Sashe 12
My Bestie's Husband Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Numfashi Nina ta sauke tace “to ilahi ya kyauta Amma ki daina kukannan kiyi addu'a ki tashi muje muyi C.A dinnan mu fito sai ki tafi gida nima gda zan tafi tunda anbamu hutun qwaqwalwa hakan zaibaki damar samo bakin zaren domin wannan mutumin da gaske yake wlh" miqewa tayi suka fita sai yamma suka gama C.A din ko hostel bata koma ba ta nufi gida hakanan tunda ta sauka a mota ta tari adaidaita taji gabanta yana faduwa jikinta a mace ta shiga gidan tana jin faduwar gabanta na tsananta,
Ajiyar zuciya tayi ganin parlour babu kowa tayi hayewarta sama tayi wanka ta canza kaya sannan ta fito,
********
*_Waiwaye adon tafiya_*
Mahaifin Rafi'ah Alh Nuhu mutum me jan iyali a jiki da kyautata musu kwata² su ukune Allah yabashi Yaya Rashid Aunty Raziqa sai ita auta Rafi'atuh inda suka taso cikin gata saboda mahaifinsu dan bokone Kuma dan siyasa sannan dan kasuwa da arziqi a gdansu bakin gwargwado gashi dason taimakon talakawa.
Don asalin alaqarta ma da Ni'imah cikin taimakon mahaifinta ne shekaru 18 baya lkcn sunada 3 years a duniya mahaifin Ni'ima maqocin shagon Abba ne a kasuwa sai karayar arziqi ta sameshi dake harkar gold sukeyi barayi suka shigo kasuwar sukayi barna Abba ma an taba dukiyarsa sosai amma dake yafisu qarfi Kuma shi kayansa ne na kansa yasa bai tozarta ba inda Alh Sabo mahaifin Ni'ima ya kasance kayansa hadin gwiwa ne don kaso 70% ba nasa bane gashi yana cikin wadanda akafi yiwa barna.
To dake akwai fahimtar juna tsakanin Alh Sabo da Alh Nuhu yasa Alh Sabo yana kuka yake zayyanewa Nuhu halin da yake ciki yana fada masa yasai da gidansa ya rage bashin kudin mutane duk wata kadara tasa ya siyar Amma bai gama biyaba har yanzu da saura 14 million da ake binsa gashi ko abinda zasuci babu a gidansa gidanma sai gdan gado ya koma kuma mahaifiyarsa ta mutu tun yana qarami matar babansa Kuma basa shiri da matarsa don kullum ciki gori takeyi musu.
Sosai Alh Nuhu ya tausaya masa take yayi masa alqawarin bashi gurin zama a gdansa sannan zai biya Masa bashin Kuma zai zuba masa sabon kaya yake juyawa har Allah ya sake dagashi ranar Alh Sabo yayi kukan farin ciki hakance ta faru a ranar Sahura ta dawo gdansu Rafi'ah da zama duk wani alqawari da Abba yayiwa Dad ya cikashi ashe kudin na Sarki Muhammad Wakil ne mahaifin Ja'afar da aka Kai masa sai yace yabarshi kawai ya yafe masa wadanda ya karba na baya ma don banasa bane na abokinsa ne murna ta cika Dad suka taho abin mamaki Abba saiya miqa masa kudin yace yasai gda dasu Amma yaqi karba qarshe suka tsaya a tsakiya kan cewa saidai a sake zubasu a shago ya zamana shima da hannun jarinsa hakance ta faru iyayensu na juya kudinsu gidansu na zaune lfy Sahura irin matannan ne masu homa dajin su wasune sai fankama ta qaru sun samu ci gaba a aro domin ko a lkcn gdan Abba ba qarami bane sosai ta rinqa shigewa Ammi har suka zama qawaye inda aka samu akasi ita Sahura macece me yawo ita Kuma Ammi batada yawo hakance tasa Sahura tafita mutane gata tun a lkcn da bin malaman masifa itakuma Ammi komai akayi sai tace Allah zai iya mata.
