Sashe 22
Raina Kama Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda Aryaan ya shigo da gudu inna ta tareshi tana fad'in “kai lafiya? minene na gudu?”.
“innarmu wlhy Uncle ne yace ki shirya mana kayanmu ni da Aiyaan zai aiko gobe a kaimu wajen Auntynmu”.
Inna tayi d'an murmushi kawai, dan ita bata d'auki maganarma serious ba.
Su dai su Aiyaan sunata murnarsu, sun tafi d'aki sun hau had'a kaya.
Babu dad'ewa da yin haka saiga daddy ya shigo da sallama, inna ta amsa masa tana gyara zama, shima zama yay kujerar dake kusada k'ofa, ganin haka inna ta fahimci da magana yazo, dan haka ta maida dukkan hankalinta Kansa.
Bayani yamata dalla-dalla akan zancen da su Galadima sukazo dashi, ya d'ora da fad'in “saiki shirya dan zamuje ai miki passport”.
Inna tace, “amma dadynsu nake ganin ai da kud'in kukaje kamar zaifi”.
Murmushi Dady yayi, yace “Ai'sha nasan miyasa kikeso zamewa, to ai kaf cikin matan yayan kece ya cancanta kije koda ace bawai Galadima ne ya biyaba, maganar ciwo Muke bawai jin dad'i ko gutsiri tsomar wasu ba, ki shirya dan zai turo wanda zamuje immigration office d'in”. daga haka ya tashi ya fice.
Shiru kawai inna tayi, itadai inda ta itace da antafi da ko innaro, dan tasan wannan tafiyar dukda ta ciwoce sai ta janyo 6acin rai a gidan.
Aiko tamkar inna tasani, dan ana fad'ama innaro tace “bata amince ba, ita ta haifi auwalu kuma da ita za'aje tayi jiyyar yaronta, bazata bama kowacce mace acikinsu wannan ragamarba.
Shiru baba k'arami da daddy sukayi, taci masifarta ta gama tayi shiru.
Baba k'arami yace, “amma dai inna kinsan jinyar Yaya sai da matarsa a kusa, kekuma k'arfinki ya k'are ya za'a d'ora miki d'awainiyar da matansa ne keda hakki a kai?”..
“yo d'awainiya ba tare da kai za'a tafiba? Kai basai kamasa ba. ni dai fa ban amince Ai'sha tajeba, dan wlhy bazan ta6a son Ai'sha ba komi zata zama, tunda dai ta silar jikokinane balle amin ilimi. k'ilama itace ta jefeshi dan taga ta kama k'asa 'yarta Na auren d'an Sarki, t........”.
“innaaaa! haba mana, dan ALLAH karma ki bari maganar nan ta fita, waishin minene laifin Ai'sha a gareki? duk cikin matanmu banga wadda take girmamaki da d'aukarki matsayin uwaba irinta, inna ya kamata wannan k'iyayyar ta koma soyayya hakanan, a baya kince dan basuda asali, kin dawo kince juya ce bata haihuwa, gashi kuma yanzu har ALLAH zai fidda jikoki daga tsatsonta, to miye kuma matsalar?”.
“toko zaka shak'eni Na fad'a makane Hameesu?”.
“a'a inna, ALLAH yabaki hak'uri”.
“kaidai ka Sani, ni yanzu bara Na tashi Na shirya Ku kaini inama kace, imagesa nema ko uwarmi oho”.
Daga Dady har baba k'arami babu Wanda ya tanka mata, tana shigewa baba k'arami ya mik'e yana cema dady “yaya ka jireta, bara naje mutafi da maman 'yan biyun, kota fito kace naje shiryawa ne”.
Kai Dady ya kad'a masa yana murmushi, baba k'arami ya fita da hanzari.
Bayan wasu mintuna saiga innaro an fito ana warware gyale za'a yafa, “yauwa jafaru muje Na shirya”.
Habiba dake kitchen tana girki duk diramar da ake tana saurare ta tuntsure da dariya, lallai tsohuwarnan akwai daru, mama Na hanya ai, itace maganinki (gwaggo Safiyya mamarsu).
Kallonta Dady yay yana murmushi, yace “to inna mu jira jafar d'in yaje shiryawa”.
