← Book details Raina Kama Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 76

Sashe 3

Raina Kama Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Misalin 8:pm saiga Sa'eed yazo gidanmu, a time d'in gwaggon Haleematu da mamansu yaa Hameed suna ta hayaniyar fad'a, wai mamansu yaa Hameed ce takama gwaggon Haleematu tana kallon Zarah dake alwala a fanfo tana dariya.
Shinefa mamansu yaa Hameed tace gwaggon Haleematu taci kanta tasha bak'in ruwa, karta lashe mata jika tun yana a ciki.
Wannan kalma ta mamansu yaa Hameed itace tajawo fad'a, Dan gwaggon Haleematu tace mamansu yaa Hameed tace mata mayya bazata yardaba. Fad'a sosai sukeyi suna cin zarafin juna da gori, dama kowa kishi Na cinta a zuciya.
Matan gidanmu duk sunyo waje anrasa masu dakatar dasu sai innarmu dake cewa suyi hak'uri Dan ALLAH, darene fa.
Amma Sam sunk'i saurarenta.
Innaro dataji hayaniyar tundaga gidanta yasata d'akko fayafi tafito, kamar anjehota haka tashigo gidan.
Sa'eed da Sulaiman suna awaje a mota, duk badak'alar da akeyi daga cikin gidanmu suna jiyowa, har shigar innaro kuwa suna kallo. Dayake su Abbanmu suna masallaci.
Innaro tanata magana sunk'i saurarenta, saiyi sukema kamar zasu fara danbe.
Mamansu yaa Hameed Na k'ok'arin kwalama gwaggon Haleematu ludayin miya dake hannunta innaro takawo jiki zata kare sai a goshinta, jikake kwarrrr!.
Tako dafe goshi tafasa k'ara..
Hakan kuma yay dai-dai da shigowar su Abba gidan, su duka ukun, tunkan sushigo sukejiyo hayaniyar dama, dukansu rai a 6ace suka shigo. Dan iskancin matan nasu ya ishesu hakanan, idonsu yarufe ko ganin motar su Sa'eed basuyiba.
Ran Abba yakuma 6aci, Dan ganin duk matansa ne ma masu hayaniyar, ga abinda sukaima mahaifiyarsa akan idonsa. batareda yabi ba'asiba yace duk sufice su bar masa gida.
Ananne kowa yay tsitt, yadaka musu tsawa yana fad'in wlhy idan basu fitaba zaisa a fiddasu, ko d'akunansu bai yarda wata takomaba kuma.
Dole sai 'ya'yansu suka d'akko musu hijjabai suna kuka da bama Abban hak'uri.
Amma yak'i sauraren kowa, daddy da baba k'arami kuwa babu Wanda yay yunk'urin hanashi.
Innarmu tamatsa kusadashi tana rok'onsa karyayi haka, yazauna ya sauraresu tukunna, Hararar daya zuba matace yasata jada baya tai 6am da bakinta.
Innaro kuwa maman safara'u ce takamata ta zaunar, goshi harya fara kumbura🙆🏻.

(((+)))***(((+)))***(((+)))

Kafin mu baro asibitin nama manta da maganar mama Fulani, saboda murnar bud'e ido da Abie yayi ta d'aukema kowa hankali kuma, gaskiya ina tausayin bawan ALLAHn nan sosai.
yauma bamuyi k'asa a guywa ba wajen cigaba da addu'oin damukeyi cikin zam-zam ni da Galadima, somuke muyi na 1week sannan afara bashi.

Washe gari Alhmdllh jikin Abie yayi k'yau sosai, Dan inka gaidashi yakan maka murmushin sa Na dattako, hakan ya sanya su papi sukayi shirin tafiya da yamma.
Ni da Galadima da Sauban muka musu rakkiya, sainaji tamkar nabisu. Harda 'yar kwallata kuwa. Inno tanata tsokanata, Dan tsohuwar tashiga raina sosai.
Tunda muka d'akko hanyar dawowa asibitin nakife kaina a cinya inata hawaye, sauban ne kawai ke tsokanata, amma Galadima tamkarma baya cikin motar. hakan saiya k'ara tunzura zuciyata, nakuma k'ara k'arfin kukan nawa.