Anan gdansu Rafi'ah aka haifi qanwar Ni'imah Yusrah sai sabon balli ya tashi musamman da Sarkin Wakil ya turo matarsa ta tsakiya wato Hajiya Fatsum barka habawa sai firita ita tazama babbar mace har matan sarakai ke zuwa Mata barka to dake hali yazo daya sai Sahura da Fatsum suka dinke duk da Fatsum ta girmi sahura don a lkcn ma yaronta autan ma yana Cairo yana karatu shikuma babban yana Uganda yana karatun Parmarcy matan Kuma biyu tayi musu aure Salma da Dija wanda sune manya.
Haduwarta da Hajiya Fatsum yasata qara kanainaye Dad duk abinda tace shi yakeyi gashi tun a wancan lkcn ba wata biyayya ta cikaba kwanciyar aure idan zaiyi da ita saiya biyata, Ni'imah kuwa da Rafi'ah Allah ya hada jininsu ko bacci baya rabasu dole duk inda sukayi bacci nan suke kwana tsakanin dakunan iyayen nasu sunada shekara biyar aka sasu makaranta tun a lkcn Rafi'ah tafi Ni'imah mayar da hankali a karatu ita wasane akanta sai fada da tsokanar masifa ga surutu ita Kuma Rafi'ah irin silent dinnan ce batada hayaniya duk da tsokanar Ni'imah batada qarfi idan tayo tsokana saita gudo gurin Rafi'ah to itamma ba qarfine da itaba Amma sai ta hana a daki Ni'imah tace a rama akanta.
Haka sukayita tafiya har secondary a jarabawa ne suka raba layi saboda Ni'imah bata samu abinda akesoba sai ta tafi Art ita Kuma Rafi'ah Science Ni'imah taso jan Rafi'ah ta koma art Amma taqi tace na marasa qoqarine a lkcn ne Kuma wata qauna ta qullu tsakanin Rafi'ah da dan wan babanta Yassar Amma fah soyayyar bada Rafi'an akeyi ba duk wani Abu saidai ya fadawa Ni'imah ita Kuma ta fada mata.
Daidai lkcn ne Dad yagama tamfatsa gdansa suka tashi suka koma ranar ansha daru dan Ni'imah qin tafiya tayi inda ita Kuma Hajiya Sahura ta nace saita tafi da yarta har wani cewa takeyi ga sabon gida mi zaayi da tsoho ta manta taohon yayi mata Rana na kusan shekara goma, dukkansu Saida sukayi rashin lfy aikuwa Basu rabuwa sai kwanciyar bacci musamman da Abba shima ya Gina wani gidan kusa da unguwar su Ni'imah duk da dadan nisa Amma yafi dayar unguwar kusa don Nan idan bakasa gandaba da qafama zakaje lkcn ne Abba ya qara aure aunty Murja itama me sanyin hali babu ruwanta, zamansu lfy Lau da Hajiya Amina wato ammi Kuma daidai lkcn ne akayi auren aunty Raziqa shima Yaya Rashid yayi aure gidan ya rage saura Rafi'ah kadai aikuwa itama guduwa tayi sai tayi sati bata gidan tana gdansu Ni'imah wannan aminta tana burge kowa don ko Yassar yasani idan zaisaiwa Rafi'ah Abu to dole saidai yasai biyu ita da Ni'imah inkuwa ba hakaba bama zata karba ba yasha tsokanar Rafi'ah yace “to waini ko ku biyu zan aurane?"