“ato shikenan bara kafin ya dawo nad'anci abinci, k! Habiba zubomin idan abincin nan ya tsotse, gara Na fita cikina da d'an nauyi”.
Habiba ta had'iye dariyarta sannan tace “innaro bai tsotseba, amma nanda kamar dai minti 5”.
“babu damuwa ai, nasan jafaru ma bai dawoba harnaci, kinsan shi da dak'undar shiri, ya tsufa amma kullum kallon kansa yake sa'ar Abdul-hameedu”.
Dariya Dady ya had'iye da k'yar, yasa handkerchief yana toshe baki dan karta fito.
★★★★★★★★
Tsaf na kammala shiryawa sannan Na kimtsa d'akin, ni dukfa a nufina nayi shirin asibitine.
Fitowa nayi dan naga ko yana falone, wayam babu kowa, sai sallama da nakeji a bakin k'ofar, amasawa nayi na bada izinin shigowa saboda naji muryar matane.
Su 10 ciff suka shigo, k'asa suka zube suna gaisheni, Na amsa musu da 'yar sakewa, “lafiya dai?”.
“lafiya lau ranki ya dad'e, mune zamu kasance hadimanki, masu miki dukkan hidima.
Nifa wlhy banason wasu bayi, amma dolene Na barsu tunda wad'ancanma Galadima ne yace su tafi, yanzu kuma baya wajen, ni kuma banida ikon korarsu tinda bansan kan abinba.
Amsa musu nayi da “to” sannan nawuce Na zauna a kujera.
Tasowa sukai suka biyoni, a tsanake suka dinga fad'amin sunansu da aiyukan da zasuyi.
Wad'anda naga bazan iya yarda suyiba Na canja musu aiki. Sallamarsu nayi, Ina k'ok'arin tashi Na shige ciki saiga Sauban ya shigo, duk zubewa sukayi suna kwasar gaisuwa a gareshi, ya amsa musu yana wani yatsine face, sai kuma ya basu izinin tafiya, fita sukayi harabar sashenmu.
Na kalleshi ina murmushi, “ashe kaima dai sarautar Na jininka yaa Sauban? Wanda bai saniba saiya d'auka duk bazaka iya wani Abu daya shafi sarautaba”.
Dariya yayi yana zama, “aunty gimbiyar mu kenan, wannan ai sai mijinki”.
Nima murmushi nayi kawai.
Ya mik'omin kayan hannunsa yana fad'in “ga break fast d'inki”..
“wayyo yaa Sauban, nikam dai nagaji da ciye-ciyennan ma, zuwa zanyi Na fara abinci da kaina”.
“wlhy dakin taimakemu Aunty gimbiya, mijinki shiya saba da cin abincin waje shiyyasa bai damu ba, ya kamata kafin Na wuce gobe naci girkinki”.
“kamarya gobe? Kana nufin zaka koma kenan?”.
“tab da gudu kuwa, aini bazan iya zaman k'asarnanba Na tsawon lokaci, tarema zamu wuce da Abba ai, harma da innarmu, yaa Sam bai sanar dakeba kenan?”.
Baki bud'e Na girgiza masa kai alamar a'a.
Sauban yay murmushi, “kinsan halin Galadiman namu ai, soyake yamiki surprise maybe, yanzu hakane yaje cuku-cukun visa d'insu ne. waito miyasa bazamu koma tare da kubane?”.
Murmushin yak'e nayi, nace, “maybe akwai ayyukan dabai gamaba shiyyasa”.
“inaga hakanne kam, ni bara naje, yace Na iskeshi birnin gayu, ga mahfuz can Na jirana”.
“ok sai kun dawo” Na iya cewa, danni daga 'yan matan masarautar har samari ba kowa Na saniba, tunda time d'in daya kamata nad'an San mutane sai muka tafi India. ni bama nason Na saba da kowa, ni da ba zama ya kawoni ba.
Maganar fita da Abba da Galadima yakeyi sai yayta cin zuciyata, kimar Galadima da darajarsa saita cika zuciyata, inason mahaifana, kuma dukkan Wanda zai nuna musu kulawa bazan manta da shiba, harda 'Yar kwallata Na share, Na tashi Na koma bedroom ba tare da nayi break fast d'inba ma.
