Sashe 24
My Enemy Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ajiyar zuciya Aunty Yolash ta sauƙar tare da faɗin "hakane bawa yakan aikata kuskure daga baya yayi nadamar abinda ya aikata, amma ina so ki sani cewa duk wanda ya tuba don wuya ba lada haka tushen hausar take amma tinda har kika gane gaskiyar lamarin duk ba laifi, amma a gaskiya komawa gidan General zai miki wuya domin a halin yanzu Yayana ba macen da yake jin daɗin tarayya da ita sai Amaryarsa, zai yi wuya ya zauna da wata mace bayan ita, kuma shi daman baya son zama da mata biyu kasancewa shi ba mazauni bane, shin a cikin maganar ki taimakon mai kike so nayi miki?...."
Hajiya Kilishi tana kuka ta ce "inaso ki sa baki General ya mai dani gidansa..."
Aunty Yolash ta ce "kai kai kaiiii ai duk yanda nake da General bazai taɓa yadda da wannan batun ba hasali ma ki ja mun baƙin jini a wurin sa, ga nan abokansa kije ki same su mana..."
Hajiya Kilishi ta ce "kab abokansa waɗanda na sani babu wurin wanda banje ba amma ya ƙi sauraronsu akan batun, bansan wani irin zuciya ne da shi ba..."
Sauƙe numfashi Aunty Yolash tayi tare da faɗin "ke ma bakya jin magana Hajiya Kilishi, ke kika jawa kanki komai wallahi duk abinda ya faru laifinki ne, inda ace kin kama kanki da mutuncinki a gidan mijinki da duk hakan bata faru ba, me zaisa kiyi abinda har Aurenki zai mutu? kin dai san General yana da matuƙar haƙuri amma idan aka kai shi maƙura baya taɓa sauƙowa akan abu, kuma idan ya cire abu a ransa baya taɓa maida shi, kin ƙure shi sosai, kinsan babu wanda zai iya riƙe ki mai zai sa ki bar gidan mijinki? kowa yana rufawa kansa asiri amma ke kina ƙara bankaɗawa kanki asiri, Ni a koda yaushe ina baki shawara bawai bana sonki bane amma kika ɗauki ƙiyayya kika ɗora mun, gani kike babu maƙiyiyar ki kamar ni, Ni kuma ina zaune da mutum da zuciya ɗaya ne, kuma wallahi wannan ranar nake guje miki kuma gashi yazo shin meye amfanin haka?..."
Hajiya Kilishi babu abinda take sai kuka ta ce "bayan fitowa ta daga gidan mijina ba ƙaramin wahala nake sha ba, kowa ya kasa riƙe ni, da farko a gidan ƙanwar mahaifiyata nake zaune amma itama daga baya ta kore ni wai bazata iya riƙe ni ba, sai na koma gurin baffana shima matansa sun hanani zama a gidan, duk zuriya babu yanda ban zagaya ba amma an rasa wanda zai riƙe ni daga ƙarshe dai zaman Abuja ya gagare ni saboda babu yanda zan shiga ga tsadar rayuwa ga bani da kuɗi, abincin da zan saya na ci gagara ta yake, yanzu haka ina zaune a garin suleja na kama gidan haya, to kuɗin da zan biya babu kuma watannin biyan kuɗin ya ƙare, bansan da wanne zan ji ba, shin da kuɗin abinci yau da kullum ko kuma kuɗin hayan gidan da nake?..."
Hajiya Kilishi ta ƙarasa tana fashewa da kuka.
Aunty Yolash sarkin tausayi ba ƙaramin tausaya mata tayi ba, ta ce "ke nam babu yanda zaki je ki zauna? abincin da zaki ci gagaranki yake shin ina Alhajan ƙawayenki matan manya-manyan masu kuɗi? shin kina nufin ki ce bakida bazawarai? to ma ina wanda kike bin sa hotel bazai iya taimaka miki bane?..."
Hajiya Kilishi dakatar da yin kukan tayi tana faɗin "yanzu na gane su waye masoyana da kuma maƙiyana, ƙawaye na suna hulɗa dani ne saboda kuɗina da kuɗin mijina, basa kula talakawa idan suka fiskanci bakada komai ka tsiyace daga nan zasu raba hanya da kai duk haka suke, suna ƙawance da wacce take da kuɗi, kuɗi sai kuɗi to ni kuma yanzu banida komai, aikin da nake yi ake biyana maƙudan kuɗaɗe kamfanin General ne kuma ya sallame ni, ko ba kuɗin salary General baya barina ba kuɗi,
Bazawarai kuma su waye zasu zo mun? idan kinga mutum yazo mun to bada niyar Aure yazo ba sai da niyar iskanci, Ni kuma na shiryu bazan iya bada kaina ba saboda kuɗi duk da wahalar da nake sha, duk kowa ya gujeni, wasu sunyi blocking number na wasu kuma idan na ƙira su basa picking, wai daman haka rayuwar take?...."
