← Book details My Bestie's Husband Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 44

Sashe 2

My Bestie's Husband Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bata jira amsaba ta miqe shina Muhseen ya miqe yana tsokanarta yace “daki ai baya tashi ragaya ta zauna ba muje tunda mun sallami baqinmu mu jira ango da amarya danni wlh bacci nakeji ma" da wannan suka jera suka Isa inda motar take suka shiga suka zauna suna dan taba hirarsu.
Duk hirar akan bikinne sukeyi inda rabin hankalinta yake kan tunanin dalilin wannan mayataccen kallo da bibiya da mijin aminiyarta yafarayi Mata tundaga kallon farko, kasa jurewa tayi ta dago ta dubi Muhseen da hankalinsa yake kan danna wayarsa tace “Mr Muhseen Wlh banason kallo a rayuwata takurani yake ya hanani sakat"
Dagowa yayi ya zuba Mata ido yace “waye ya dameki da kallo?" Ajiyar zuciya taja ta kawar dakai tace ka share kawai" yariga yasan inda ta dosa fada masane bazatayi ba hakan yashi sake kallonta yace “to Rafi'ah meye laifin mutane don sunbawa ido abinci kedince Allah ya ginaki ginin gaske wlh na dade banga mace me cikar halittarki ba kinsan ba kowa yake iya gani ya dauke Kai ba kekuma gaki kamar me aljanu da mutum yace yanasonki sai ki Kama gaba dashi"

Murmushi tayi tace “wannan dalilin ne yasa banason kallo saboda nasan daga kallo saqo yake shiga zuciya nikuma na tsani ma ace anasona wlh tunda Yassar ya rasu nakejin bana sha'awar sake soyayya da kowa" tabe baki yayi yace “wanda ya tafi ya tafi kenan bazai dawo ba garama ki manta da komai ki fara sabuwar rayuwa kina ganidai ga aminiyarki yanzun bikinta akeyi ke kanki bazakiji dadin rayuwa ke dayaba ko Ina kun tare ku tashi nan ku fadi csn kwanciyar bacci ke rabaku itama in kunso"
Hadiye wani Abu tayi me ciwo tace “babu komai ana tare insha Allahu inasa ran zabi mafi kyawun kyau gurin lillahi Muhseen badagani bane zuciyata takasa karbar madadin Yassar shi na fara so shi ya huda zuciyata shiyasa madadinsa yayi wahala"
Ji sukayi ana qwanqwasa glass din gabanta ya fadi lkcn da Muhseen ya sauke glass din idanunsa akanta yace “kazo ka sata a corner me kake karanta mata?" Shafa kansa yayi ya bude masa yace “kawai nasiha nakeyi Mata itama ta fitar da miji cikin masoyanta tayi aure saboda lkc qurewa yakeyi" bai wani bawa mgnr muhimmanci ba suka shiga shida Ni'imah Muhseen yaja motar suka tafi.

Tunda suka taho babu me cewa wani qala lkcn da sukaje duk motocin sun jima da zuwa anayin parking Rafi'ah ta bude qofar tanayiwa Muhseen Saida safe ta shige cikin gidan mutane nayita yimata tsiyar saura ita itama ta fitar da miji suzo susha shagali murmushi kawai takeyi ta shige ciki ta haye saman ta fada dakin Ni'imah ta kwanta tana mayar da numfashi.
A haka Ni'imah tazo ta sameta t zauna a gefenta tace “Sweet yace kiyi hqr da laifin da yayi mki kike gudun hada inuwa dashi"
Dagowa tayi ta dubeta tace “baimin komai ba Bestie kaina kw ciwo nakeson samun relief" miqewa Ni'imah tayi ta cire kayanta tace “ke kika sani ni wanka zanyi na kwanta" itama miqewa tayi ta cire rigar jikinta ta daura zani Ni'imah na fitowa ta fada wankan tana fitowa taja bargo tare da addu'a bacci ya dauketa.
Saboda gajiyar da sukayi Basu farka ba sai da Rana ta fito shima momy ce mahaifiyar Ni'imah tazo ta tashesu suka tashi Ni'imah tayi wanka tayi sallah kasancewar sun makara ita Kuma dake ba sallar takeyi ba tayi wankan sukazo sukayi zaman shiryawa me kwalliyar ta  shigo tayi musu suna gama shiryawa aka daura auren rungume juna sukayi suka saki wani ihu daya janyo hankalin kowa dake gdan.........