*****************************
Innaro dai tun ana jiran dawowar baba k'arami harta fara gyangyad'i, habiba data kammala abincin ta d'ebo ta kawo mata, nuni Dady yay mata akan ta koma.
Habiba ta koma da baya ba tare da ta k'araso falonba.
Tun tana gyangyad'i harta 6ingire a kujerar barci mai nauyi ya d'auketa (ho innaronmu ta mutunci🤸🏻♀😜).
Baba k'arami da innarsu munaya kam tuni sunyi ficewarsu, dayake Abu Na kud'i dandanan aka gama cuku-cukun komai, Nuren ne tsaye, saida komai ya daidaita suka samu visa d'insu a hannu sannan suka fito.
Har gida ya maidosu ya koma suna jera masa godiya da addu'a shi da Galadima.
Innaro daga gyangyad'in jiran abinci ya tsotse aka zarce da barci mai nauyi, shima Dady lalla6awa yay ya fito dan asibiti zaije.
Tafiyarsa babu dad'ewa saiga gwaggo Safiyya ta iso da yaranta biyu.
Hayaniyar su Dahiru ita ta tada innaro, ta mik'e zumbur tana fad'in “yauwa Jafaru kadawo mu tafi ko? Habiba bar abincin kawai idan muka dawo naci.
Mi Dahiru da Naja'atu zasu ba dariya ba, suka shiga shek'ama innaro dariyar shak'iyanci. Wai kota kwanta da yunwa ne.
Zaginsu ta hau yi ta d'auki filon kujera tana dukansu.
Sai da gwaggo Safiyya ta musu magana sannan suka nutsu, “inna ina zakuje da Jafaru ne?”.
Gyara zama innaro tayi tashiga bama gwaggo Safiyya labari.
Murmushi kawai gwaggo Safiyya tayi, danta gane wayo suka mata suka gudu kawai, itama sai tace “to inna ki cigaba da jiransu, k'ila dan sunga kina barcine suka jira ki tashi sannan Ku tafi.
Da wannan gwaggo Safiyya ta rufe bakin innaro ta zauna jiran su dady.
Aiki🤣🤣😝.
**********
Galadima daya fita kai tsaye asibiti ya nufa, su yaa hameed kawai ya iske can, dan dady ya hana matan gidan zuwa sai anjima, doctors Na complain akan suna cika wajen da yawa.
Cikin mutunta juna Galadima ya gaisa dasu yaa sabi'u sannan yashiga yaga daddy.
Yau kam Alhmdllh dan ba barci yakeba, kumbirin fuskarsa kuma yad'an sa6e kad'an, saidai baya iya magana sai dai yayta bin mutane da idanu.
Dukda bazai iya amsawa ba haka Galadima ya risinna ya gaidashi, tare da masa fatan samun lafiya sannan ya fita office d'in doctor.
Bayan sun gaisa doctor ya bama Galadima file d'in bayanan Abba dasuka tattara.
Kar6a Galadima yayi ya duba, dukda bawai ya fahimci bayanan bane, ( kusan dai rubutun doctors sai su). Suka d'an tattauna akan cigaban da aka samu sannan Galadima ya fito.
Ya iske daddy ya iso, suka gaisa sannan yamasa dukkan bayanan da doctor yamasa shima. Dady ma yaji dad'in cigaban da aka samu.
Galadima yay musu sallama ya fito.
Guntun tsaki yaja saboda yanda jama'a suka wani zuba masa idanu tamkar sunga magiji, da sauri wani dogari ya bud'e masa motar ya shiga, sannan suma suka shiga.
Daga asibiti Galadima yace su wuce birnin gayu plaza.
Cike da girmamawa sarkin mita ya amsa da to.
Maida kansa yayi jikin seat ya kwanta tareda lumshe idanu ya fad'a duniyar tunani................✍🏼
Barkanku da juma'a💋💋💋🤝🏻.
Musha weekend lafiya sisters⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀😄.