Dariya takanyi tace “nikam da nafi kowa murna gani ga Bestie na gidanmu daya mijinmu daya kaga shikenan aminta tayi Rana" duk lkcn da ta fadi haka sai Ni'imah ta harareta tace “Allah ya kiyaye nayi sharing miji ke nifa wlh Bestie yanda ban taso naga kishiya a gdanmu ba haka zan rayu babu kishiya don wlh yanda nakejin kishin mijina tun kafin nasanshi zan iya kasheshi ns kashe kaina akan batun qara aure" Rafi'ah takanyi murmushi tace “nikam banida matsala akan abinda ubangiji ya halalta Ni'imah kishi kafirci ne shiyasa nake roqon Allah kada ya jarabceni da zazzafan kishin da zai hanani yiwa mijina biyayya kishin da zaisani yin shirka kishin da zai hanani haduwa da Allah salin alin Ina roqon Allah indai yayoni a wannan sahun to ya qaddaramin mutuwa kafin nayi aure don bana fatan na zamewa mijina fitina masifa Kuma bala'in rayuwarsa"
Tsaki Ni'imah takanyi tace “ai saikiyi banza mara sanin ciwon Kai yo akanme zanyi addu'a Allah ya ragemin kishi bayan kishin adone ga ya mace nifa ko akan kishi da Yusrah ma bugawa zamuyi me qarfi ya kwaci kansa Kuma wlh don na kashe kishiya bazan taba nadama don nasan itama ba Sona takeyi ba da zata samu dama zata iya kasheni to da ka bari a kasheka gara Kai ka fara kashewa"
Yanayin Rafi'ah bata musu balle jayayya hakan yakansa da taja taga Ni'imah ta kafe akan ra'ayinta saita qyaleta abinda ta dauka wani abin halitta ce baka Isa canxa mutum ba haka watanni sukayita turawa tafi na tafiya har shekaru saura wata bakwai candynsu akasa auren Rafi'ah da Yassar murna gurinsu baa cewa komai Yassar kusan yanayinsu daya da Rafi'ah shima sanyine dashi yana nuna Mata madarar qauna me mantar da zuciya damuwa kullum suna tare babu abinda yake rabasu su uku sai bacci wani lkcn suna zaune sai kawai Ni'imah ta Kama kuka idan suka tambayeta sai tace tana tunanin ranar da Bestienta zata tafi ta barta ta kwana ta yini bata ganta ba, itama Rafi'ah saita Kama kuka abinka da quruciya tasha samun Yassar ita dashi ta roqeshi ya auresu su biyu yakanyi dariya yace.
“Bakida hankali yarinya ni ba mijin mace biyu bane Kuma ko zan qara aure Ni'imah batayimin ba banason farar mace sannan ta cika son jiki da rakin masifa ke nifah har tausayin mijinta nakeyi" akan haka Wai yana kushe Bestienta akwai lkcn da Saida sukayi sati uku basa mgn har saida manya suka shiga abin saboda ita Rafi'ah tata matsalar kafiyar masifa indai aka sake ta furta abu to komai wuyarsa sai tayi shiyasa iyayenta suke takatsantsan da furucinta dama Hausawa sunce muskilin mutum wuyar sha'ani gareshi shiyasa yawa yawan mutane suke cewa ta fiye jin izza kamar wata yar sarki wasu suce don tana dakyaune take wulaqanta mutane.
Ajiyar zuciya tayi ganin parlour babu kowa tayi hayewarta sama tayi wanka ta canza kaya sannan ta fito,
********
*_Waiwaye adon tafiya_*
Mahaifin Rafi'ah Alh Nuhu mutum me jan iyali a jiki da kyautata musu kwata² su ukune Allah yabashi Yaya Rashid Aunty Raziqa sai ita auta Rafi'atuh inda suka taso cikin gata saboda mahaifinsu dan bokone Kuma dan siyasa sannan dan kasuwa da arziqi a gdansu bakin gwargwado gashi dason taimakon talakawa.
Don asalin alaqarta ma da Ni'imah cikin taimakon mahaifinta ne shekaru 18 baya lkcn sunada 3 years a duniya mahaifin Ni'ima maqocin shagon Abba ne a kasuwa sai karayar arziqi ta sameshi dake harkar gold sukeyi barayi suka shigo kasuwar sukayi barna Abba ma an taba dukiyarsa sosai amma dake yafisu qarfi Kuma shi kayansa ne na kansa yasa bai tozarta ba inda Alh Sabo mahaifin Ni'ima ya kasance kayansa hadin gwiwa ne don kaso 70% ba nasa bane gashi yana cikin wadanda akafi yiwa barna.
To dake akwai fahimtar juna tsakanin Alh Sabo da Alh Nuhu yasa Alh Sabo yana kuka yake zayyanewa Nuhu halin da yake ciki yana fada masa yasai da gidansa ya rage bashin kudin mutane duk wata kadara tasa ya siyar Amma bai gama biyaba har yanzu da saura 14 million da ake binsa gashi ko abinda zasuci babu a gidansa gidanma sai gdan gado ya koma kuma mahaifiyarsa ta mutu tun yana qarami matar babansa Kuma basa shiri da matarsa don kullum ciki gori takeyi musu.
