e fuska ya koma mata ainahin marwan da bai d'aukar raini, cikin daka tsawa da hargagi yamik'a mata shayin, jiki na rawa takar6a tafara sha, tayi nisa dashan tafara amai kuma, mama Rabi'a tarik'eta, sukuma suka shiga mata sannu, yaa marwan na dafe da kansa cikin damuwa kiran Galadima ya shigo masa, kamar bazai d'aukaba saikuma yaciro wayar a aljihu ya diba.
Mamakine ya kamashi dayaga sunan Galadima ta Nigeria, (ko sunzo k'asarne?), da hanzari ya d'auka tana gab da katsewa.
Yanda Galadima yaji muryar yaa marwan yayinda yake amsa masa sallama sai hankalinsa ya tashi, ko gaisuwar kirki basuyiba Galadima ya hau masa tambaya akan Abba.
Yaa marwan yace “gaskiyane ranka ya dad'e, jiya misalin 12pm Abba yayi accident, sunyi taho mu gama da wata thriller, yanzu hakama yana general hospital”.
Zufar dake tsatstsafowa a fuskarsa yasa handkerchief ya share, muryarsa na rawa yace, “Marwan da gaske?”.
Kula yaa marwan yayi Galadima kamar ba a hayyacinsa yakeba, shima muryarsa na rawa yace, “da gaskene ranka ya dad'e”.
“hasbinallahu wani'imal'wakil” Galadima yafara maimaitawa akan la66ansa, ya sauke wayar a hankali zuciyarsa na wani irin suya, yama rasa wane kalar tunani yakamata ace yayi? Yaya zai fassara wannan lamarin? Kenan akwai wani Abu dabai saniba, kodai Abban munaya yanada wata masaniya akan lamarinsa, kokuma bai saniba yafad'a tarko, tabbas yakamata ma akan kansa yay wannan tunanin kodan abinda yayta faruwa tsakaninsa da Munaya, cikin k'araji yace “MUFTAHU!! kasan komai, dolenema kasan komai muftahu!!!, tabbas duk da kasancewarka d'an uwana, jinina, saina binneka da ranka a tsakkiyar masarautarnan inhar mahaifin matata ya rasa ransa wlhy, wannan ALWASHI NANE!!.
ya k'are maganar yana buga table glass dake gabansa da masifar k'arfi, aiko ya tarwatse a wajen, kwalba ta yanka masa hannu. baibi takan ciwon dayaji ba yamik'e a harzuk'e ya d'auki wayar ya fice.
A yanda yafito sai hankali hadimansa ya tashi, ga hannunsa yana d'igar da mini kad'an-kad'an, kuma suna gaisheshi yak'i amsama kowa gaisuwarsa, ko hannun daya saba d'aga musu inbaya buk'atar maganar yau basu samuba, da kansa yabud'e motar yashiga, hakan yasaka sarkin Mora Shiga da hanzari shima shida sauran dogaran dakan bisa in zai fita.
Ko takan zuwa fada yay gaisuwa baibiba, suna fita daga masarautar kiran Nuren yashigo wayarsa.
Yana d'agawa yace, “kajiramu a plaza”. ‘abinda yace kenan kawai ya Yanke wayar'.
Nuren yabi wayar da kallo, inhar kunnensa yajiye masa dai-dai to ran Galadima a matsanancin 6ace yake, to mi aka masa? kokuma shida mutuniyar tasane mama Fulani? Nuren ya girgiza kai kawai yana murmushi, mama Fulani da Galadima sai addu'a kawai, dan tamkar suna ganin hanjin junane.
Tafiyar mintuna 30 takawosu plaza, amma basu shigoba, dan haka Nuren yana hangosu yataso yafito.
Matashin Saurayine shima, mai kama da Galadima sosai, dan wandama bai saniba saiya d'auka tagwayene, abubuwa kad'anne suka banbantasu, dan a shekaruma zasu iya zuwa d'aya, shima Nuren dagani yana cikin Hutu sosai, gashi d'an gaye ajin farko cikin nutsatstsun matasa masu ji da kai.
