Sashe 16
Raina Kama Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu dad'ewa saiga 'yan gidanmu nata shigowa, yanda kowanne fuskarsa ke a washe sai suka bani mamaki, nakasa hak'uri nace, “Abba ne ya tashi? kuke farin ciki haka?”.
“shima insha ALLAH zai tashi 'Yar albarka”. Cewar innaro tana dariya.
Ni duk sun kuma d'auremin kai da addu'ar da sukeyi suna fad'in ALLAH ya inganta.
Mamansu Fauziyya tace minakeso akawo min naci.
Nace, “banajin yunwa mama, ni sonake ma Na kuma ganin Abba”..
“karki damu, Abba yana barci ne, kedai kisamu kici abinci babynmu yak'ara k'ato kafin ki haifo mana”.
Ban fahimci maganar ta Fiddausi ba, Dan naga awajen akwai masu ciki da yawa, aunty Ramlah, aunty Khaleesat, aunty Hauwa'u, Siyama, Zarah, aunty Raihana duk cikinsu ya tsufa, haihuwa yau ko gobe.
Na kalli innarmu dake tsaye batace komaiba, murmushi namata, itama saita mayarmin, nace, “wai har yanzu Munuhiya ba a cire mata ruwanba?”.
Mama Rabi'a tabani amsa da cewar “an cire, barci takeyi”.
Cikin marairaicewar murya nace “ALLAH sarki Sweetheart d'ina, ALLAH yabaki lafiya”.
Duk suka amsa da amin.
Doctor Farida tashigo tana sanar musu ga Galadima nan zai shigo.
'Yar rige-rigen fita iyayena suka farayi, kowa yana jin nauyin suruki ya shigo ya iskeshi, ni dariyama suka bani, nayi murmushi ina komawa Na kwanta.
Saida suka fita kaf sannan nafara jiyo takun takalminsa.
Idanu Na lumshe kamar mai barci.
Tunda ya shigo idonsa Na kaina, yacigaba da takowa gaban gadon, duk tunaninsa barcin gaske nakeyi, maimakon ya zauna saiya dafa gadon ya rankwafo kaina, da sauri da sauri zuciyata tafara bugu saboda kusantoni da ya keyi, fuskarsa daf da tawa tamkar zai had'e bakinmu, mikuma ya tuna saiya janye ya maida saitin goshina ya manna min kisses guda biyu a goshi da saman hanci.
Cikeda mamaki Na waro manyan idanuna, kallon ido cikin ido mukaima juna, ya d'aga min gira d'aya.
Saurin kauda idanuna nayi gefe.
Shikuma yaja kujera ya zauna dab da fuskata yana murmushi.
Munja wasu seconds sannan yasaka hannunsa bisa kumatuna ya juyo da face d'ina inda yake, kin bud'e idona nayi Na kallesa, bai damuba yace “yalla6iya dama haka kike da saurin cafke Abu?”.
Babu shiri Na waro idanuna kansa, nace “yalla6ai mina cafke?”.
Idanunsa ya d'an jujjuya alamar tunani, saikuma ya kalleni, har yanzu hannunsa Na tallafe da fuskata, yace “uhuumm mima kika cafke? Na manta ma”. Ya k'are maganar da d'age kafad'a yana ta6e baki.
d'an hararsa nayi ina tura baki, mutuminnan ya iya rainin wayo.
Yanzunma murmushin yamin, saikuma ya d'ora hannunsa saman shafaffen cikina mai kama da babu ko kayan ciki balle kayi tunanin akwai mutum.
Da sauri Na rik'e hannunsa ina fad'in “ yalla6ai lafiya kuwa?”.
Cikin basarwa yace “itace ta kawo haka, bakimin murna ba”.
Nace, “Murna kuma? tami?”.
Cikin d'age gira d'aya yace “Muhammad Sameer Saifudden yazam pah-pah”.
d'auremin kai maganarsa tayi, Na yunk'ura a hankali zan tashi, mik'ewa yayi ya taimakamin Na zauna yana fad'in “yi da kula karkima jama'ar gari 6arna, dan akwai sarkinsu anan”.
Waige-waige Na farayi, nidai banga kowa ba bayan mu biyun dake zaune, saina d'auka da kansa yake, na d'an ta6e bakina kawai.
Shima saiya ta6e bakin yana komawa ya zauna. kusan mintuna biyu duk mukai shiru.
