Sashe 6
My Enemy Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shima kansa ta bashi tausayi shafar sumar kanta kawai yayi,
Abbah kallon Baiwar ALLAH yayi yace "Dota ya kike tsaye ne, ki ƙaraso mana..."
haka take jan ƙafa ta ƙaraso cikin falon ta zauna itama a cikin ɗaya daga jerukan kujerun,
Aunty Yolash murmushi tasau tana kallon Baiwar ALLAH tace "Ammatan Roshan an kusan zama Amarya, duk wannan kayayyakin kine, saboda haka ki kwantar da hankalinki Roshan shine mijin da yafi dacewa da rayuwarki, mutum ne mai kyakkyawar zuciya, kuma yana matuƙar ƙaunarki tinda kullum sai ya ƙirani ya bani labarinki, kinsan Roshan in har yana son abu toh haukacewa yake, don haka ki riƙe mana ɗan Amanar mu hannu bibbiyu, idan muka ganshi cikin ƙunci to kece sila, haka kuma idan muka ganshi cikin walwala da farin ciki nan ma kece sila, Ƴar Amana da Ɗan Amana ku kula mana da kan ku dan ALLAH, yanzu dai sauran mana kwana uku ɗaurin Aure, Insha ALLAHU daga gobe zamu fara ganin manya-manyan baƙi daga ƙasashen waje da garurruwa, sannan ƴan uwan mahaifiyarsu daga Saudiyya suma suna nan tafe...."
Baiwar ALLAH hawaye ne kawai yake faman gangaro mata, abu biyu ne suka tada mata da hankali na farko bata son Auren nan sannan kuma taji an ambaci sunan Ƴar Amana, sai kawai taji zuciyarta na bugun uku-uku, maganar zuci ta shiga yi tana faɗin "yanzu a wani hali kike ciki Ƴar uwata, shin kin mutu ne ko kina raye? a cikin haske kike ko a cikin duhu? wayyo Allah Ƴar Amana ina kewarki...."
bata san lokacin da kuka ya kuɓuto mata ba, kuka take na gaske kanta na kallon ƙasi...
Aunty Yolash tana cikin jawabi taji ƙarar kukan Baiwar ALLAH nan ta dakata da maganar tana kallonta,
Shima Abbah hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ba, murya a harharɗe yake faɗin "lafiya kuwa Dota? meya sameki kike kukan? shin bakya son Auren ne? ki gaya mun dan ALLAH yanzu a dakatar..."
kowa ya kasa kunne yana son jin abinda Baiwar ALLAH zata ce,
Aunty Yolash ce itama ta tashi ta nufi wurin da take zaune ta zauna tare da rungimarta tace "Dota kiyi haƙuri ki sanar mana abinda yake ranki, Bama son muyi miki dole domin ke ɗin Amana ce a gare mu, shin bakya son Auren ne?..."
Razhdeen idonsa a kanta ya rasa gane meye dalilin kukanta,
Ummy tana zaune kai a ƙasi ƙirjinta na bugun uku-uku tana addu'ar kar Baiwar ALLAH tace bata son Auren, domin Roshan zai iya shiga mungun mawuyancin hali, tsoronta kar ciwon zuciyarsa ta tashi..."
Rukky tana kwance kan cinyar Pinky domin ba lafiya ne gareta ba tana fama da zazzaɓi, murya na kakkarwa alamar jin sanyi tace "Aunty daman fah idan Amarya anayi mata nasiha kuka take, kowace Amarya ma hakane..."
Aunty Yolash tace "a'ah muna son jin daga bakinta ne domin bamu san abinda ke ranta ba, kar mu toye mata hakki..."
Pinky ɗan tsuka taja tare da kawar da fuska gefe daman ita sam bata ƙaunar Auren nan domin a duniyar nan babu mace data fi tsana kamar Baiwar ALLAH, a cewar ta ita tayi sanadiyar rabasu da mahaifiyarsu..."
Aunty Yolash ce ta ƙara tambayarta cewar "Dota bakya son Auren ne?..."
Girgiza kai Baiwar ALLAH tayi alamar a'ah...
Aunty Yolash tace "to meyasa kike kuka?..."
Baiwar ALLAH tace "babu komai kawai lokaci guda naji kukan ban san meyasa ba...."