Da sauri dogari d'aya yafito ya rissina yana gaisheshi, hannu ya d'aga masa cikin sarauta (hakan ya tabbatar min shima jinin sarautar ne) dogarin yabud'e masa inda Galadima yake ya shiga.
Kallo d'aya yayma Galadima ya tabbatar akwai Matsala, hannu yabashi sukayi musabaha, cikin tsantsar kulawa yace, “brother mike faruwa ne?”.
Galadima ya kalli Nuren da idanunsa da suka koma jajaye, cikin matsanancin d'acin zuciya yace, “bansan alak'ar data sashi cikin tawa ba”.
Nuren yace, “waye?”.
Kauda idonsa Galadima yayi daga kallon Nuren, ya maida ga window yana kallon mutane daketa harkokinsu, wani murmushin takaici yayi, sanan yafurta *“SIRIKI!”*
Nuren yazaro idanunsa waje, a zabure yace, “yanzu haka yana ina?”.
“general hospital ”.
Nuren yay hanzarin fad'ama sarkin mota “muje general hospital na garinnan”.
“to ranka ya dad'e”. ‘sarkin mota yafad'a a ladabce.
Hannun Galadima dake d'igar jini har yanzu Nuren ya kamo, ya kalli Galadima da alamar tambayar miya damesa? amma shi galadiman sai yamak'i kallonsa, Nuren ya girgiza kai kawai Dan yasan hakan dayayi bazai fad'aba ne, handkerchief d'insa ya Ciro ya d'aure hannun Na Galadima Dan jinin a samu ya tsaya daga zubar, dukya d'an 6ata seat d'in mortar kad'an, da yake a nan ya ajiye hannun daga gefe. ran Nuren a 6ace yace “brother dolene muyi bincike akan Surukinka, dan duk ta yanda zamu fassara a yanzu, zukatanmu bazasu d'aukaba. zamu iya zargin akwaima hannunsa a ciki, zamu iya zargin sunnemi wani Abu daga garesa yak'i basu had'in kai, zamu iya zargin abubuwa da dama”.
Iska Galadima ya furzar daga bakinsa, yasaka hannu ya tura hularsa baya, kansa ya jingina da kujerar tareda lumshe idanu. zuciyarsa tana tunani yaushene zai kawo k'arshen mak'iyan mahaifinsa? Sai yaushene za'ayi walk'iya yagansu? yana buk'atar sanin dalilinsu Na za6ar maida masa mahaifi haka, miyayi musu?.
Wannan tambayoyin yakema kansa kullu yaumin ta kowacce rana.
Hannunsa Nuren yakamo yad'an matsa, Galadima yabud'e idonsa dasuka fara komawa kalar jaa. “brother a wannan karon bana buk'atar 6acin ranka, dan duk sanda ranka ya6aci baka iya Controlling d'in fushinka, fushinka Na saka aikinmu tafiyar wahainiya, lokaci yayi dazaka saba da irin wad'annan abubuwan fa, karinga saka nutsuwa a zuciyarka aduk lokacin da irin haka tafaru, kamarfa yanda takawa (papi) yake fad'a mana ne a kullum, sufa sunayin wad'annan abubuwanne dan kawai su fusata ka, a haukansu zasu iya samun nasara a kankan saboda ciwon da ALLAH ya jarabceka dashi, waynote kaikuma ka karya wannan kwarin guywar tasu OK?”.
Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, shima ya dafa hannun Nuren d'in yana lumshe idanu, a hankali yace “Okey it's better”.
Daga nan motar ta d'auki shiru, ahaka suka isa asibitin.
Zuwa lokacin jama'ar gidanmu sun kuma cika asibitin, harsu Munubiya duk sunzo suma.
Tunda motocin Galadima uku suka shigo asibitin kallo ya koma Kansu, kowa son ganin mai fitowa yakeyi.
Dogaraine suka fara fitowa, kafin abud'ema su Galadima.
'Yan gidanmu sun fahimci daga masarautane, amma babu Wanda yay tunanin ganin Galadima d'in.
Tunda yafito kwarjininsa da cikar haibarsa ta kasancewarsa jinin sarauta ta cika idanun jama'ar wajen, dogarensa sun tsare ko ina babu mai damar ra6arsa, Nuren na gefen hannun damarsa.