Zuwa can nace, “nikam dai na dawo normal, kace musu su sallameni kawai”.
Batare daya d'agoba yace “nafi buk'atar hakan, mi kikeso Sameer yamiki k'yauta da shi?”.
“k'yauta kuma? akanmi?”.
“Abie ya fara magana”.
Babu shiri na wuntsilo daga gadon ina fad'in da gaske?”.
Da sauri Galadima ya ruk'oni, jikinsa har rawa yakeyi, jina nai kawai bisa cinyarsa.
“yalla6ai!”. nafad'a cikin zaro idanu, sai kuma na hau waige-waigen kar wanifa ya ganmu.
Daf yamatso da fuskarsa kusada tawa, numfashin junanmu na sauka bisa fuskokinmu, na marairaice fuska tamkar zanyi kuka, yanda yasaka idonsa cikin nawa tsigar jikina dukta mimmik'e, jikina har tsuma yakeyi, amma tsabar muguntarsa yak'i ya janye, yakuma hanani damar da zan janye nawa.
A hankali tamkar mai rad'a, yace “ki kula, domin abin cikin kwan yafi kwan dad'i my friend ”. ‘ ya k'are maganar da d'age min gira sama’.
Lumshe idanuna nayi kozan sami sassaucin daina ganin abinda ke yawo a idanun Galadima.
hakan yabashi damar d'ora bakinsa akan nawa, shima ya lumshe nasa idanun.
Babu shiri na bud'e nawa saboda tsorata, ni Munaya mike damun wannan bawa yau? duk yanda naso kwatar kaina hakan ya gagara, dole na sallama yayi iya yinsa sannan ya sakeni.
Zumbur na mik'e daga jikinsa ina sharar kwallar takaici, shima saiya mik'e yana karkad'amin d'anyatsa, ya matso daf dani a hankali ya furta “k'yautar farko kenan”.
juyawa yay yafita yana murmushi da gyara zaman hular kansa.
Na bishi da kallo ina maimaita zancensa na k'arshe, “k'yautar farko? Kamar ya k'yautar farko? mi yake nufi to?”. ban kai ga samo amsarba doctor Farida ta shigo tana murmushi. “ginbiyarmu yalla6ai yace abaki sallama kuje gida ki huta gaba d'aya”.
Saboda Banason tafiyar, sai nace doctor jikina bai gama sakiba, ki Ce masa sai dare zaku sallameni kawai”.
'Yar dariya tayi, ta nunamin Galadima dake bakin k'ofa tsaye ya hard'e hannaye a k'irji.
Baki na tunzuro gaba saboda borin kunya.
Shikuma ya janye idanunsa yana ta6e baki.
Doctor Farida ta bamu sallama, na d'auki alk'yabbata na saka, tareda d'aukar handbag d'ita, sai wani ciccin Magani nakeyi, shi da nakeyi danshi yawani share tamkar bai gane da shi nakeyi ba.
Jinai ya sak'alo hannunsa cikin nawa, na kalleshi da sauri, saiya kannemin ido d'aya.
Ja nayi na tsaya, shima saiya tsaya, ga mutane duk sun zubo mana idanu, kuma har 'yan gidanmu. tamkar zan fasa ihu nace, “yalla6ai ni dai wlhy ka sakeni, kai bakajin kunyar su innarmu ma?”.
Yace “kai ALLAH dai ya shiryeka Sameer, yalla6iya Sameer najin kunyar su Innarmu fa, sai dai kuma yana gudun amasa gangancin abin cikin kwan ne”.
Kallonsa nayi, “ wai minene wannan abin cikin kwan daka ishi mutane da fad'a”.
Ya d'an d'ora hannunsa saman bakinsa alamar mamaki, “yamzu nan bakisan abin cikin kwan ba friend? Lallai news ya wuce dake, ina tayaki jaje kam”.
Kuma kullemin kai yayi a duhu.
Ita dai doctor Farida dake bayanmu sai kuma birgeta muke da bata dariyar salon namu.
Mutane kam dake kallonmu tunaninsu koda doctor Farida muke magana, Dan bazaka ta6a d'auka Galadima ya iya zaro magana hakaba. nikaina mamakin dama yana magana mai tsayi irin haka nakeyi, narasa miya d'abbak'a wannan farin cikin nasa na yau?, duk da bawai yanata dariya baneba, fuskarsa nanan yanda take babu walwala, sai dai yau akwai sakewa tattare dashi, kuma yakan yawaita murmushi bakamar ko yausheba.