Ta ƙarisa maganar tana kallon Aunty Yolash,
Aunty Yolash ta ce "yanda kika yi dai haka akayi miki, Allah ya ɗanɗana miki kiji yanda sauran mutanen suke ji da zaran sun zo neman taimakon ki, shin ba haka kike yi ba? idan kina tare da mutum da zaran ya rasa wani abu shikenam zaki nemi hanyar barinsa a cikin ƙunci maimakon ki taimaka masa, hatta ƴan uwanki bakya taimaka musu shiyasa suma yanzu bazasu iya taimaka miki ba, kar ma kiga laifinsu domin ke kika fara ɗanɗana musu raɗaɗin haka, duk wani ɗan uwanki da zaran yazo yanda kike zaki nemi kici masa mutunci sannan ki kore shi, wallahi ban taɓa ganin mata marar wayo ba sai ke, ai inda Ni ce a mazanninki babu wani ɗan uwana da zaiyi kukan talauci, jansu zanyi a jikina suma su ci arziƙi saboda nasan wata rana wani abu zai iya faruwa dani wanda dole sai ƴan uwana ne zasu mun, amma ke daga ke sai ƴaƴanki bakya son wani ya raɓi jikinki, ga shi yanzu kin ci ke kaɗai sannan kina shan wahala ke kaɗai yanzu meye amfanin haka?..."
Hajiya Kilishi ido yayi jawur fuska a kokkoɗe ta ce "nayi nadama bazan ƙara aikata makamancin abinda na aikata a baya ba..."
Aunty Yolash ta ce "tam yanzu dai kin san masu sonki da kuma waÉ—anda basa sonki..."
Hajiya Kilishi tayi saurin katse ta da cewa "indai ata ɓangaren ƙawaye da kuma abokai babu masu Sona tsakani da ALLAH, ƴan uwana kuma daman haushi na suke ji shiyasa suka kasa taimaka mun..."
Aunty Yolash ta ce "tam yanzu dai idan Allah yasa kika koma gidan General babu ruwanki da wani ɗagun kai da girman kai da wulaƙanci da kuma masifa ki kama kanki, kinga wacce take zaune yanzu babu ruwanta batada tashin hankali, idan wani abu ya ɓullo za'a ce ke ce..."
Hajiya Kilishi ta ce "ai babu abinda zai faru Insha Allahu, zan riƙe abokiyar zamana hannu bibbiyu..."
Aunty Yolash murmushi tayi sannan ta ce "Ni na manta ashe dai kince bakya son zama da kishiya..."
Hajiya Kilishi ta ce "wallahi ruÉ—in duniya ne amma ni yanzu General ko mata uku ya jera to zanje na zauna ata huÉ—un..."
Aunty Yolash ta ce "to shikenam gobe Insha Allahu zan shiga jirgi naje Abuja na same shi da maganar duk yanda ake ciki zanje har yanda kike a sulejan na sanar miki..."
Hajiya Kilishi bata san lokacin da ta washe baki ba na farin ciki ta ce "Nagode sosai Auntyn yara Allah ya saka da ALKHAIRI..."
Aunty Yolash ta ce "kar ki damu, a rayuwata na tsani ganin uwa ta fita tabar ƴaƴanta a gida ina jin takaicin haka, amma sai dai ƙaddara ta riga fata, za'a san yanda za'ayi Insha ALLAHU...."
Hajiya Kilishi cikin nuna farin ciki ta miƙe tare da faɗin "shikenam Auntyn yara Ni zan koma suleja..."
Aunty Yolash ta ce "ok muje na sauƙe ki a airport to..."
Hajiya Kilishi ta ce "a'ahh bani da kuÉ—in hawa jirgi, zanje na shiga mota..."
Aunty Yolash gani É—aya tayi wa Hajiya Kilishi tasan bata da kuÉ—in motar ma kawai tayi iya kuÉ—in zuwa ne,
Ta ce "shin kina da na motar ne?..."
Hajiya Kilishi sunkuyar da kanta tayi ƙasi tare da girgiza kai,
Aunty Yolash ta ce "Ok kar ki damu, idan kika ce mota zaki shiga zaki yi dare ne, muje kawai na biya miki na jirgin..."