Wayyo, nanfa ido yaymasa caa, baya son kallo ko kad'an, amma yaya zaiyi, tunda jama'a sunga abin kallon.🤦🏻♀
Tunkan ya k'araso su yaa Hameed suka mik'e suka nufoshi. Munubiya kam bayansa kawai take lek'awa, azatonta harda 'Yar uwarta. amma ganin babu alamar mace ma acikinsu sai jikinta yay sanyi.
Hannu Galadima ya d'agama dogaransa alamar su dakata, baya suka ja, yayinda shikuma yamik'ama yaa Shafi'u daya fara k'arasowa hannu, sun gaisa da yayuna cikin girmama juna, kafin sumasa jagora zuwa ciki inda Abba yake.
Dayake su Munubiya suna daga gefene, shiyyasa basu gaisa da Galadima ba, sai k'amshin turarensa daya cika hancinansu.
Dukda halin da ake ciki, saida 'yan gidanmu sukaji Hassada, kowa jitake inama mijin 'yartane🤕🥴.
Humm doctor daya hana kowa ganin Abba saigashi jikinsa Na rawa ya tarbi Galadima, daddy da baba k'arami sunje gida suyo wanka, bayan dawowar su yaa Naseer sai sukuma suka tafi.
Doctor yama Galadima jagora har d'akin da Abba yake kwance. “Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un” kawa Galadima ke iya fad'a a la66ansa, maganar gaskiya jikin Abba babu k'yawun gani, yaa Shafi'u ma mai ragguwar zuciya kasa daurewa yayi yafice da sauri yana hawaye, yaa Hameed kam runshe ido yayi zuciyarsa Na suya kamar zata fad'o k'asa.
Galadima ya dafe bango tareda rik'e kansa dayaji ya sara masa, halin da Abba yake ciki exactly dana Alhaji Abdus'salam Abba.
Da sauri Nuren yaruk'o hannunsa, a hankali yake fad'in “Control yourself please”.
Doctor yajawo kujera biyu yabama Galadima da Nuren dansu zauna.
Ina kasa zaman sukayi, dole suka fito. Galadima yabuk'aci ganin doctor d'in.
'Yan gidanmu kuwa fitowar yaa Shafi'u yana share hawaye yasaka zukatansu kuma tashi, caa sukayo kansa da tambayar lafiya.
Kasa magana yayi, ahaka su Dady suka samesu, sukansu jiki a sanyaye suka k'araso wajen, kardai ace d'an uwansu yatafi ya barsune. muryoyinsu har rawa sukeyi wajen tambayar lafiya?.
Sai alokacin yaa shafi'u yasamu bakin maganar cemusu bafa rasuwa yayiba, jikinnasane sai babu dad'in kallo.
Baba k'arami yace, “sun bari kun gansane?”.
“Eh baba, Galadima ne mijin Munaya yazo”.
Dady da baba k'arami ciki suka shiga, sukabar 'yan gidanmu dake kuka abin gwanin tausayi.
A take zuciyarsa tabashi amsa da *Baban matarka ta contract*. wata fad'uwar gabace ta samesa lokaci guda, wadda ALLAH ya tak'aita bata buga da bugun zuciyarsa ba, cikin tsitstsinkewar tunani dana zuciya yashiga bitar message d'in kamar mai haddar karatu, idan ya fahimci sak'onan dai akwai mummunan al'amari daya faru akan mahaifin munaya kenan? “ya salam”. ‘ya furta a fili, cikin dafe kansa yakuma fad'in “to adalilin mi wani abu zai samesa kuma yazam kamar yashafeni?”. gabansa yakuma fad'uwa, mutuwar Alhaji Abdussalam Abba mahaifinsu Samha ta dawo masa a rai, (mijin aunty Mimi). dafe kansa dake shirin sara masa yayi, to mizai kawo Abban munaya cikin case d'insa kuma? Sam bazai yuwuba ma, koma dai by mistake wani yaturo masa sak'on ne?. “mtoww! K'ilama hakane”. ‘yay maganar a fili yanajan guntun tsaki, tareda jefa wayar kan gado yacigaba da shirinsa.