Sosai Alh Nuhu ya tausaya masa take yayi masa alqawarin bashi gurin zama a gdansa sannan zai biya Masa bashin Kuma zai zuba masa sabon kaya yake juyawa har Allah ya sake dagashi ranar Alh Sabo yayi kukan farin ciki hakance ta faru a ranar Sahura ta dawo gdansu Rafi'ah da zama duk wani alqawari da Abba yayiwa Dad ya cikashi ashe kudin na Sarki Muhammad Wakil ne mahaifin Ja'afar da aka Kai masa sai yace yabarshi kawai ya yafe masa wadanda ya karba na baya ma don banasa bane na abokinsa ne murna ta cika Dad suka taho abin mamaki Abba saiya miqa masa kudin yace yasai gda dasu Amma yaqi karba qarshe suka tsaya a tsakiya kan cewa saidai a sake zubasu a shago ya zamana shima da hannun jarinsa hakance ta faru iyayensu na juya kudinsu gidansu na zaune lfy Sahura irin matannan ne masu homa dajin su wasune sai fankama ta qaru sun samu ci gaba a aro domin ko a lkcn gdan Abba ba qarami bane sosai ta rinqa shigewa Ammi har suka zama qawaye inda aka samu akasi ita Sahura macece me yawo ita Kuma Ammi batada yawo hakance tasa Sahura tafita mutane gata tun a lkcn da bin malaman masifa itakuma Ammi komai akayi sai tace Allah zai iya mata.
Anan gdansu Rafi'ah aka haifi qanwar Ni'imah Yusrah sai sabon balli ya tashi musamman da Sarkin Wakil ya turo matarsa ta tsakiya wato Hajiya Fatsum barka habawa sai firita ita tazama babbar mace har matan sarakai ke zuwa Mata barka to dake hali yazo daya sai Sahura da Fatsum suka dinke duk da Fatsum ta girmi sahura don a lkcn ma yaronta autan ma yana Cairo yana karatu shikuma babban yana Uganda yana karatun Parmarcy matan Kuma biyu tayi musu aure Salma da Dija wanda sune manya.
Haduwarta da Hajiya Fatsum yasata qara kanainaye Dad duk abinda tace shi yakeyi gashi tun a wancan lkcn ba wata biyayya ta cikaba kwanciyar aure idan zaiyi da ita saiya biyata, Ni'imah kuwa da Rafi'ah Allah ya hada jininsu ko bacci baya rabasu dole duk inda sukayi bacci nan suke kwana tsakanin dakunan iyayen nasu sunada shekara biyar aka sasu makaranta tun a lkcn Rafi'ah tafi Ni'imah mayar da hankali a karatu ita wasane akanta sai fada da tsokanar masifa ga surutu ita Kuma Rafi'ah irin silent dinnan ce batada hayaniya duk da tsokanar Ni'imah batada qarfi idan tayo tsokana saita gudo gurin Rafi'ah to itamma ba qarfine da itaba Amma sai ta hana a daki Ni'imah tace a rama akanta.
Haka sukayita tafiya har secondary a jarabawa ne suka raba layi saboda Ni'imah bata samu abinda akesoba sai ta tafi Art ita Kuma Rafi'ah Science Ni'imah taso jan Rafi'ah ta koma art Amma taqi tace na marasa qoqarine a lkcn ne Kuma wata qauna ta qullu tsakanin Rafi'ah da dan wan babanta Yassar Amma fah soyayyar bada Rafi'an akeyi ba duk wani Abu saidai ya fadawa Ni'imah ita Kuma ta fada mata.