Nidai nace, “dan ALLAH yalla6ai kayi hak'uri, wlhy bazan iya zuwa gabansu baba k'arami ahakaba”.
Baice komaiba ya saki hannuna, amma munci gaba da tafiya kafad'a da kafad'a dashi.
Wata kuyanga cikin kuyangin da uwargidan Sarki ta had'omu tai saurin tasowa ta kar6i bag d'in hannuna, ban musaba na mik'a mata, mutane sai gaishini sukeyi, nidai kunyama ta isheni, Dan wasu sun girmemin.
Mun Isa gaban 'yan gidanmu, kowa ya taso yana k'ara min sannu da jiki, nidai sai ce musu make na samu sauk'i.
d'akin da Abba yake muka shiga, hawaye suka cikamin idanu, Galadima ya ruk'o min hannu, kallonsa nayi saiya girgiza min kai alamar kar nayi.
Bance komaiba na janye idanuna, sannan na k'arasa gaban gadon nafara tofa masa addu'oi, shima Galadima ya matso ya tayani, daganan fitowa mukayi, Galadima yakuma gargad'ar police d'in akan su kula sosai, inhar wata matsala ta biyo baya to suyi kuka da Kansu.
Cikin girmamawa suka amsa masa da insha ALLAH hakan bazata faruba ma.
Ni dai ina wajen 'yan gidanmu, jinake kamar karna tafi wlhy, amma innaro tace kartaji karta gani, nabi mijina naje gida na huta, suma sauran 'yan uwana duk gida zasu tafi hakanan, tunda dai iya k'ok'ari galadima tsaye yake akan komai na abban, dukkan kulawa yasaka ana bashi gwargwadon iko.
Nidai sai tunzura baki nake su Fiddausi namin dariya.
Muna haka Galadima ya k'araso wajen, cikin girmamawa yace yakamata suma 'yan gidanmu suje gida hakanan su huta, insha ALLAH Abba zai samu kulawa tamkar suna nan.
Godiya suka shiga yimasa, innaro nata kwararamasa addu'oin gamawa da rayuwa lafiya, da samun afuwa shima ga mahaifinsa, ta k'are maganar da f'adin “ALLAH ya kawo mana kishiyata ko angona duniya lafiya”.
K'asaitaccen murmushi Galadima yayi, a kan la66ansa ya amsa da ammin Granny ”.
Daga nan wajen Munubiya muka nufa, suma 'yan gidanmu suka shiga dansu k'ara ganin Abba su tafi.
Munubiya na kwance tana barci har yanzu ana k'ara mata ruwa, rungumeta nayi ina hawaye, yayinda Galadima da yaa Marwan suke gaisawa cikin mutunta juna, inajinsu sunama juna Congrat, amma ban fahimci na mineneba.
Nace “yaa marwan wai mike damun sweetheart ne haka ta rame?”.
Dariya yaa marwan yayi, yace “babynku ne”.
“lah yaa marwan kana nufin tanada cikine?”.
Kansa ya jinjina min.
Cikeda murna na kuma rungume munubiya ina fad'in “ashe na kusa zama mummy”.
Galadima ya kauda kai gefe yana murmushi kawai, shina yaa marwan sai k'aramar dariya yakeyi.
Da k'yar dai na hak'ura na baro asibitin nan badan nasoba, suma 'yan gidanmu duk sun wuce gida.
*****************
A mota sai zun6ire-zun6iren baki nakeyi, saboda haushin banso rabuwa da 'yan uwana ba yanzu, Galadima ya wani shareni.
shikam dukya gajine, bai cika wahalar zirga-zirga irin hakaba, gashi dama bawani isashshen barci yasamuba jiya.
Batare dana kalleshi ba nace “wai ina yaa Sauban ne?”.
Bai d'ago daga latsa wayar dayakeyiba ya bani amsa da “suna tare da Nuren”.
Da sauri na kalleshi danjin ya ambaci sunan Wanda nake son Sanin wanene shi?, cikin kwantar da murya nace “yalla6ai wai wanene Nuren? ”.
Tambayar tabashi mamaki, amma saiya share ya d'ago muka had'a ido, kowa ya janye cikin basarwa. bai bani amsarba har muka shiga cikin masarautar...................✍🏼
Kuyi manage da wannan sister's🤗.