Aunty Yolash tace "Ayyah sorry Dota saboda zaki kasance cikin Amarci ne shiyasa, kuma son samu ace iyayenki suma suga ranar Auren ki...."
kafin Aunty Yolash ta ƙarasa maganar taji Baiwar ALLAH ta ƙara fashewa da wani sabon kukan,
rungumarta tayi tana rarrashinta daƙyar ta iya dakatar da kukan..."
Saida Abbah yayi mata nasiha sosai mai ratsa jiki, ya rarrasheta kafin nan zuciyarta tayi sanyi,
Saida suka kammala tattaunawarsu tsab akan batun Auren kafin nan Abbah ya dawo kan Razhdeen,
ya kalle shi sannan yace Razhdeen!.."
Uncle Deen kallon Abbah yayi jin ya ambaci sunansa, shi gaba ɗaya hankalinsa akan Ƴar Amana yake, tunaninta kawai yake sai fuskarta yana masa gizo...
Abbah ya cigaba da cewa "Yakamata duk wannan shirmen da kake ka dena shi Razhdeen, faɗan da nake maka bawai bana sonka bane, bazan taɓa iya cire hannuna daga kanka ba Razhdeen, miskilancinka yayi yawa ka rage koda bazaka iya cire wa gaba ɗaya ba, girman kanka yayi yawa komai naka yayi yawa haba Razhdeen,
wani irin zuciya ne Allah yayi maka, acikin sojojin duniya gaba ɗaya da wuya a samu mai kalar ɗabi'unka na rashin jin magana, amma duk da haka ina mai ƙara godewa Allah yasa kai ba manemin mata bane sannan kai bame shaye-shaye bane, kai ba ɓarawo bane, duk waɗannan Bad behavior zan shaidi ƴaƴana babu maiyinsu, sai rashin jin magana,
Please Major General Razhdeen be careful about all the things that is make me unhappiness..."
Razhdeen idonsa akan carpet ko É—ago da kai baiyi ba, motsi ya fara yi da lips É—insa a hankali yake furta "sorry Dad I'll try to make you happy but my behavior's can never change..."
Aunty Yolash kawar da kai gefe tayi tana dariya ciki-ciki domin Razhdeen ba ƙaramin dariya ya bata ba,
daɗinta dashi baya ɓoye maitarsa, koda mutum bazaiji daɗi ba to dole saiya gaya masa abinda ke ransa, baya tsoro kuma baya fargaban abinda zaije ya dawo..."
Abbah cikin kalar tausayi yace "why Razhdeen?..."
Yace "because I don't have a Bad character's, kawai raini ne bana so sannan banason wulaƙanci da rashin tarbiyya,
har yanzu baku fahimci yanda tsarin rayuwata take ba, inada zuciyar da bazan iya ɗaukar duk wani shirme ba, lokaci guda zan ɗauki hukunci akan mutum shiyasa kuke ganin rashin haƙuri na..."
Abbah yace "TOH shi Roshan daka ɗauki hukunci akansa fa? shi da ya gama fahimtar halinka kuma yake kiyaye ɓacin ranka..."
Razhdeen kallon Abbah yayi sannan yace "why tin lokacin baku tambayeni laifin da yayi mun ba sai yanzu? Dad you known banason yawan magana sosai, my headache..."
Abbah yace "it's okay nasan Kanada matsalar nan,
abinda ya wuce ya rigada ya wuce sai dai bama fatan hakan ya sake faruwa, kayi haƙuri da wannan ciwon kan nakan magana nakeso nayi dakai, dole yau zaka ɗan motsa yin magana kafin kaje kaɗan huta Koh..."
haɗe gira yayi tare da faɗin "okay let me go and sleep before..." ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin miƙewa.
Abbah yayi saurin dakatar dashi yana faÉ—in "Noooo ka saurara kaji kalar tattaunawar da zamuyi mana..."
zama yayi ya kasa kunne yana sauraron Abbah,
Baiwar ALLAH haka kawai sai satar kallon Razhdeen take tayi...
Abbah ya cigaba da cewa "naji mai martaba ya fara mun wata magana ne dangane da ƙanwar matarsa Maamie, akan cewa za'a haɗa Auren ka dana Roshan itace wacce zaka Aura..."
Dasauri Razhdeen ya ɗago yana kallon Abbah fuska a murtuƙe babu alamun Annuri a fuskar,
Aunty Yolash itama da sauri ta furta "whattttt!..."