Aunty Yolash ta haura saman upstairs yanda room ɗinta yake taje ta ɗauko wasu maƙudan kuɗaɗe a cikin baƙar laida ta sauƙo tare da miƙawa Hajiya Kilishi tana faɗin "ga wannan kije ki biya duk kan buƙatunki da su, ki biya kuɗin haya sannan ki sayi kayayyakin abinci da dai sauran abubuwan da kike buƙata..."
Cikin nuna farin ciki Hajiya Kilishi ta karɓa tana godiya haɗi da cewa "wannan ai zan daɗe ina amfana da su.."
Aunty Yolash ta ce "to muje na biya miki kuÉ—in jirgi ..."
A tare suka fita Aunty Yolash ta ja su a mota sai airport....
___________________________________
A bangaren Ƴar Amana kuwa har zuwa wannan lokutan fushi take da Razhdeen saboda ya tafi ya barta, ma sha ALLAH sai haɓaka take tayi, a shekara ɗaya ta zankaɗe tayi tsayi ga dirin jiki kamar wacce ake hura mata iska, fatar jikinta kuwa kamar zaka taɓa jini ya fito tsabar farin da tayi ba ƙaramin kyau tayi ba, ga gashin kanta a baje kamar wanda ake ƙara jansa sai tsayi yake yana tafe da murɗi-murɗinsa, ta ko ina a jikinta ya ciko hatta breast ɗinta sun fito sun cicciko, ƙugunta kuwa ba'a magana daman kuma can Ƴar Amana ba siririya bace da ɗan dirinta balle yanzu ta haɗa da cikar budurci, hips ɗinta irin mai shape ɗin kifi ne.
Tana zaune a falo tana kallo kwatsam taji Madam Blessing ta zauna kusa da ita tana shirin miƙa mata wayar hannunta, da sauri Ƴar Amana ta ture wayar tare da miƙe wa tabar falon ta koma room ɗinta domin tasan Razhdeen ne yake son yin video call da ita, tinda Razhdeen ya tafi tsawon shekara guda Ƴar Amana bata taɓa yadda sunyi video call ba shi kuwa kullum sai ya ƙira madam blessing akan ta haɗa shi video da Saararsa amma fur Ƴar Amana taƙi yadda hatta photo bata taɓa yadda tayi ba tinda Razhdeen ya tafi saboda tasan indai ta ɗauka sai madam blessing ta tura masa, kullum sai yayi complain akan a turo masa photon Saarah amma Ƴar Amana taƙi, har takai ta kawo yanzu indai taga waya a hannun madam blessing bata yadda ta zauna a kusa da ita saboda kar ta ɗauke ta a photo, a tunanin ta indai yaji zafin haka zai dawo.
Hajiya Kilishi tana kuka ta ce "inaso ki sa baki General ya mai dani gidansa..."
Aunty Yolash ta ce "kai kai kaiiii ai duk yanda nake da General bazai taɓa yadda da wannan batun ba hasali ma ki ja mun baƙin jini a wurin sa, ga nan abokansa kije ki same su mana..."
Hajiya Kilishi ta ce "kab abokansa waɗanda na sani babu wurin wanda banje ba amma ya ƙi sauraronsu akan batun, bansan wani irin zuciya ne da shi ba..."
Sauƙe numfashi Aunty Yolash tayi tare da faɗin "ke ma bakya jin magana Hajiya Kilishi, ke kika jawa kanki komai wallahi duk abinda ya faru laifinki ne, inda ace kin kama kanki da mutuncinki a gidan mijinki da duk hakan bata faru ba, me zaisa kiyi abinda har Aurenki zai mutu? kin dai san General yana da matuƙar haƙuri amma idan aka kai shi maƙura baya taɓa sauƙowa akan abu, kuma idan ya cire abu a ransa baya taɓa maida shi, kin ƙure shi sosai, kinsan babu wanda zai iya riƙe ki mai zai sa ki bar gidan mijinki? kowa yana rufawa kansa asiri amma ke kina ƙara bankaɗawa kanki asiri, Ni a koda yaushe ina baki shawara bawai bana sonki bane amma kika ɗauki ƙiyayya kika ɗora mun, gani kike babu maƙiyiyar ki kamar ni, Ni kuma ina zaune da mutum da zuciya ɗaya ne, kuma wallahi wannan ranar nake guje miki kuma gashi yazo shin meye amfanin haka?..."