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
[7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_*
*_Haske writer's asso...._*💡
*_♦RAINA KAMA......♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻
~Book 2~ 👉🏻8⃣
“shima insha ALLAH zai tashi 'Yar albarka”. Cewar innaro tana dariya.
Ni duk sun kuma d'auremin kai da addu'ar da sukeyi suna fad'in ALLAH ya inganta.
Mamansu Fauziyya tace minakeso akawo min naci.
Nace, “banajin yunwa mama, ni sonake ma Na kuma ganin Abba”..
“karki damu, Abba yana barci ne, kedai kisamu kici abinci babynmu yak'ara k'ato kafin ki haifo mana”.
Ban fahimci maganar ta Fiddausi ba, Dan naga awajen akwai masu ciki da yawa, aunty Ramlah, aunty Khaleesat, aunty Hauwa'u, Siyama, Zarah, aunty Raihana duk cikinsu ya tsufa, haihuwa yau ko gobe.
Na kalli innarmu dake tsaye batace komaiba, murmushi namata, itama saita mayarmin, nace, “wai har yanzu Munuhiya ba a cire mata ruwanba?”.
Mama Rabi'a tabani amsa da cewar “an cire, barci takeyi”.
Cikin marairaicewar murya nace “ALLAH sarki Sweetheart d'ina, ALLAH yabaki lafiya”.
Duk suka amsa da amin.
Doctor Farida tashigo tana sanar musu ga Galadima nan zai shigo.
'Yar rige-rigen fita iyayena suka farayi, kowa yana jin nauyin suruki ya shigo ya iskeshi, ni dariyama suka bani, nayi murmushi ina komawa Na kwanta.
Saida suka fita kaf sannan nafara jiyo takun takalminsa.
Idanu Na lumshe kamar mai barci.
Tunda ya shigo idonsa Na kaina, yacigaba da takowa gaban gadon, duk tunaninsa barcin gaske nakeyi, maimakon ya zauna saiya dafa gadon ya rankwafo kaina, da sauri da sauri zuciyata tafara bugu saboda kusantoni da ya keyi, fuskarsa daf da tawa tamkar zai had'e bakinmu, mikuma ya tuna saiya janye ya maida saitin goshina ya manna min kisses guda biyu a goshi da saman hanci.
Cikeda mamaki Na waro manyan idanuna, kallon ido cikin ido mukaima juna, ya d'aga min gira d'aya.
Saurin kauda idanuna nayi gefe.
Shikuma yaja kujera ya zauna dab da fuskata yana murmushi.
Munja wasu seconds sannan yasaka hannunsa bisa kumatuna ya juyo da face d'ina inda yake, kin bud'e idona nayi Na kallesa, bai damuba yace “yalla6iya dama haka kike da saurin cafke Abu?”.
Babu shiri Na waro idanuna kansa, nace “yalla6ai mina cafke?”.
Idanunsa ya d'an jujjuya alamar tunani, saikuma ya kalleni, har yanzu hannunsa Na tallafe da fuskata, yace “uhuumm mima kika cafke? Na manta ma”. Ya k'are maganar da d'age kafad'a yana ta6e baki.
d'an hararsa nayi ina tura baki, mutuminnan ya iya rainin wayo.
Yanzunma murmushin yamin, saikuma ya d'ora hannunsa saman shafaffen cikina mai kama da babu ko kayan ciki balle kayi tunanin akwai mutum.
Da sauri Na rik'e hannunsa ina fad'in “ yalla6ai lafiya kuwa?”.
Cikin basarwa yace “itace ta kawo haka, bakimin murna ba”.
Nace, “Murna kuma? tami?”.
Cikin d'age gira d'aya yace “Muhammad Sameer Saifudden yazam pah-pah”.
d'auremin kai maganarsa tayi, Na yunk'ura a hankali zan tashi, mik'ewa yayi ya taimakamin Na zauna yana fad'in “yi da kula karkima jama'ar gari 6arna, dan akwai sarkinsu anan”.
Waige-waige Na farayi, nidai banga kowa ba bayan mu biyun dake zaune, saina d'auka da kansa yake, na d'an ta6e bakina kawai.
Shima saiya ta6e bakin yana komawa ya zauna. kusan mintuna biyu duk mukai shiru.
Zuwa can nace, “nikam dai na dawo normal, kace musu su sallameni kawai”.