Yaran gidan kuwa gaba É—aya haÉ—a baki sukayi wurin cewa "Ramlatttt!..."
Baiwar ALLAH kuwa kanta ne yayi wani irin sarawa da ƙarfin gaske kamar wanda aka doka mata Gatari, dasauri ta sunkuyar da kanta ƙasi tana dafe dashi....
Aunty Yolash tace "wai Yaya kana nufin kace Ramlah ƙanwar MAAMIE? Impossible wallahi, kaima kasan cewa Hajia Maamie ta shure Hajia Kilishi matarka wulaƙanci da rashin mutunci Koh? shin baka san cewa Hajia Maamie ita take iko da mai martaba ba koh? toh idan baka saniba yau zan sanar maka, duk abinda hajia Maamie tace ayi a masarautar nan shi akeyi idan tace bata son abu TOH kuwa mai martaba bai iya yayi ba, itace hakima mai mulkar masarautar...."
Abbah yace "ehh king ya sanar mun amma nace ya bari sai sunzo zamu tattauna akan batun tinda duk zasu zo Auren nan, amma ita yarinyar batada matsala ai koh?..."
Aunty Yolash tace "hakane amma kuma tana ɗaukar zugar Yayarta Hajia Maamie, nipah gaskiya Yaya bazaiyu a rinƙa tara mana mata marasa tarbiyya a gida ba, Hajia Kilishi ma ya muka ƙare da ita kuma du a ƙara kawo mana wata, itama Hajia Maamie za'a ɗau hukunci akanta ai....."
wani irin harara Pinky ta wurga wa Aunty Yolash dai-dain lokacin da suka haÉ—a ido da Aunty Yolash,
Aunty Yolash ce ta ɗauki pillow ta wurga mata tare da faɗin "kin ci ubanki Balkisu! Ni sa'arki ce ko kuma ina wasa dake? aikin banza kawai shin ƙarya nayi ne Uwarki tayi abun arziƙine a gidan nan ? tin kafin a haife ku ake shan gwagwarmaya da ita, gaskiya kuma dole a faɗe ta..."
murguÉ—a baki pinky tayi tana gunaguni tace "Uwata bata gidan ma amma baza'a barta tasha iska ba..."
Aunty Yolash tace "ita data sha iska kuwa har abada domin ko mutuwa tayi dole a faɗi halayarta na Arziƙi ko akasin haka,
ke nifa ba abokiyar yinki bane, Uwarki ce sa'ar yina domin ko Auntynki Minal bata isheni kallo ba tinda a gabana duk aka haife ku..."
ƙara wurga mata harara Pinky tayi tare da murguɗa baki tace "to kiyi dani ɗin mana..."
dasauri Rukky ta tashi daga cinyarta tana Binta da kallo cike da mamakin yanda Pinky ta tsaya tana yiwa Aunty Yolash ƙanwar Abbansu rashin kunya,
Pinky bata ankara ba taji Abbah ya zabga mata mari tare da jefota ƙasin carpet yana cankinta,
Abbah cikin zafin rai yake tattaka ta yana faÉ—in "Æ´ar uwar tawan kike wa rashin kunya dan ubanki, itama mahaifiya ce a wurinku, ashe rashin tarbiyar takun har takai haka?..."
Abbah har numfashinsa ne yake shirin ɗagewa tsabar ɓacin rai dake yanada hawan jini, Aunty Yolash ce ta tashi tana rirriƙe shi tare da bashi haƙuri tana rarrashinsa,
Pinky tana kwance ba abinda take sai kuka, ji nayi an ɗagota da hannu ɗaya ana janta suka nufi hanyar bakin ƙofa za'a fita da ita, idanuwanta ta buɗe tana ƙoƙarin ganin wanda yake shirin fita da ita, naga Razhdeen ne fuska ba annuri, daga nan ta saddaƙar cewa yau ranar mutuwarta ne, Ihu ta fara kurmawa tana ƙiran sunan Mommy, "wayyo Allah nah Mommy kizo ki temake Ni zasu kashe Ni, Mommy nah wayyo, Dan ALLAH Uncle Deen kayi haƙuri ka ƙyaleni, wallahi bazan ƙara baaa...."
Abbah kuwa cewa yake "kaje ka hukuntata tinda itama halin uwarta gareta, ba'a gidan nan za'a mun wannan iskanci ba..."