Nufosu sukayi da sauri suka riqosu aka rabasu daqyar tare da zaman rarrashinsu itadai Rafi'ah zazzabi ne ya rufeta ta koma ta kwanta tana rawar sanyi angwayen da suka shigone sukaga meke faruwa Ja'afar ya Kira wani abokinsa likita yazo ya dubata yabata magunguna tasha ta kwanta yinin ranar bata iya tsinanawa kanta uwar komai ba sai bacci da takeyi har aka gama bikin da yamma ta farka anata shirye shiryen Kai amarya batare data bari kowa yaganta ba ta sulale tabar gidan bikin ta cikin saa tana fita tasamu napep ta nufi unguwarsu ta shiga gidansu babu kowa sai kishiyar mamanta mama tana wajen kai amarya.

Aunty Murja tana ganinta tasan ba lafiya ba ganin bata saurari kowa ba ta shige dakinta ta kullo yasata miqewa tabita ta tarar da ita zaune ta hade Kai da gwiwa sai kuka takeyi, zama tayi kusa da ita tace “ni bantaba ganin irin wannan rayuwa taku ta qaryaba to dawwama zakuyi babu aure yanzu da Allah yayi naki auren ita ya zatayi da sai yanzu Allah ya nufi nata? Dama kun hqr kunsawa zuciyarku hqr da salama kowacce mace wannan lkcn take jira ita ta tafi Abuja ke Kuma waye yasan inda zaki"
Shiru tayi batace komai ba sai kukanta da takeci gaba dayi ganin bajin lallashin zatayi ba yasa Anti Murja miqewa tacd idan ya isheki kyayi Shiru nikam nayi nan" tana fita wayarta tafara ring ta duba taga number Bestie ce ta mayar ta kife saboda bata buqatar wani Abu da zai qara daga Mata hankali a wannan lkcn hakance tasata tayi kwanciyarta, Ni'imah tayi Mata misscall yafi ashirin taqi dagawa qarshe ma ta kashe wayar haka tana kuka tana Kiran Bestie aka sata a mota aka nufi wani Martaba Estate dake cikin garin na Bauchi domin Kai amarya.

Saida komai ya lafa akakai amarya dakinta gdanta babba me kyau da tsari an zuba kaya Kuma ankashe kudi a gidan kasancewar iyayen Ni'imah masu haline shima kuma mijin da arziqinsa dan sarautar Azare ne Ja'afar Wakil suna tashen kudi da mulki mahaifinsa ne abokin mahaifin Ni'ima sune suka hada auren cikin wata biyu akayi komai aka gama abinka da masu data a hannunsu.
Angwayen ne zaune cikin mota Muhseen ya dubi Ja'afar yace “kai kanada matsala baka iya control din zuciyarka ba don Allah Ja'afar na roqeka kads ka soma wannan katobarar ita zuciya tausarta akeyi ba komai ake qyalets tayi abinda takeso ba kada kasa ka zamo silar yankewar wannan kyakkyawan zumunci da aka faroshi tun yarinta Ja'afar Mata basuda hankali akan wannan qaramin issue din sai hankalin kowa ya tashi koda yake inada yaqinin Rafi'ah bazata taba baka fuskaba"