Daidai lkcn ne Dad yagama tamfatsa gdansa suka tashi suka koma ranar ansha daru dan Ni'imah qin tafiya tayi inda ita Kuma Hajiya Sahura ta nace saita tafi da yarta har wani cewa takeyi ga sabon gida mi zaayi da tsoho ta manta taohon yayi mata Rana na kusan shekara goma, dukkansu Saida sukayi rashin lfy aikuwa Basu rabuwa sai kwanciyar bacci musamman da Abba shima ya Gina wani gidan kusa da unguwar su Ni'imah duk da dadan nisa Amma yafi dayar unguwar kusa don Nan idan bakasa gandaba da qafama zakaje lkcn ne Abba ya qara aure aunty Murja itama me sanyin hali babu ruwanta, zamansu lfy Lau da Hajiya Amina wato ammi Kuma daidai lkcn ne akayi auren aunty Raziqa shima Yaya Rashid yayi aure gidan ya rage saura Rafi'ah kadai aikuwa itama guduwa tayi sai tayi sati bata gidan tana gdansu Ni'imah wannan aminta tana burge kowa don ko Yassar yasani idan zaisaiwa Rafi'ah Abu to dole saidai yasai biyu ita da Ni'imah inkuwa ba hakaba bama zata karba ba yasha tsokanar Rafi'ah yace “to waini ko ku biyu zan aurane?"
Dariya takanyi tace “nikam da nafi kowa murna gani ga Bestie na gidanmu daya mijinmu daya kaga shikenan aminta tayi Rana" duk lkcn da ta fadi haka sai Ni'imah ta harareta tace “Allah ya kiyaye nayi sharing miji ke nifa wlh Bestie yanda ban taso naga kishiya a gdanmu ba haka zan rayu babu kishiya don wlh yanda nakejin kishin mijina tun kafin nasanshi zan iya kasheshi ns kashe kaina akan batun qara aure" Rafi'ah takanyi murmushi tace “nikam banida matsala akan abinda ubangiji ya halalta Ni'imah kishi kafirci ne shiyasa nake roqon Allah kada ya jarabceni da zazzafan kishin da zai hanani yiwa mijina biyayya kishin da zaisani yin shirka kishin da zai hanani haduwa da Allah salin alin Ina roqon Allah indai yayoni a wannan sahun to ya qaddaramin mutuwa kafin nayi aure don bana fatan na zamewa mijina fitina masifa Kuma bala'in rayuwarsa"
Tsaki Ni'imah takanyi tace “ai saikiyi banza mara sanin ciwon Kai yo akanme zanyi addu'a Allah ya ragemin kishi bayan kishin adone ga ya mace nifa ko akan kishi da Yusrah ma bugawa zamuyi me qarfi ya kwaci kansa Kuma wlh don na kashe kishiya bazan taba nadama don nasan itama ba Sona takeyi ba da zata samu dama zata iya kasheni to da ka bari a kasheka gara Kai ka fara kashewa"
Yanayin Rafi'ah bata musu balle jayayya hakan yakansa da taja taga Ni'imah ta kafe akan ra'ayinta saita qyaleta abinda ta dauka wani abin halitta ce baka Isa canxa mutum ba haka watanni sukayita turawa tafi na tafiya har shekaru saura wata bakwai candynsu akasa auren Rafi'ah da Yassar murna gurinsu baa cewa komai Yassar kusan yanayinsu daya da Rafi'ah shima sanyine dashi yana nuna Mata madarar qauna me mantar da zuciya damuwa kullum suna tare babu abinda yake rabasu su uku sai bacci wani lkcn suna zaune sai kawai Ni'imah ta Kama kuka idan suka tambayeta sai tace tana tunanin ranar da Bestienta zata tafi ta barta ta kwana ta yini bata ganta ba, itama Rafi'ah saita Kama kuka abinka da quruciya tasha samun Yassar ita dashi ta roqeshi ya auresu su biyu yakanyi dariya yace.
“Bakida hankali yarinya ni ba mijin mace biyu bane Kuma ko zan qara aure Ni'imah batayimin ba banason farar mace sannan ta cika son jiki da rakin masifa ke nifah har tausayin mijinta nakeyi" akan haka Wai yana kushe Bestienta akwai lkcn da Saida sukayi sati uku basa mgn har saida manya suka shiga abin saboda ita Rafi'ah tata matsalar kafiyar masifa indai aka sake ta furta abu to komai wuyarsa sai tayi shiyasa iyayenta suke takatsantsan da furucinta dama Hausawa sunce muskilin mutum wuyar sha'ani gareshi shiyasa yawa yawan mutane suke cewa ta fiye jin izza kamar wata yar sarki wasu suce don tana dakyaune take wulaqanta mutane.