*_ALLAH ka gafartama iyayen mu_*🙏🏻😭
[7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_*
*_Haske writer's asso...._*💡
*_♦RAINA KAMA......♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻
“innarmu wlhy Uncle ne yace ki shirya mana kayanmu ni da Aiyaan zai aiko gobe a kaimu wajen Auntynmu”.
Inna tayi d'an murmushi kawai, dan ita bata d'auki maganarma serious ba.
Su dai su Aiyaan sunata murnarsu, sun tafi d'aki sun hau had'a kaya.
Babu dad'ewa da yin haka saiga daddy ya shigo da sallama, inna ta amsa masa tana gyara zama, shima zama yay kujerar dake kusada k'ofa, ganin haka inna ta fahimci da magana yazo, dan haka ta maida dukkan hankalinta Kansa.
Bayani yamata dalla-dalla akan zancen da su Galadima sukazo dashi, ya d'ora da fad'in “saiki shirya dan zamuje ai miki passport”.
Inna tace, “amma dadynsu nake ganin ai da kud'in kukaje kamar zaifi”.
Murmushi Dady yayi, yace “Ai'sha nasan miyasa kikeso zamewa, to ai kaf cikin matan yayan kece ya cancanta kije koda ace bawai Galadima ne ya biyaba, maganar ciwo Muke bawai jin dad'i ko gutsiri tsomar wasu ba, ki shirya dan zai turo wanda zamuje immigration office d'in”. daga haka ya tashi ya fice.
Shiru kawai inna tayi, itadai inda ta itace da antafi da ko innaro, dan tasan wannan tafiyar dukda ta ciwoce sai ta janyo 6acin rai a gidan.
Aiko tamkar inna tasani, dan ana fad'ama innaro tace “bata amince ba, ita ta haifi auwalu kuma da ita za'aje tayi jiyyar yaronta, bazata bama kowacce mace acikinsu wannan ragamarba.
Shiru baba k'arami da daddy sukayi, taci masifarta ta gama tayi shiru.
Baba k'arami yace, “amma dai inna kinsan jinyar Yaya sai da matarsa a kusa, kekuma k'arfinki ya k'are ya za'a d'ora miki d'awainiyar da matansa ne keda hakki a kai?”..
“yo d'awainiya ba tare da kai za'a tafiba? Kai basai kamasa ba. ni dai fa ban amince Ai'sha tajeba, dan wlhy bazan ta6a son Ai'sha ba komi zata zama, tunda dai ta silar jikokinane balle amin ilimi. k'ilama itace ta jefeshi dan taga ta kama k'asa 'yarta Na auren d'an Sarki, t........”.
“innaaaa! haba mana, dan ALLAH karma ki bari maganar nan ta fita, waishin minene laifin Ai'sha a gareki? duk cikin matanmu banga wadda take girmamaki da d'aukarki matsayin uwaba irinta, inna ya kamata wannan k'iyayyar ta koma soyayya hakanan, a baya kince dan basuda asali, kin dawo kince juya ce bata haihuwa, gashi kuma yanzu har ALLAH zai fidda jikoki daga tsatsonta, to miye kuma matsalar?”.
“toko zaka shak'eni Na fad'a makane Hameesu?”.
“a'a inna, ALLAH yabaki hak'uri”.
“kaidai ka Sani, ni yanzu bara Na tashi Na shirya Ku kaini inama kace, imagesa nema ko uwarmi oho”.
Daga Dady har baba k'arami babu Wanda ya tanka mata, tana shigewa baba k'arami ya mik'e yana cema dady “yaya ka jireta, bara naje mutafi da maman 'yan biyun, kota fito kace naje shiryawa ne”.
Kai Dady ya kad'a masa yana murmushi, baba k'arami ya fita da hanzari.
Bayan wasu mintuna saiga innaro an fito ana warware gyale za'a yafa, “yauwa jafaru muje Na shirya”.
Habiba dake kitchen tana girki duk diramar da ake tana saurare ta tuntsure da dariya, lallai tsohuwarnan akwai daru, mama Na hanya ai, itace maganinki (gwaggo Safiyya mamarsu).
Kallonta Dady yay yana murmushi, yace “to inna mu jira jafar d'in yaje shiryawa”.