Girgiza Kai yayi yace “Muhseen bakada adalci a rayuwarka 34 years muna tare dakai katabajin nace maka inason mace da aure wlh da gaske nakeson Rafi'ah tsakanin jiya da yau zuciyata tana azabtuwa da qaunarta bansan meyesa hakan ta faru ba meyesa bansanta ita kadaiba meyesa batazomin babu alaqa ba sai tazomin a matsayin aminiyar matata Muhseen kabani mafita wlh idan har banga Rafi'ah a daren nan ba bazan iya yiwa yarinyar nan komai ba Kai nifa badan lkc ya qure ba da zuwa zanyi na samu Dad na fada masa a janye na samu wacce nakeso wacce na dade Ina mafarkin samu irin matar da na dade Ina zanawa a zuciyata"
Sarai yasan halin abokin nasa iyakar gaskiyarsa yake fada shidin ba mutumne ma'abocin qarya ba kuma bai iya boye Abu a ransa ba, ji yayi ya damqesa yace “don Allah don annabi kakaini naganta wlh babu abinda zance Mata Muhseen iyakar ganine insson sanin halin da take ciki bansan hanyar gidansu ba da tuni na tafi"

Badon Muhseen yaso ba ya juya motar daga gurin da sukazo siyawa amarya kaza suka nufi unguwar su Rafi'ah a bakin get suka tarar da Abba da me gadi suna tattaunawa saboda haka Kai tsaye shi suka nufa suka gaisa yace bai ganesu ba Muhseen yace “Abba surukanka ne mijin yarkane da ka aurar yau Ni'imah shine tace muzo mu gano Mata meye ya hana Bestie dinta zuwa rakata gidan mijinta"
Dariya Abba yayi irin tasu ta manya yace “kayy Amma yaro yarone shine kums kuka dauko jiki Kuma da taya shirme hauka, bari na shiga na gano muku ita  naji uwayenta suna cewa batada lfy ma"
Shigewa yayi ciki Ja'afar ya miqe ya daga hannu sama yayi hamdala babu jimawa saiga Abba ya fito yace “ai kawai ku shiga tanacan ma amai taketa fama ita dama jinyarta amai kamar me yaron ciki" wani dadine ya cika zuciyar Ja'afar ya fadada murmushinsa Muhseen ya harareshi tare dayin qwafa kan ya ankara tuni Ja'afar yaje qofar falon suka shiga da Abba jansu Abba yayi har saman ya tura qofar ya shiga tana kwance daga ita sai dogon sikert da taja har qirjinta ko bra babu a jikinta har yanzu kuka takeyi Ammi na rarrashinta tsaki Abba yayi yace.

“Do Allah amina ku qyaleta tayita kukan gajiyane batayi ba yo naji iskanci so kike a qyaleta kuyita babare a gari ke babu aure ita babu kaji wani sakarci" sake shigewa jikin Ammi tayi ta shafa kanta tace “to bandama abin me sunan manya kema ai addu'a mukeyi Allah ya kawo mijin mu auraddake kema kije kiyi bautaTashi tayi zaune daidai lkcn da Ammi suke gaisawa dasu Muhseen idon Ja'afar akan qirjinta ya sauke numfashi tare da cewa “ya jikinki" wata uwar harara ta watsa masa ta dauki hijjab dinta ta zura ta koma can qarshen gadon ta kwanta ba Shiba hatta Abba Saida abin yabashi dariya yace “to Ja'afaru kai me laifine fa ka rabata da aminiyarta"
Murmushi yayi a ransa yace “kema very soon zan daukeki sai naga ya amintar zata kaya tunda kunayiwa dodo daya tsafi" a fili kuwa cewa yayi “kiyi hqr bansan da wannan amintar ba dana bari anyi Rana daya Kinga da duk haka bata faruba".......

_Please share_
_And_
_Comments_

*_Oum Hairan_*
[1/1, 10:17 AM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's Husband_*

*_Ummuh Hairan_*

*_Happy birthday Nazifi Yarimah_*

_Wannan shafin sadaukarwa ne ga Nazifi Yareemah Happy birthday more shekaru da nauyayan money in your bank account da Mata ta gari_

*3-4*
Chapter 2 · 0% Book details