Batare daya d'agoba yace “nafi buk'atar hakan, mi kikeso Sameer yamiki k'yauta da shi?”.
“k'yauta kuma? akanmi?”.
“Abie ya fara magana”.
Babu shiri na wuntsilo daga gadon ina fad'in da gaske?”.
Da sauri Galadima ya ruk'oni, jikinsa har rawa yakeyi, jina nai kawai bisa cinyarsa.
“yalla6ai!”. nafad'a cikin zaro idanu, sai kuma na hau waige-waigen kar wanifa ya ganmu.
Daf yamatso da fuskarsa kusada tawa, numfashin junanmu na sauka bisa fuskokinmu, na marairaice fuska tamkar zanyi kuka, yanda yasaka idonsa cikin nawa tsigar jikina dukta mimmik'e, jikina har tsuma yakeyi, amma tsabar muguntarsa yak'i ya janye, yakuma hanani damar da zan janye nawa.
A hankali tamkar mai rad'a, yace “ki kula, domin abin cikin kwan yafi kwan dad'i my friend ”. ‘ ya k'are maganar da d'age min gira sama’.
Lumshe idanuna nayi kozan sami sassaucin daina ganin abinda ke yawo a idanun Galadima.
hakan yabashi damar d'ora bakinsa akan nawa, shima ya lumshe nasa idanun.
Babu shiri na bud'e nawa saboda tsorata, ni Munaya mike damun wannan bawa yau? duk yanda naso kwatar kaina hakan ya gagara, dole na sallama yayi iya yinsa sannan ya sakeni.
Zumbur na mik'e daga jikinsa ina sharar kwallar takaici, shima saiya mik'e yana karkad'amin d'anyatsa, ya matso daf dani a hankali ya furta “k'yautar farko kenan”.
juyawa yay yafita yana murmushi da gyara zaman hular kansa.
Na bishi da kallo ina maimaita zancensa na k'arshe, “k'yautar farko? Kamar ya k'yautar farko? mi yake nufi to?”. ban kai ga samo amsarba doctor Farida ta shigo tana murmushi. “ginbiyarmu yalla6ai yace abaki sallama kuje gida ki huta gaba d'aya”.
Saboda Banason tafiyar, sai nace doctor jikina bai gama sakiba, ki Ce masa sai dare zaku sallameni kawai”.
'Yar dariya tayi, ta nunamin Galadima dake bakin k'ofa tsaye ya hard'e hannaye a k'irji.
Baki na tunzuro gaba saboda borin kunya.
Shikuma ya janye idanunsa yana ta6e baki.
Doctor Farida ta bamu sallama, na d'auki alk'yabbata na saka, tareda d'aukar handbag d'ita, sai wani ciccin Magani nakeyi, shi da nakeyi danshi yawani share tamkar bai gane da shi nakeyi ba.
Jinai ya sak'alo hannunsa cikin nawa, na kalleshi da sauri, saiya kannemin ido d'aya.
Ja nayi na tsaya, shima saiya tsaya, ga mutane duk sun zubo mana idanu, kuma har 'yan gidanmu. tamkar zan fasa ihu nace, “yalla6ai ni dai wlhy ka sakeni, kai bakajin kunyar su innarmu ma?”.
Yace “kai ALLAH dai ya shiryeka Sameer, yalla6iya Sameer najin kunyar su Innarmu fa, sai dai kuma yana gudun amasa gangancin abin cikin kwan ne”.
Kallonsa nayi, “ wai minene wannan abin cikin kwan daka ishi mutane da fad'a”.
Ya d'an d'ora hannunsa saman bakinsa alamar mamaki, “yamzu nan bakisan abin cikin kwan ba friend? Lallai news ya wuce dake, ina tayaki jaje kam”.
Kuma kullemin kai yayi a duhu.
Ita dai doctor Farida dake bayanmu sai kuma birgeta muke da bata dariyar salon namu.
Mutane kam dake kallonmu tunaninsu koda doctor Farida muke magana, Dan bazaka ta6a d'auka Galadima ya iya zaro magana hakaba. nikaina mamakin dama yana magana mai tsayi irin haka nakeyi, narasa miya d'abbak'a wannan farin cikin nasa na yau?, duk da bawai yanata dariya baneba, fuskarsa nanan yanda take babu walwala, sai dai yau akwai sakewa tattare dashi, kuma yakan yawaita murmushi bakamar ko yausheba.
