← Book details Mazan Ko Matan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 96

Sashe 13

Mazan Ko Matan Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Sai wajajen shidda saura suka suka shigo gidan da gudu daga Aman har Amal sukazo suka rungume kakansu abinci Ummi takawo, tama Hajiya unripe plantain porridge datasa shuwaka da bushashen kifi da daddawa aciki shima ba maggi ba gishiri sai kamshi daddawa da kifi sun bama abincin taste, tayi jellof rice da naman rago ma sauran mutane, duk suka baje harda Nura za’aci abinci anan falo, Ummi takoma gefe ta duka Hajiya tace “kema taho nan kici, an taba haka ki mana girki saiki koma gefe, tahonan” dan satan kallon Nura tayi shi harya faracin faten Hajiya ma, da idanu yamata tazo nan, hakanan taje tashiga cikinsu suka faracin abinci, ita da Ameena da su Aman shinkafa sukeci, tunda tafara aiki yaune rana na farko data ji kaman tana gidansu Hajiya ne Gwaggon ta Amina kuma yan uwanta, sai hayaniya su Amal keyi anacin abinci, no wonder Alhaji keda kirki mahaifiyar shi batada matsala at all. Nura yace “Hajiya dan ban juice din cucumber dinki nasha” jug din Hajiya ta kalla tace “kai Nura na tsammaka na tsammaka harna gaji da sammaka wai kaine mara lafiyan nan ne”? Dariya akayi Ummi itama dan boye dariya ta tayi ganin yanda Hajiya keda barkwanci, takalli Nura tace “inje inmaka kaima Alhaji”? Batare daya kalleta ba yace “a’a kihuta zansha na Hajiya” kofi Hajiya ta dauka ta tsiyaya mai rabi ya karbe ita ta shanye rabin tace “Allah miki albarka Ummi zaki koyama wannan shashashan Autan nawa kafin mu koma” gyadama Hajiya kai tayi, Hajiya tace “Auta dukta cinye ke bakici komiba” dasauri Ummi tace “naci sosai wlh” kashigo falon ji zakayi inama haka farin ciki zai dawwama agidan, Nura yana lura da yanda bini bini Ummi kecin abincin tana duba Amal da Aman, chan kuma saita debo tai feeding Amal da mostly wasa take da abincin at this point bazaiyi karyaba yarinyar ta shiga ranshi sosai barinma dayaji labarinta dazu, yaji ta taba aure har ta haihu dudda pre matured birth tayi amma saiyaji yakara natsuwa da ita, wato saisa takeson yaranshi kuma saisa takeda hankali koba komi tanada experience, baison yayi mu’amala da yara masu danyan kai that knows nothing akan aure koba komi tasan menene aure kuma tayi zaman aure, tayi rainon ciki, sannan tayi nakuda, hakan is perfect for him.
Sake lura da yanda yake satan kallonta Hajiya tayi daidai nan aka bude kofa aka shigo dukansu suka dago kai cikeda fara’a Hajiya tace “oyoyo oyoyoo, sannu da dawowa Hadiza” tundaga inda Hadiza ke tsaye tabi kowa na falon da kallo da yanda falon yayi kacha kacha dudda bawai kacha kachan yayi ba kayansu ne jaka da gyaluluwa dasuka zuba akan kujera dan dawowansu kenan Ummi ta taresu da abinci sai abincin da Amal da zuzzubar a falon rice din, daidai nan idanunta yasauka akan Ummi dake cin abinci tareda Amina dakuma yaranta akasa tana kokarin bama Amal abinci abaki hankalinta kwance dan akasa take zaune technically batayi laifi ba yau. “Ke menene aikinki? Jibi yanda gidana yayi kacha kacha zama kikayi kinacin abinci? Kina yar aiki waya gayamiki kinada darajan zama inda mijina yake kici abinci eh”? Yunkurawa Ummi tayi jikinta yayi sanyi zata tashi dasauri Hajiya tace “dakata Ummi” takalli Hadiza dake tsaye awajen da taje tace “ninace taci abinc……” “Hajiya dan Allah kidakata badake nake magana ba” Hadiza tayi maganan rai abace dasauri daga Nura har Ameena suka juyo suka kalleta da mugun mamaki itama Hajiya tayi tsuri tana kallonta dan batasan haka Hadiza tazama tasan ta dai da rashin son aiki ko sunzo babban salla Kano dama ba zama take agidanta ba saidai ta gudu gidansu so bata wani zauna da Hadiza one on one na dogon lokaci ba, ganin abun zai zama wani kala yasa dasauri Ummi ta tashi zata juya strictly Nura yace “dawo ki zauna kicigaba da cin abincin ki” cikeda tsoro Ummi takalli Nura gabanta na faduwa tadan kalli Hadiza dake kallonta rai abace ahankali takoma ta zauna abun ya mugun mugun yima Hadiza ciwo dan yaune rana na farko daya nuna bata isaba agaban yar aikin yawanci ba agaban idanunta suke tsiyansu ba, zuciyanta wani kalan baki yayi takalli Nura tace “muzuba nidakai badai anzo har cikin gidana ana nema ajuyamaka kai ba tun yanzu an fara kulla kisisina da shairi ko da sunan rashin lafiya amman bakin mutum rass yazauna yana zakalkalan abinci to wlh muzuba dani dakai” Ameena jitayi kirjinta na tafarfasa badan Ya Nura na zaune wajen ba da wlh saita durama Hadiza ashar wucewa tayi fuuuu tayi sama kunyan duniya rufe Nura yayi abinda matarshi tama Hajiya jiyayi ma abincin ya isheshi kowama hatta yaran jisukayi abincin ya ishesu Hajiya ta kalli Ameena tace “tashi keda Ummi ku gyara wurin” kunya yasa Nura yamike yama kasa kallon kwayan idanun Hajiya yajuya yace “bari nazo Hajiya” baima jira amsanta ba yafice dasauri Hajiya tabishi da kallo saitaji dan nata yabata tausayi.
Kayan daya sayo dazu yasa mai gadi ya kwashe yakaima Ummi sannan yaja mota yabar gidan.
Chapter 13 · 0% Book details