Shiri yake amma yakasa fidda abin a ransa, koyayi k'ok'arin ture tunanin gefe sai yakasa, dukda zuciyarsa tak'i yarda ta gaskata sak'on nasane. shiri ya kammala cikin Ash color d'in shadda gizna dakakkiya, tamasa k'yau ainun, komai nasa saiya saka Ash, Takalminsa helf cover, agogo da hula duk ash, ya kwashi phones nashi a hannu, ya fesa turare da gyara zaman hularsa sannan ya ciro wayarsa d'aya a aljihu, dan yakasa daurewa, number yaa marwan ya lalubo ya kirasa.
A time d'in yaa marwan nata lallashin Munubiya tasha shayi sutafi asibitin amma tak'i, ta gardame akan ta k'oshi itadai su tafi kawai, mama Rabi'a dasu Ayusher sunyi lallashi amma tak'i yin shiru tasha, sai kuka take, hakan yasaka feena zuwa d'akin yaa marwan takirasa, shine yaketa lalla6ata amma tak'i kar6a, sai kawai ya had'e fuska ya koma mata ainahin marwan da bai d'aukar raini, cikin daka tsawa da hargagi yamik'a mata shayin, jiki na rawa takar6a tafara sha, tayi nisa dashan tafara amai kuma, mama Rabi'a tarik'eta, sukuma suka shiga mata sannu, yaa marwan na dafe da kansa cikin damuwa kiran Galadima ya shigo masa, kamar bazai d'aukaba saikuma yaciro wayar a aljihu ya diba.
Mamakine ya kamashi dayaga sunan Galadima ta Nigeria, (ko sunzo k'asarne?), da hanzari ya d'auka tana gab da katsewa.
Yanda Galadima yaji muryar yaa marwan yayinda yake amsa masa sallama sai hankalinsa ya tashi, ko gaisuwar kirki basuyiba Galadima ya hau masa tambaya akan Abba.
Yaa marwan yace “gaskiyane ranka ya dad'e, jiya misalin 12pm Abba yayi accident, sunyi taho mu gama da wata thriller, yanzu hakama yana general hospital”.
Zufar dake tsatstsafowa a fuskarsa yasa handkerchief ya share, muryarsa na rawa yace, “Marwan da gaske?”.
Kula yaa marwan yayi Galadima kamar ba a hayyacinsa yakeba, shima muryarsa na rawa yace, “da gaskene ranka ya dad'e”.
“hasbinallahu wani'imal'wakil” Galadima yafara maimaitawa akan la66ansa, ya sauke wayar a hankali zuciyarsa na wani irin suya, yama rasa wane kalar tunani yakamata ace yayi? Yaya zai fassara wannan lamarin? Kenan akwai wani Abu dabai saniba, kodai Abban munaya yanada wata masaniya akan lamarinsa, kokuma bai saniba yafad'a tarko, tabbas yakamata ma akan kansa yay wannan tunanin kodan abinda yayta faruwa tsakaninsa da Munaya, cikin k'araji yace “MUFTAHU!! kasan komai, dolenema kasan komai muftahu!!!, tabbas duk da kasancewarka d'an uwana, jinina, saina binneka da ranka a tsakkiyar masarautarnan inhar mahaifin matata ya rasa ransa wlhy, wannan ALWASHI NANE!!.
ya k'are maganar yana buga table glass dake gabansa da masifar k'arfi, aiko ya tarwatse a wajen, kwalba ta yanka masa hannu. baibi takan ciwon dayaji ba yamik'e a harzuk'e ya d'auki wayar ya fice.
A yanda yafito sai hankali hadimansa ya tashi, ga hannunsa yana d'igar da mini kad'an-kad'an, kuma suna gaisheshi yak'i amsama kowa gaisuwarsa, ko hannun daya saba d'aga musu inbaya buk'atar maganar yau basu samuba, da kansa yabud'e motar yashiga, hakan yasaka sarkin Mora Shiga da hanzari shima shida sauran dogaran dakan bisa in zai fita.
Ko takan zuwa fada yay gaisuwa baibiba, suna fita daga masarautar kiran Nuren yashigo wayarsa.