Nidai nace, “dan ALLAH yalla6ai kayi hak'uri, wlhy bazan iya zuwa gabansu baba k'arami ahakaba”.
Baice komaiba ya saki hannuna, amma munci gaba da tafiya kafad'a da kafad'a dashi.
Wata kuyanga cikin kuyangin da uwargidan Sarki ta had'omu tai saurin tasowa ta kar6i bag d'in hannuna, ban musaba na mik'a mata, mutane sai gaishini sukeyi, nidai kunyama ta isheni, Dan wasu sun girmemin.
Mun Isa gaban 'yan gidanmu, kowa ya taso yana k'ara min sannu da jiki, nidai sai ce musu make na samu sauk'i.
d'akin da Abba yake muka shiga, hawaye suka cikamin idanu, Galadima ya ruk'o min hannu, kallonsa nayi saiya girgiza min kai alamar kar nayi.
Bance komaiba na janye idanuna, sannan na k'arasa gaban gadon nafara tofa masa addu'oi, shima Galadima ya matso ya tayani, daganan fitowa mukayi, Galadima yakuma gargad'ar police d'in akan su kula sosai, inhar wata matsala ta biyo baya to suyi kuka da Kansu.
Cikin girmamawa suka amsa masa da insha ALLAH hakan bazata faruba ma.
Ni dai ina wajen 'yan gidanmu, jinake kamar karna tafi wlhy, amma innaro tace kartaji karta gani, nabi mijina naje gida na huta, suma sauran 'yan uwana duk gida zasu tafi hakanan, tunda dai iya k'ok'ari galadima tsaye yake akan komai na abban, dukkan kulawa yasaka ana bashi gwargwadon iko.
Nidai sai tunzura baki nake su Fiddausi namin dariya.
Muna haka Galadima ya k'araso wajen, cikin girmamawa yace yakamata suma 'yan gidanmu suje gida hakanan su huta, insha ALLAH Abba zai samu kulawa tamkar suna nan.
Godiya suka shiga yimasa, innaro nata kwararamasa addu'oin gamawa da rayuwa lafiya, da samun afuwa shima ga mahaifinsa, ta k'are maganar da f'adin “ALLAH ya kawo mana kishiyata ko angona duniya lafiya”.
K'asaitaccen murmushi Galadima yayi, a kan la66ansa ya amsa da ammin Granny ”.
Daga nan wajen Munubiya muka nufa, suma 'yan gidanmu suka shiga dansu k'ara ganin Abba su tafi.
Munubiya na kwance tana barci har yanzu ana k'ara mata ruwa, rungumeta nayi ina hawaye, yayinda Galadima da yaa Marwan suke gaisawa cikin mutunta juna, inajinsu sunama juna Congrat, amma ban fahimci na mineneba.
Nace “yaa marwan wai mike damun sweetheart ne haka ta rame?”.
Dariya yaa marwan yayi, yace “babynku ne”.
“lah yaa marwan kana nufin tanada cikine?”.
Kansa ya jinjina min.
Cikeda murna na kuma rungume munubiya ina fad'in “ashe na kusa zama mummy”.
Galadima ya kauda kai gefe yana murmushi kawai, shina yaa marwan sai k'aramar dariya yakeyi.
Da k'yar dai na hak'ura na baro asibitin nan badan nasoba, suma 'yan gidanmu duk sun wuce gida.
*****************
A mota sai zun6ire-zun6iren baki nakeyi, saboda haushin banso rabuwa da 'yan uwana ba yanzu, Galadima ya wani shareni.
shikam dukya gajine, bai cika wahalar zirga-zirga irin hakaba, gashi dama bawani isashshen barci yasamuba jiya.
Batare dana kalleshi ba nace “wai ina yaa Sauban ne?”.
Bai d'ago daga latsa wayar dayakeyiba ya bani amsa da “suna tare da Nuren”.
Da sauri na kalleshi danjin ya ambaci sunan Wanda nake son Sanin wanene shi?, cikin kwantar da murya nace “yalla6ai wai wanene Nuren? ”.
Tambayar tabashi mamaki, amma saiya share ya d'ago muka had'a ido, kowa ya janye cikin basarwa. bai bani amsarba har muka shiga cikin masarautar...................✍🏼
Kuyi manage da wannan sister's🤗.
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
[7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_*
*_Haske writer's asso...._*💡
*_♦RAINA KAMA......♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻
~Book 2~ 👉🏻8⃣