“ato shikenan bara kafin ya dawo nad'anci abinci, k! Habiba zubomin idan abincin nan ya tsotse, gara Na fita cikina da d'an nauyi”.
Habiba ta had'iye dariyarta sannan tace “innaro bai tsotseba, amma nanda kamar dai minti 5”.
“babu damuwa ai, nasan jafaru ma bai dawoba harnaci, kinsan shi da dak'undar shiri, ya tsufa amma kullum kallon kansa yake sa'ar Abdul-hameedu”.
Dariya Dady ya had'iye da k'yar, yasa handkerchief yana toshe baki dan karta fito.
★★★★★★★★
Tsaf na kammala shiryawa sannan Na kimtsa d'akin, ni dukfa a nufina nayi shirin asibitine.
Fitowa nayi dan naga ko yana falone, wayam babu kowa, sai sallama da nakeji a bakin k'ofar, amasawa nayi na bada izinin shigowa saboda naji muryar matane.
Su 10 ciff suka shigo, k'asa suka zube suna gaisheni, Na amsa musu da 'yar sakewa, “lafiya dai?”.
“lafiya lau ranki ya dad'e, mune zamu kasance hadimanki, masu miki dukkan hidima.
Nifa wlhy banason wasu bayi, amma dolene Na barsu tunda wad'ancanma Galadima ne yace su tafi, yanzu kuma baya wajen, ni kuma banida ikon korarsu tinda bansan kan abinba.
Amsa musu nayi da “to” sannan nawuce Na zauna a kujera.
Tasowa sukai suka biyoni, a tsanake suka dinga fad'amin sunansu da aiyukan da zasuyi.
Wad'anda naga bazan iya yarda suyiba Na canja musu aiki. Sallamarsu nayi, Ina k'ok'arin tashi Na shige ciki saiga Sauban ya shigo, duk zubewa sukayi suna kwasar gaisuwa a gareshi, ya amsa musu yana wani yatsine face, sai kuma ya basu izinin tafiya, fita sukayi harabar sashenmu.
Na kalleshi ina murmushi, “ashe kaima dai sarautar Na jininka yaa Sauban? Wanda bai saniba saiya d'auka duk bazaka iya wani Abu daya shafi sarautaba”.
Dariya yayi yana zama, “aunty gimbiyar mu kenan, wannan ai sai mijinki”.
Nima murmushi nayi kawai.
Ya mik'omin kayan hannunsa yana fad'in “ga break fast d'inki”..
“wayyo yaa Sauban, nikam dai nagaji da ciye-ciyennan ma, zuwa zanyi Na fara abinci da kaina”.
“wlhy dakin taimakemu Aunty gimbiya, mijinki shiya saba da cin abincin waje shiyyasa bai damu ba, ya kamata kafin Na wuce gobe naci girkinki”.
“kamarya gobe? Kana nufin zaka koma kenan?”.
“tab da gudu kuwa, aini bazan iya zaman k'asarnanba Na tsawon lokaci, tarema zamu wuce da Abba ai, harma da innarmu, yaa Sam bai sanar dakeba kenan?”.
Baki bud'e Na girgiza masa kai alamar a'a.
Sauban yay murmushi, “kinsan halin Galadiman namu ai, soyake yamiki surprise maybe, yanzu hakane yaje cuku-cukun visa d'insu ne. waito miyasa bazamu koma tare da kubane?”.
Murmushin yak'e nayi, nace, “maybe akwai ayyukan dabai gamaba shiyyasa”.
“inaga hakanne kam, ni bara naje, yace Na iskeshi birnin gayu, ga mahfuz can Na jirana”.
“ok sai kun dawo” Na iya cewa, danni daga 'yan matan masarautar har samari ba kowa Na saniba, tunda time d'in daya kamata nad'an San mutane sai muka tafi India. ni bama nason Na saba da kowa, ni da ba zama ya kawoni ba.
Maganar fita da Abba da Galadima yakeyi sai yayta cin zuciyata, kimar Galadima da darajarsa saita cika zuciyata, inason mahaifana, kuma dukkan Wanda zai nuna musu kulawa bazan manta da shiba, harda 'Yar kwallata Na share, Na tashi Na koma bedroom ba tare da nayi break fast d'inba ma.