Yana d'agawa yace, “kajiramu a plaza”. ‘abinda yace kenan kawai ya Yanke wayar'.
Nuren yabi wayar da kallo, inhar kunnensa yajiye masa dai-dai to ran Galadima a matsanancin 6ace yake, to mi aka masa? kokuma shida mutuniyar tasane mama Fulani? Nuren ya girgiza kai kawai yana murmushi, mama Fulani da Galadima sai addu'a kawai, dan tamkar suna ganin hanjin junane.
Tafiyar mintuna 30 takawosu plaza, amma basu shigoba, dan haka Nuren yana hangosu yataso yafito.
Matashin Saurayine shima, mai kama da Galadima sosai, dan wandama bai saniba saiya d'auka tagwayene, abubuwa kad'anne suka banbantasu, dan a shekaruma zasu iya zuwa d'aya, shima Nuren dagani yana cikin Hutu sosai, gashi d'an gaye ajin farko cikin nutsatstsun matasa masu ji da kai.
Da sauri dogari d'aya yafito ya rissina yana gaisheshi, hannu ya d'aga masa cikin sarauta (hakan ya tabbatar min shima jinin sarautar ne) dogarin yabud'e masa inda Galadima yake ya shiga.
Kallo d'aya yayma Galadima ya tabbatar akwai Matsala, hannu yabashi sukayi musabaha, cikin tsantsar kulawa yace, “brother mike faruwa ne?”.
Galadima ya kalli Nuren da idanunsa da suka koma jajaye, cikin matsanancin d'acin zuciya yace, “bansan alak'ar data sashi cikin tawa ba”.
Nuren yace, “waye?”.
Kauda idonsa Galadima yayi daga kallon Nuren, ya maida ga window yana kallon mutane daketa harkokinsu, wani murmushin takaici yayi, sanan yafurta *“SIRIKI!”*
Nuren yazaro idanunsa waje, a zabure yace, “yanzu haka yana ina?”.
“general hospital ”.
Nuren yay hanzarin fad'ama sarkin mota “muje general hospital na garinnan”.
“to ranka ya dad'e”. ‘sarkin mota yafad'a a ladabce.
Hannun Galadima dake d'igar jini har yanzu Nuren ya kamo, ya kalli Galadima da alamar tambayar miya damesa? amma shi galadiman sai yamak'i kallonsa, Nuren ya girgiza kai kawai Dan yasan hakan dayayi bazai fad'aba ne, handkerchief d'insa ya Ciro ya d'aure hannun Na Galadima Dan jinin a samu ya tsaya daga zubar, dukya d'an 6ata seat d'in mortar kad'an, da yake a nan ya ajiye hannun daga gefe. ran Nuren a 6ace yace “brother dolene muyi bincike akan Surukinka, dan duk ta yanda zamu fassara a yanzu, zukatanmu bazasu d'aukaba. zamu iya zargin akwaima hannunsa a ciki, zamu iya zargin sunnemi wani Abu daga garesa yak'i basu had'in kai, zamu iya zargin abubuwa da dama”.
Iska Galadima ya furzar daga bakinsa, yasaka hannu ya tura hularsa baya, kansa ya jingina da kujerar tareda lumshe idanu. zuciyarsa tana tunani yaushene zai kawo k'arshen mak'iyan mahaifinsa? Sai yaushene za'ayi walk'iya yagansu? yana buk'atar sanin dalilinsu Na za6ar maida masa mahaifi haka, miyayi musu?.
Wannan tambayoyin yakema kansa kullu yaumin ta kowacce rana.
Hannunsa Nuren yakamo yad'an matsa, Galadima yabud'e idonsa dasuka fara komawa kalar jaa. “brother a wannan karon bana buk'atar 6acin ranka, dan duk sanda ranka ya6aci baka iya Controlling d'in fushinka, fushinka Na saka aikinmu tafiyar wahainiya, lokaci yayi dazaka saba da irin wad'annan abubuwan fa, karinga saka nutsuwa a zuciyarka aduk lokacin da irin haka tafaru, kamarfa yanda takawa (papi) yake fad'a mana ne a kullum, sufa sunayin wad'annan abubuwanne dan kawai su fusata ka, a haukansu zasu iya samun nasara a kankan saboda ciwon da ALLAH ya jarabceka dashi, waynote kaikuma ka karya wannan kwarin guywar tasu OK?”.
Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, shima ya dafa hannun Nuren d'in yana lumshe idanu, a hankali yace “Okey it's better”.
Daga nan motar ta d'auki shiru, ahaka suka isa asibitin.
Zuwa lokacin jama'ar gidanmu sun kuma cika asibitin, harsu Munubiya duk sunzo suma.
Tunda motocin Galadima uku suka shigo asibitin kallo ya koma Kansu, kowa son ganin mai fitowa yakeyi.
Dogaraine suka fara fitowa, kafin abud'ema su Galadima.
'Yan gidanmu sun fahimci daga masarautane, amma babu Wanda yay tunanin ganin Galadima d'in.
Tunda yafito kwarjininsa da cikar haibarsa ta kasancewarsa jinin sarauta ta cika idanun jama'ar wajen, dogarensa sun tsare ko ina babu mai damar ra6arsa, Nuren na gefen hannun damarsa.
Wayyo, nanfa ido yaymasa caa, baya son kallo ko kad'an, amma yaya zaiyi, tunda jama'a sunga abin kallon.🤦🏻♀
Tunkan ya k'araso su yaa Hameed suka mik'e suka nufoshi. Munubiya kam bayansa kawai take lek'awa, azatonta harda 'Yar uwarta. amma ganin babu alamar mace ma acikinsu sai jikinta yay sanyi.
Hannu Galadima ya d'agama dogaransa alamar su dakata, baya suka ja, yayinda shikuma yamik'ama yaa Shafi'u daya fara k'arasowa hannu, sun gaisa da yayuna cikin girmama juna, kafin sumasa jagora zuwa ciki inda Abba yake.
Dayake su Munubiya suna daga gefene, shiyyasa basu gaisa da Galadima ba, sai k'amshin turarensa daya cika hancinansu.
Dukda halin da ake ciki, saida 'yan gidanmu sukaji Hassada, kowa jitake inama mijin 'yartane🤕🥴.
Humm doctor daya hana kowa ganin Abba saigashi jikinsa Na rawa ya tarbi Galadima, daddy da baba k'arami sunje gida suyo wanka, bayan dawowar su yaa Naseer sai sukuma suka tafi.
Doctor yama Galadima jagora har d'akin da Abba yake kwance. “Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un” kawa Galadima ke iya fad'a a la66ansa, maganar gaskiya jikin Abba babu k'yawun gani, yaa Shafi'u ma mai ragguwar zuciya kasa daurewa yayi yafice da sauri yana hawaye, yaa Hameed kam runshe ido yayi zuciyarsa Na suya kamar zata fad'o k'asa.
Galadima ya dafe bango tareda rik'e kansa dayaji ya sara masa, halin da Abba yake ciki exactly dana Alhaji Abdus'salam Abba.
Da sauri Nuren yaruk'o hannunsa, a hankali yake fad'in “Control yourself please”.
Doctor yajawo kujera biyu yabama Galadima da Nuren dansu zauna.
Ina kasa zaman sukayi, dole suka fito. Galadima yabuk'aci ganin doctor d'in.
'Yan gidanmu kuwa fitowar yaa Shafi'u yana share hawaye yasaka zukatansu kuma tashi, caa sukayo kansa da tambayar lafiya.
Kasa magana yayi, ahaka su Dady suka samesu, sukansu jiki a sanyaye suka k'araso wajen, kardai ace d'an uwansu yatafi ya barsune. muryoyinsu har rawa sukeyi wajen tambayar lafiya?.
Sai alokacin yaa shafi'u yasamu bakin maganar cemusu bafa rasuwa yayiba, jikinnasane sai babu dad'in kallo.
Baba k'arami yace, “sun bari kun gansane?”.
“Eh baba, Galadima ne mijin Munaya yazo”.
Dady da baba k'arami ciki suka shiga, sukabar 'yan gidanmu dake kuka abin gwanin tausayi.