Sauban yasamu guri yay parking, da hannu Galadima yamasa alamar yaje.
Fita yay yana k'uk'uni da k'umshe dariya, wai “su boss za'ayi lallashi shine aka koroni”. Saida yay nisa da motar sannan yasami damar dariyar, har yashiga wajensu Momma.
Daga Momma har Aunty Mimi kalli
onsa sukeyi,, aunty Mimi tace, “Auta lafiyarka kuwa?”.
Saida ya zauna sannan yashiga kora musu bayani, dariya kawai sukayi, sunsan Sauban babu sauk'i wajen taso mutum agaba.

Tunda Sauban ya fita sai Galadima ya gyara zamansa kawai ya zubamin ido, mutum ne shi dabaya son shiga hak'in wani, ko kad'an baiso ace wane yana cikin damuwa ta dalilinsa......
Wayarsa aka kira, ya kalli wayar kafin yakai hannu ya d'auka, salamar da akayi daga can ya amsa suka gaisa.
Jin ya ambaci Nuren nagane da Wanda suka ta6a yin waya kwanakine, nad'an tsagaita da kukan ina sauraren mizasu tattauna. Galadima naji yace,
“miya farune kakeson nazo Nigeria haka da gaggawa Nuren”.
“no babu wani damuwa, driver da yarinyar nanfa suna hannu, so yakamata ka shigo muyi abinda yadace ko?”.
“ok babu damuwa, insha ALLAH zuwa Wednesday idan jikin Abie ya kuma lafawa zan shigo”.
“O right, ALLAH ya k'ara masa lafiya, a gaishesu”.
“zasuji insha ALLAH, bye”.
Wayar ya ajiye a tsakkiyarmu ya maida hankalinsa kaina.

Cikin wani salo yace, “Munaaya!”.
Wani Yarr naji a jikina, karo na biyu kenan danaji sunana a bakinsa, sainaji sunan nawa ya canja kamar ba shiba, danya iya sarrafa sunan a harshensa..... ganin ban d'agoba yakuma kiran sunan.
Kasa jurewa nayi nad'ago idona na kallesa, ganin ya tsareni da idanu saina janye nawa. yad'an lumshe nasa ya bud'e a kaina ya furzar da huci “kina ganin haka abokai yakamata su kasance? ni friend nakine, miyasa bazaki iya fad'amin damuwarki ba? kiyi hak'uri nasan kina buk'atar zuwa gida, last week naso maidaki Nigeria, amma sai jikin Abie Daya motsa ya dakatar dani”.
Tausayi yabani, nad'ago na kallesa, mutumne shi mai sauk'in kai, saidai idan baka fahimceshi ba zaka sameshi a amurd'e, domin yanada wahalar sha'ani, hawayen dasuka ziraromin na goge, muryata na rasa nace, “kayi hak'uri ina kewar su Munubiya ne, insha ALLAH bazan sake yin kukanba amma”.
Murmushi yaymin yana jinjina kai, yad'an shafa girarsa zuwa kai sannan yace, “kinada tsiwa, amma wani time d'in kinada kirki”.
Bansan lokaci da dariya tazominba, nad'an dara sannan nace kaima ai hakan kake, kanada tsauri kanada sauk'i”.
Yawani k'ank'ance idanu cikin wani salon kallon yace, “really?”.
Gira d'aya na d'aga masa nima nace, “yaah”.
Murmushi mai k'ayatarwa yayi yakwashi wayoyinsa yabud'e motar yafita batare data sake cewa komaiba.
Ganin haka nima saina fito fuskata washe da murmushi, kamar banice nagama kukan shagwa6a ba😉.
Tunda muka shigo aunty Mimi da Momma suka zubo mana ido, Sauban kam dariyar shak'iyanci yafara k'asa-k'asa.
Momma tace, “ina kuka mak'ale haka?”.
Murmushi yayi yana zama kujerar dake kusada Abie yace, “ba ko ina Momma”..
Momma tayi 'yar dariya tace, “shikenan tunda ba'aso muji”.
Sauban da Aunty Mimi ma dariya sukayi, nikam kunya tasani k'asa da kaina inad'an murmushi.