*ƳAR AMANA*🕊ï¸ðŸ•Šï¸ðŸ•Šï¸
Abbah kallon Baiwar ALLAH yayi yace "Dota ya kike tsaye ne, ki ƙaraso mana..."
haka take jan ƙafa ta ƙaraso cikin falon ta zauna itama a cikin ɗaya daga jerukan kujerun,
Aunty Yolash murmushi tasau tana kallon Baiwar ALLAH tace "Ammatan Roshan an kusan zama Amarya, duk wannan kayayyakin kine, saboda haka ki kwantar da hankalinki Roshan shine mijin da yafi dacewa da rayuwarki, mutum ne mai kyakkyawar zuciya, kuma yana matuƙar ƙaunarki tinda kullum sai ya ƙirani ya bani labarinki, kinsan Roshan in har yana son abu toh haukacewa yake, don haka ki riƙe mana ɗan Amanar mu hannu bibbiyu, idan muka ganshi cikin ƙunci to kece sila, haka kuma idan muka ganshi cikin walwala da farin ciki nan ma kece sila, Ƴar Amana da Ɗan Amana ku kula mana da kan ku dan ALLAH, yanzu dai sauran mana kwana uku ɗaurin Aure, Insha ALLAHU daga gobe zamu fara ganin manya-manyan baƙi daga ƙasashen waje da garurruwa, sannan ƴan uwan mahaifiyarsu daga Saudiyya suma suna nan tafe...."
Baiwar ALLAH hawaye ne kawai yake faman gangaro mata, abu biyu ne suka tada mata da hankali na farko bata son Auren nan sannan kuma taji an ambaci sunan Ƴar Amana, sai kawai taji zuciyarta na bugun uku-uku, maganar zuci ta shiga yi tana faɗin "yanzu a wani hali kike ciki Ƴar uwata, shin kin mutu ne ko kina raye? a cikin haske kike ko a cikin duhu? wayyo Allah Ƴar Amana ina kewarki...."
bata san lokacin da kuka ya kuɓuto mata ba, kuka take na gaske kanta na kallon ƙasi...
Aunty Yolash tana cikin jawabi taji ƙarar kukan Baiwar ALLAH nan ta dakata da maganar tana kallonta,
Shima Abbah hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ba, murya a harharɗe yake faɗin "lafiya kuwa Dota? meya sameki kike kukan? shin bakya son Auren ne? ki gaya mun dan ALLAH yanzu a dakatar..."
kowa ya kasa kunne yana son jin abinda Baiwar ALLAH zata ce,
Aunty Yolash ce itama ta tashi ta nufi wurin da take zaune ta zauna tare da rungimarta tace "Dota kiyi haƙuri ki sanar mana abinda yake ranki, Bama son muyi miki dole domin ke ɗin Amana ce a gare mu, shin bakya son Auren ne?..."
Razhdeen idonsa a kanta ya rasa gane meye dalilin kukanta,
Ummy tana zaune kai a ƙasi ƙirjinta na bugun uku-uku tana addu'ar kar Baiwar ALLAH tace bata son Auren, domin Roshan zai iya shiga mungun mawuyancin hali, tsoronta kar ciwon zuciyarsa ta tashi..."
Rukky tana kwance kan cinyar Pinky domin ba lafiya ne gareta ba tana fama da zazzaɓi, murya na kakkarwa alamar jin sanyi tace "Aunty daman fah idan Amarya anayi mata nasiha kuka take, kowace Amarya ma hakane..."
Aunty Yolash tace "a'ah muna son jin daga bakinta ne domin bamu san abinda ke ranta ba, kar mu toye mata hakki..."
Pinky ɗan tsuka taja tare da kawar da fuska gefe daman ita sam bata ƙaunar Auren nan domin a duniyar nan babu mace data fi tsana kamar Baiwar ALLAH, a cewar ta ita tayi sanadiyar rabasu da mahaifiyarsu..."
Aunty Yolash ce ta ƙara tambayarta cewar "Dota bakya son Auren ne?..."
Girgiza kai Baiwar ALLAH tayi alamar a'ah...
Aunty Yolash tace "to meyasa kike kuka?..."
Baiwar ALLAH tace "babu komai kawai lokaci guda naji kukan ban san meyasa ba...."