Hajiya Kilishi babu abinda take sai kuka ta ce "bayan fitowa ta daga gidan mijina ba ƙaramin wahala nake sha ba, kowa ya kasa riƙe ni, da farko a gidan ƙanwar mahaifiyata nake zaune amma itama daga baya ta kore ni wai bazata iya riƙe ni ba, sai na koma gurin baffana shima matansa sun hanani zama a gidan, duk zuriya babu yanda ban zagaya ba amma an rasa wanda zai riƙe ni daga ƙarshe dai zaman Abuja ya gagare ni saboda babu yanda zan shiga ga tsadar rayuwa ga bani da kuɗi, abincin da zan saya na ci gagara ta yake, yanzu haka ina zaune a garin suleja na kama gidan haya, to kuɗin da zan biya babu kuma watannin biyan kuɗin ya ƙare, bansan da wanne zan ji ba, shin da kuɗin abinci yau da kullum ko kuma kuɗin hayan gidan da nake?..."
Hajiya Kilishi ta ƙarasa tana fashewa da kuka.
Aunty Yolash sarkin tausayi ba ƙaramin tausaya mata tayi ba, ta ce "ke nam babu yanda zaki je ki zauna? abincin da zaki ci gagaranki yake shin ina Alhajan ƙawayenki matan manya-manyan masu kuɗi? shin kina nufin ki ce bakida bazawarai? to ma ina wanda kike bin sa hotel bazai iya taimaka miki bane?..."
Hajiya Kilishi dakatar da yin kukan tayi tana faɗin "yanzu na gane su waye masoyana da kuma maƙiyana, ƙawaye na suna hulɗa dani ne saboda kuɗina da kuɗin mijina, basa kula talakawa idan suka fiskanci bakada komai ka tsiyace daga nan zasu raba hanya da kai duk haka suke, suna ƙawance da wacce take da kuɗi, kuɗi sai kuɗi to ni kuma yanzu banida komai, aikin da nake yi ake biyana maƙudan kuɗaɗe kamfanin General ne kuma ya sallame ni, ko ba kuɗin salary General baya barina ba kuɗi,
Bazawarai kuma su waye zasu zo mun? idan kinga mutum yazo mun to bada niyar Aure yazo ba sai da niyar iskanci, Ni kuma na shiryu bazan iya bada kaina ba saboda kuɗi duk da wahalar da nake sha, duk kowa ya gujeni, wasu sunyi blocking number na wasu kuma idan na ƙira su basa picking, wai daman haka rayuwar take?...."
Ta ƙarisa maganar tana kallon Aunty Yolash,
Aunty Yolash ta ce "yanda kika yi dai haka akayi miki, Allah ya ɗanɗana miki kiji yanda sauran mutanen suke ji da zaran sun zo neman taimakon ki, shin ba haka kike yi ba? idan kina tare da mutum da zaran ya rasa wani abu shikenam zaki nemi hanyar barinsa a cikin ƙunci maimakon ki taimaka masa, hatta ƴan uwanki bakya taimaka musu shiyasa suma yanzu bazasu iya taimaka miki ba, kar ma kiga laifinsu domin ke kika fara ɗanɗana musu raɗaɗin haka, duk wani ɗan uwanki da zaran yazo yanda kike zaki nemi kici masa mutunci sannan ki kore shi, wallahi ban taɓa ganin mata marar wayo ba sai ke, ai inda Ni ce a mazanninki babu wani ɗan uwana da zaiyi kukan talauci, jansu zanyi a jikina suma su ci arziƙi saboda nasan wata rana wani abu zai iya faruwa dani wanda dole sai ƴan uwana ne zasu mun, amma ke daga ke sai ƴaƴanki bakya son wani ya raɓi jikinki, ga shi yanzu kin ci ke kaɗai sannan kina shan wahala ke kaɗai yanzu meye amfanin haka?..."
Hajiya Kilishi ido yayi jawur fuska a kokkoɗe ta ce "nayi nadama bazan ƙara aikata makamancin abinda na aikata a baya ba..."
Aunty Yolash ta ce "tam yanzu dai kin san masu sonki da kuma waÉ—anda basa sonki..."
Hajiya Kilishi tayi saurin katse ta da cewa "indai ata ɓangaren ƙawaye da kuma abokai babu masu Sona tsakani da ALLAH, ƴan uwana kuma daman haushi na suke ji shiyasa suka kasa taimaka mun..."
Aunty Yolash ta ce "tam yanzu dai idan Allah yasa kika koma gidan General babu ruwanki da wani ɗagun kai da girman kai da wulaƙanci da kuma masifa ki kama kanki, kinga wacce take zaune yanzu babu ruwanta batada tashin hankali, idan wani abu ya ɓullo za'a ce ke ce..."