__((*))__((*))__((*))__((*))__

Abba dai bai yarda su maman yaa Hameed su kwana a gidanba, a daren kowacce tanufi gidansu, yayinda baba k'arami ya d'auki innaro zuwa asibiti.
Su Sa'eed kam zare jiki sukai suka koma gida, zukatansu tab da mamakin wannan lamari.

A ranar zarah sai sashenmu ta kwana a tsohon d'akinmu ni da munubiya, saboda Aminu ya sanar mata yaga Sa'eed da mijin Siyama a k'ofar gidanmu.
Gaba d'aya saitaji yau tanajin haushin mamansu, dan daba ta tanka dariyar da gwaggon Haleematu tamata ba ai dabasuyi rigima har Abba ya korasu gidaba, dayanzu gidanta zata kwana jikin mijinta itama, wane irin abin kunyane wannan kai kana gida uwarka na gidansu itama🤦🏻‍♀.

%%%%%%%%%%%%%%%

Dawowarmu kenan ni da Sauban da Samha daga zagaya gari, nagaji ovar, jikina sai ciwo yakemin, dama Yaya lafiyar giwa, saman sofa na zube Ina sauk'i numfashin wahala, wani zazza6ima nakejin yana neman rufeni, harna rufe idanu naji wayata na wringing, lalubowa nayi na duba mai kirana, nasan dai duk Wanda zai kirani to daga Nigeria ne, dan su Samha duk suna gida, Galadima kam bai ta6a kirana a wayaba, banmayi tunanin yanada number ba duk da shine ya sayi layin.
Sunan munubiya dana gani yasani fad'ad'a murmushina, saida nabari ya katse sannan na kirata.
Bugu biyu ta d'aga, jin muryarta can k'asa sai hankalina ya tashi, nashiga tambayarta ko lafiya.
“sweetheart wlhy banajin dad'i, ko school nakai sati banjeba, ya kuke?”.
“ayya sorry sweetheart, mike damunki?”.
“wlhy zazza6i, kema naji muryarki wata iri ai?”.
“nima lafiyar sai a slow wlhy, ina yaa marwan?”.
“tofa, ciwo a time d'aya mu duka? ALLAH yabamu lafiya to, yaa marwan yafita gaida su mama, ya jikin Abie da Galadima?”.
“everything Alhmdllh dear, jikin Abie ma yanata sauk'i, sun fara masa amfani da addu'oin, amma naji kamar doctors d'inshi suna complain wai abar shafa masa abinda ake shafa masa”.
“karku wani sauraresu, Ku cigaba kawai, ALLAH yasa muji alkairi”.
“insha ALLAH dear, dama haka Galadima yace shima”.
“ALLAH ubangiji yabashi lafiya, bara na barki ki huta, a gaida minsu”.
“ok sweetheart bye”.

Ina ajiye wayar na mik'e, bayi nashiga nahad'a ruwa mai zafi nagasa jikina kozanji dad'i, haka nake kusan yini wanka da ruwan zafi, wai ko zan dainajin ciwon jiki, amma a banza, danayi wanka bana wuce mintuna talatin ciwon yake dawowa sabo.
Wani ash d'in wando da Riga na jawo na saka, kayan basuda nauyi sosai, wandon kad'an yawuce guywata, rigar kam hannunta iya kafad'a ya tsaya, kamardai vest d'in maza take, saidai daga gaba tanada banbanci data maza. nasan Galadima bazai dawo gidan yanzuba saboda koya tashi aiki saiya biya ta asibiti kafin yazo gida, yanzu kuma akayi isha'i nasan sai zuwa irin 11, shiyyasa nayi tunanin sakasu ko zan ragema kaina nauyin jikin. komawa nayi saman sofa data zama gadona na kwanta, amma sai naji dukna takura, najujjuya naji babu dad'i kwanciyar, tsaki nayi namik'e nakoma saman gadon na kwanta, insha ALLAH kafin maishi yadawo dai natashi😏.
Banfi 5minutes ba da kwanciya barci ya d'aukeni.
Chapter 3 · 0% Book details