*****************************
Innaro dai tun ana jiran dawowar baba k'arami harta fara gyangyad'i, habiba data kammala abincin ta d'ebo ta kawo mata, nuni Dady yay mata akan ta koma.
Habiba ta koma da baya ba tare da ta k'araso falonba.
Tun tana gyangyad'i harta 6ingire a kujerar barci mai nauyi ya d'auketa (ho innaronmu ta mutunci🤸🏻♀😜).
Baba k'arami da innarsu munaya kam tuni sunyi ficewarsu, dayake Abu Na kud'i dandanan aka gama cuku-cukun komai, Nuren ne tsaye, saida komai ya daidaita suka samu visa d'insu a hannu sannan suka fito.
Har gida ya maidosu ya koma suna jera masa godiya da addu'a shi da Galadima.
Innaro daga gyangyad'in jiran abinci ya tsotse aka zarce da barci mai nauyi, shima Dady lalla6awa yay ya fito dan asibiti zaije.
Tafiyarsa babu dad'ewa saiga gwaggo Safiyya ta iso da yaranta biyu.
Hayaniyar su Dahiru ita ta tada innaro, ta mik'e zumbur tana fad'in “yauwa Jafaru kadawo mu tafi ko? Habiba bar abincin kawai idan muka dawo naci.
Mi Dahiru da Naja'atu zasu ba dariya ba, suka shiga shek'ama innaro dariyar shak'iyanci. Wai kota kwanta da yunwa ne.
Zaginsu ta hau yi ta d'auki filon kujera tana dukansu.
Sai da gwaggo Safiyya ta musu magana sannan suka nutsu, “inna ina zakuje da Jafaru ne?”.
Gyara zama innaro tayi tashiga bama gwaggo Safiyya labari.
Murmushi kawai gwaggo Safiyya tayi, danta gane wayo suka mata suka gudu kawai, itama sai tace “to inna ki cigaba da jiransu, k'ila dan sunga kina barcine suka jira ki tashi sannan Ku tafi.
Da wannan gwaggo Safiyya ta rufe bakin innaro ta zauna jiran su dady.
Aiki🤣🤣😝.
**********
Galadima daya fita kai tsaye asibiti ya nufa, su yaa hameed kawai ya iske can, dan dady ya hana matan gidan zuwa sai anjima, doctors Na complain akan suna cika wajen da yawa.
Cikin mutunta juna Galadima ya gaisa dasu yaa sabi'u sannan yashiga yaga daddy.
Yau kam Alhmdllh dan ba barci yakeba, kumbirin fuskarsa kuma yad'an sa6e kad'an, saidai baya iya magana sai dai yayta bin mutane da idanu.
Dukda bazai iya amsawa ba haka Galadima ya risinna ya gaidashi, tare da masa fatan samun lafiya sannan ya fita office d'in doctor.
Bayan sun gaisa doctor ya bama Galadima file d'in bayanan Abba dasuka tattara.
Kar6a Galadima yayi ya duba, dukda bawai ya fahimci bayanan bane, ( kusan dai rubutun doctors sai su). Suka d'an tattauna akan cigaban da aka samu sannan Galadima ya fito.
Ya iske daddy ya iso, suka gaisa sannan yamasa dukkan bayanan da doctor yamasa shima. Dady ma yaji dad'in cigaban da aka samu.
Galadima yay musu sallama ya fito.
Guntun tsaki yaja saboda yanda jama'a suka wani zuba masa idanu tamkar sunga magiji, da sauri wani dogari ya bud'e masa motar ya shiga, sannan suma suka shiga.
Daga asibiti Galadima yace su wuce birnin gayu plaza.
Cike da girmamawa sarkin mita ya amsa da to.
Maida kansa yayi jikin seat ya kwanta tareda lumshe idanu ya fad'a duniyar tunani................✍🏼
Barkanku da juma'a💋💋💋🤝🏻.
Musha weekend lafiya sisters⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀😄.
*_ALLAH ka gafartama iyayen mu_*🙏🏻😭
[7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_*
*_Haske writer's asso...._*💡
*_♦RAINA KAMA......♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