Hajiya Kilishi ta ce "ai babu abinda zai faru Insha Allahu, zan riƙe abokiyar zamana hannu bibbiyu..."
Aunty Yolash murmushi tayi sannan ta ce "Ni na manta ashe dai kince bakya son zama da kishiya..."
Hajiya Kilishi ta ce "wallahi ruÉ—in duniya ne amma ni yanzu General ko mata uku ya jera to zanje na zauna ata huÉ—un..."
Aunty Yolash ta ce "to shikenam gobe Insha Allahu zan shiga jirgi naje Abuja na same shi da maganar duk yanda ake ciki zanje har yanda kike a sulejan na sanar miki..."
Hajiya Kilishi bata san lokacin da ta washe baki ba na farin ciki ta ce "Nagode sosai Auntyn yara Allah ya saka da ALKHAIRI..."
Aunty Yolash ta ce "kar ki damu, a rayuwata na tsani ganin uwa ta fita tabar ƴaƴanta a gida ina jin takaicin haka, amma sai dai ƙaddara ta riga fata, za'a san yanda za'ayi Insha ALLAHU...."
Hajiya Kilishi cikin nuna farin ciki ta miƙe tare da faɗin "shikenam Auntyn yara Ni zan koma suleja..."
Aunty Yolash ta ce "ok muje na sauƙe ki a airport to..."
Hajiya Kilishi ta ce "a'ahh bani da kuÉ—in hawa jirgi, zanje na shiga mota..."
Aunty Yolash gani É—aya tayi wa Hajiya Kilishi tasan bata da kuÉ—in motar ma kawai tayi iya kuÉ—in zuwa ne,
Ta ce "shin kina da na motar ne?..."
Hajiya Kilishi sunkuyar da kanta tayi ƙasi tare da girgiza kai,
Aunty Yolash ta ce "Ok kar ki damu, idan kika ce mota zaki shiga zaki yi dare ne, muje kawai na biya miki na jirgin..."
Aunty Yolash ta haura saman upstairs yanda room ɗinta yake taje ta ɗauko wasu maƙudan kuɗaɗe a cikin baƙar laida ta sauƙo tare da miƙawa Hajiya Kilishi tana faɗin "ga wannan kije ki biya duk kan buƙatunki da su, ki biya kuɗin haya sannan ki sayi kayayyakin abinci da dai sauran abubuwan da kike buƙata..."
Cikin nuna farin ciki Hajiya Kilishi ta karɓa tana godiya haɗi da cewa "wannan ai zan daɗe ina amfana da su.."
Aunty Yolash ta ce "to muje na biya miki kuÉ—in jirgi ..."
A tare suka fita Aunty Yolash ta ja su a mota sai airport....
___________________________________
A bangaren Ƴar Amana kuwa har zuwa wannan lokutan fushi take da Razhdeen saboda ya tafi ya barta, ma sha ALLAH sai haɓaka take tayi, a shekara ɗaya ta zankaɗe tayi tsayi ga dirin jiki kamar wacce ake hura mata iska, fatar jikinta kuwa kamar zaka taɓa jini ya fito tsabar farin da tayi ba ƙaramin kyau tayi ba, ga gashin kanta a baje kamar wanda ake ƙara jansa sai tsayi yake yana tafe da murɗi-murɗinsa, ta ko ina a jikinta ya ciko hatta breast ɗinta sun fito sun cicciko, ƙugunta kuwa ba'a magana daman kuma can Ƴar Amana ba siririya bace da ɗan dirinta balle yanzu ta haɗa da cikar budurci, hips ɗinta irin mai shape ɗin kifi ne.
Tana zaune a falo tana kallo kwatsam taji Madam Blessing ta zauna kusa da ita tana shirin miƙa mata wayar hannunta, da sauri Ƴar Amana ta ture wayar tare da miƙe wa tabar falon ta koma room ɗinta domin tasan Razhdeen ne yake son yin video call da ita, tinda Razhdeen ya tafi tsawon shekara guda Ƴar Amana bata taɓa yadda sunyi video call ba shi kuwa kullum sai ya ƙira madam blessing akan ta haɗa shi video da Saararsa amma fur Ƴar Amana taƙi yadda hatta photo bata taɓa yadda tayi ba tinda Razhdeen ya tafi saboda tasan indai ta ɗauka sai madam blessing ta tura masa, kullum sai yayi complain akan a turo masa photon Saarah amma Ƴar Amana taƙi, har takai ta kawo yanzu indai taga waya a hannun madam blessing bata yadda ta zauna a kusa da ita saboda kar ta ɗauke ta a photo, a tunanin ta indai yaji zafin haka zai dawo.