Aunty Yolash tace "Ayyah sorry Dota saboda zaki kasance cikin Amarci ne shiyasa, kuma son samu ace iyayenki suma suga ranar Auren ki...."
kafin Aunty Yolash ta ƙarasa maganar taji Baiwar ALLAH ta ƙara fashewa da wani sabon kukan,
rungumarta tayi tana rarrashinta daƙyar ta iya dakatar da kukan..."
Saida Abbah yayi mata nasiha sosai mai ratsa jiki, ya rarrasheta kafin nan zuciyarta tayi sanyi,
Saida suka kammala tattaunawarsu tsab akan batun Auren kafin nan Abbah ya dawo kan Razhdeen,
ya kalle shi sannan yace Razhdeen!.."
Uncle Deen kallon Abbah yayi jin ya ambaci sunansa, shi gaba ɗaya hankalinsa akan Ƴar Amana yake, tunaninta kawai yake sai fuskarta yana masa gizo...
Abbah ya cigaba da cewa "Yakamata duk wannan shirmen da kake ka dena shi Razhdeen, faɗan da nake maka bawai bana sonka bane, bazan taɓa iya cire hannuna daga kanka ba Razhdeen, miskilancinka yayi yawa ka rage koda bazaka iya cire wa gaba ɗaya ba, girman kanka yayi yawa komai naka yayi yawa haba Razhdeen,
wani irin zuciya ne Allah yayi maka, acikin sojojin duniya gaba ɗaya da wuya a samu mai kalar ɗabi'unka na rashin jin magana, amma duk da haka ina mai ƙara godewa Allah yasa kai ba manemin mata bane sannan kai bame shaye-shaye bane, kai ba ɓarawo bane, duk waɗannan Bad behavior zan shaidi ƴaƴana babu maiyinsu, sai rashin jin magana,
Please Major General Razhdeen be careful about all the things that is make me unhappiness..."
Razhdeen idonsa akan carpet ko É—ago da kai baiyi ba, motsi ya fara yi da lips É—insa a hankali yake furta "sorry Dad I'll try to make you happy but my behavior's can never change..."
Aunty Yolash kawar da kai gefe tayi tana dariya ciki-ciki domin Razhdeen ba ƙaramin dariya ya bata ba,
daɗinta dashi baya ɓoye maitarsa, koda mutum bazaiji daɗi ba to dole saiya gaya masa abinda ke ransa, baya tsoro kuma baya fargaban abinda zaije ya dawo..."
Abbah cikin kalar tausayi yace "why Razhdeen?..."
Yace "because I don't have a Bad character's, kawai raini ne bana so sannan banason wulaƙanci da rashin tarbiyya,
har yanzu baku fahimci yanda tsarin rayuwata take ba, inada zuciyar da bazan iya ɗaukar duk wani shirme ba, lokaci guda zan ɗauki hukunci akan mutum shiyasa kuke ganin rashin haƙuri na..."
Abbah yace "TOH shi Roshan daka ɗauki hukunci akansa fa? shi da ya gama fahimtar halinka kuma yake kiyaye ɓacin ranka..."
Razhdeen kallon Abbah yayi sannan yace "why tin lokacin baku tambayeni laifin da yayi mun ba sai yanzu? Dad you known banason yawan magana sosai, my headache..."
Abbah yace "it's okay nasan Kanada matsalar nan,
abinda ya wuce ya rigada ya wuce sai dai bama fatan hakan ya sake faruwa, kayi haƙuri da wannan ciwon kan nakan magana nakeso nayi dakai, dole yau zaka ɗan motsa yin magana kafin kaje kaɗan huta Koh..."
haɗe gira yayi tare da faɗin "okay let me go and sleep before..." ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin miƙewa.
Abbah yayi saurin dakatar dashi yana faÉ—in "Noooo ka saurara kaji kalar tattaunawar da zamuyi mana..."
zama yayi ya kasa kunne yana sauraron Abbah,
Baiwar ALLAH haka kawai sai satar kallon Razhdeen take tayi...
Abbah ya cigaba da cewa "naji mai martaba ya fara mun wata magana ne dangane da ƙanwar matarsa Maamie, akan cewa za'a haɗa Auren ka dana Roshan itace wacce zaka Aura..."
Dasauri Razhdeen ya ɗago yana kallon Abbah fuska a murtuƙe babu alamun Annuri a fuskar,
Aunty Yolash itama da sauri ta furta "whattttt!..."
Yaran gidan kuwa gaba É—aya haÉ—a baki sukayi wurin cewa "Ramlatttt!..."
Baiwar ALLAH kuwa kanta ne yayi wani irin sarawa da ƙarfin gaske kamar wanda aka doka mata Gatari, dasauri ta sunkuyar da kanta ƙasi tana dafe dashi....
Aunty Yolash tace "wai Yaya kana nufin kace Ramlah ƙanwar MAAMIE? Impossible wallahi, kaima kasan cewa Hajia Maamie ta shure Hajia Kilishi matarka wulaƙanci da rashin mutunci Koh? shin baka san cewa Hajia Maamie ita take iko da mai martaba ba koh? toh idan baka saniba yau zan sanar maka, duk abinda hajia Maamie tace ayi a masarautar nan shi akeyi idan tace bata son abu TOH kuwa mai martaba bai iya yayi ba, itace hakima mai mulkar masarautar...."
Abbah yace "ehh king ya sanar mun amma nace ya bari sai sunzo zamu tattauna akan batun tinda duk zasu zo Auren nan, amma ita yarinyar batada matsala ai koh?..."
Aunty Yolash tace "hakane amma kuma tana ɗaukar zugar Yayarta Hajia Maamie, nipah gaskiya Yaya bazaiyu a rinƙa tara mana mata marasa tarbiyya a gida ba, Hajia Kilishi ma ya muka ƙare da ita kuma du a ƙara kawo mana wata, itama Hajia Maamie za'a ɗau hukunci akanta ai....."
wani irin harara Pinky ta wurga wa Aunty Yolash dai-dain lokacin da suka haÉ—a ido da Aunty Yolash,
Aunty Yolash ce ta ɗauki pillow ta wurga mata tare da faɗin "kin ci ubanki Balkisu! Ni sa'arki ce ko kuma ina wasa dake? aikin banza kawai shin ƙarya nayi ne Uwarki tayi abun arziƙine a gidan nan ? tin kafin a haife ku ake shan gwagwarmaya da ita, gaskiya kuma dole a faɗe ta..."
murguÉ—a baki pinky tayi tana gunaguni tace "Uwata bata gidan ma amma baza'a barta tasha iska ba..."
Aunty Yolash tace "ita data sha iska kuwa har abada domin ko mutuwa tayi dole a faɗi halayarta na Arziƙi ko akasin haka,
ke nifa ba abokiyar yinki bane, Uwarki ce sa'ar yina domin ko Auntynki Minal bata isheni kallo ba tinda a gabana duk aka haife ku..."
ƙara wurga mata harara Pinky tayi tare da murguɗa baki tace "to kiyi dani ɗin mana..."
dasauri Rukky ta tashi daga cinyarta tana Binta da kallo cike da mamakin yanda Pinky ta tsaya tana yiwa Aunty Yolash ƙanwar Abbansu rashin kunya,
Pinky bata ankara ba taji Abbah ya zabga mata mari tare da jefota ƙasin carpet yana cankinta,
Abbah cikin zafin rai yake tattaka ta yana faÉ—in "Æ´ar uwar tawan kike wa rashin kunya dan ubanki, itama mahaifiya ce a wurinku, ashe rashin tarbiyar takun har takai haka?..."
Abbah har numfashinsa ne yake shirin ɗagewa tsabar ɓacin rai dake yanada hawan jini, Aunty Yolash ce ta tashi tana rirriƙe shi tare da bashi haƙuri tana rarrashinsa,
Pinky tana kwance ba abinda take sai kuka, ji nayi an ɗagota da hannu ɗaya ana janta suka nufi hanyar bakin ƙofa za'a fita da ita, idanuwanta ta buɗe tana ƙoƙarin ganin wanda yake shirin fita da ita, naga Razhdeen ne fuska ba annuri, daga nan ta saddaƙar cewa yau ranar mutuwarta ne, Ihu ta fara kurmawa tana ƙiran sunan Mommy, "wayyo Allah nah Mommy kizo ki temake Ni zasu kashe Ni, Mommy nah wayyo, Dan ALLAH Uncle Deen kayi haƙuri ka ƙyaleni, wallahi bazan ƙara baaa...."
Abbah kuwa cewa yake "kaje ka hukuntata tinda itama halin uwarta gareta, ba'a gidan nan za'a mun wannan iskanci ba..."
*ƳAR AMANA*🕊ï¸ðŸ•Šï¸ðŸ•Šï¸