Sashe 5
Kukan Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lafiya kalau Kanol ya kwanta bayan yasha magungunan sa, amma cikin dare wani azababban ciwon ciki ya turnike sa sai murkusu yake tun yana iya daurewa harya tashi Ummi dake barci, ganin halin dayake ciki gaba ɗaya hankalinta yatashi ta gigice tama kasa basa taimako, Fahad taiwa waya sukazo shida Jabir suka garzaya asibiti, Su'ad da Mami basusan Kanol ba lafiya ba saida safe sukaje asibitin, lokacin yaɗanji sauki ba kamar sanda aka kawo saba, Su'ad na rikeda hannun Daddynta tunda suka shugo take hawaye shidai Kanol kallonta kawai yake yana girgiza mata kai alamar tai shuru, "Yi shuru Autata daina kukan haka nafa ji sauki Fahad yana shugowa zance ya sallamemu mu koma gida ko haka kike so" kai kurum Su'ad ta girgiza masa, shafa kanta yayi yana faɗin Allah yai maku albarka ya albarkace ku gaba ɗaya" shugowar Fahad yasa Kanol cewa "Yauwa maida Auta gida zamuyi magana da su Mami kici abinci ki wanka anjima saiki dawo ki tahomin da fatan dankali" kai Su'ad tasake gyaɗawa haka kurum takejin jikinta duk ba daɗi, jiki a sanyaye tamike zata futa, ta juyo tana kallon Kanol daya rike hannun Fahad duk da bata jiyo abinda Daddyn yake faɗa haka kurum take zaton maganarta yakewa Uncle ɗin"Ga amanar Su'ad nan na damka a hannunka itace karama kabata kulawa kabata duk wani farin ciki na rayuwa kada kabari ta koka ko bayan raina" Fahad yace "Insha Allah Daddy zanyi abinda kake so Allah yabaka lafiya" Ameen ya furta saman laɓɓansa kana muka fita daga ɗakin,
Kanol ya kalli Mami yana murmushi "Kuyi hakuri banjin wannan ciwon nawa na tashi ne! kuyafemin ga amanar yarana nan na damka a hannunku kuci gaba da basu ingartacciyar tarbiya kamar wacce muke basu ina raye, dan Allah kada kubari wani ruɗe na duniya yasa ku raba kanku kuci gaba da haɗe kanku kamar yanda kuke ayanzu, sannan Su'ad na bawa Fahad ya aureta ko bayan raina kuka canza ban yafe ba! da sauri Mami ta kalli Kanol "Abban Su'ad yazakace haka su yaran sukace maka suna son junansu shakuwa ce kawai fa a tsakaninsu ba soyayya, inma shi Fahad sonta yake to ita Su'ad tanada wanda ta..."Umarni na bayar lallene acikan burina ko bayan raina! "Kanol dan Allah kayi shuru cuta fa ba mutuwa bace, kabari inkaji sauki saimu tattauna" murmushi kawai yayi yana kallon Ummi data kasa magana hawaye kawai take, Kanol ya lumshe idanu yana faɗin "La'ilaha illallah muhammadan rasulillah" azabure Ummi ta ɗago tana kallonsa ganin yanda hannunsa dake cikin nata yasaki, wata kara tasaki haɗeda salati itama nan ta zube, dai dai shugowar Fahad daya dawo daga gida dan ganin yaya jikin Daddyn turus yayi ya tsaya bakin kofar ɗakin yama kasa shugowa, Mami ke salati tana girgiza Ummi datake zaton itama mutuwar tayi, "Fahad ka tsaya anan karaso ciki ka bata taimakon gaggawa Daddy yau Allah ya amshi abinsa, hasbinallahu wani'imal wakil" azabure fahad yashugo ɗakin yasoma tattaɓa Daddyn saida ya tabbata rai yayi halinsa kana yasa Mami ta ɗora Ummi saman gadon dake kusa dana Daddy yasoma bata taimakon gaggawa, a firgice ta farka dai dai shugowar Fatima da sai sannan taji Daddy bayada lafiya, ganin mutum lulluɓe da farin yadi yasa Fatiman ta buɗe yanayin dataga Daddy yatabbatar mata baya lumfashi luuu tayi baya zata faɗi mijinta ya rukota ta faɗa jikinsa tana fashewa da kuka, Fahad da kwamishina su suka jajirce kan gawar Kanol aka gama haɗasa suka ɗaukesa zuwa gida dan masa sallah akaisa makwancinmu na gaskiyya😰
*Su'ad*
Sauri sauri nake na kammala fatan dankalin da Daddy yace nayi masa ko wanka banyi ba haka kurum duk nakejin jikina yai wani irin sanyi, na zuba dankalin kenan naji wata faɗuwar gaba tareda kara haɗida salati kamar muryar Yaya Shareef nakeji shiyasa na futo daga kicin ɗin da sauri kamar zan faɗi na nufi compound na gidan inda nake jiyo hayaniya, nima salati na saki ina kamewa awaje ɗaya saboda abinda idanuna suka ganemin, wata irin girgiza nayi sai gani gaban motar na rirrike Uncle Fahad ina kuka kamar raina zai futa, Rukoni yayi sosai yana goge hawayan fuskarsa yama kasa cewa komai, hannuna yaja muka shuge cikin gidan ɗakinsa yakaini ya zaunar dani gefan gado shima ya zauna har sannan hawaye ke zuba daga cikin idanunsa yabuɗe baki zaiyi magana kawai yafashe da kuka, sosai yake kuka yanda yake kukan zakasan mutuwar ta taɓa masa zuciya, cikin kuka yake lallashina "Muyi hakuri! bamuda yanda zamuyi inama wani yana fansar wani dana mutu Daddy ya rayu, tabbas munyi babban rashi Su'ad dabazamu samu madadinsa ba" mikewa yayi ganin yanda na haɗe jikina waje ɗaya ina kuka dukkan ilahirin jikina karkarwa yake allura yake shirin yimin na ɗago ina kallonsa "Uncle mai zakamin allurar barci please dan Allah karkamin kabarni naga Daddy na nai masa kallon karshe nai masa addu'a", ajje alluran yayi muka futa falo tuni mutane sun fara taruwa, kasancewar juma'a ce ana idar da sallah a masallacin unguwarmu aka sallaci gawar Daddy munaji muna gani badan ranmu naso ba aka kai Daddy makoncinsa, mutuwar Daddy gaba ɗaya ta canzar rayuwata nazama wata slent sam ba rigimar nan dana saba bana komai sai karatun kur'ani dan tuni Mami ta takamin burki da yawan kukan danake, tace ba abinda zai amfanarwa Daddy saima azaba da zanja masa, Fu'ad yazo tun randa akayi matuwar dashi aka sallaci Daddy, yan uwansa ma sunzo sosai harda Umma da mai martaba, Abbi ɗinsa ne baya nan a waya yamin ta'aziya nai mamaki sosai yanda yan uwansa suka san dani, hatta babbar y'ar mai martaba Hidaya wacce ke auran sarkin garinmu saida tazo mana gaisuwa.
Rasuwar Daddy ta canza rayuwar jama'ar gidanmu baki É—aya kowa yazama ustaz sai ahankali muka saba da rashin Daddy tuni kowa ya koma bakin aikinsa, yaya sharif ya koma kaduna inda yake aiki domin shima soja ne sai yaya Jabeer dake aikin banki nida Yazeed mun koma makaranta ni ina shekara ta biyu shi kuma yana shekarar karshe, duk fanni É—aya muke karanta low.
Watan Daddy ɗaya da wani yammaci ina zaune falo na biyu wata mata tayi sallama ta shugo duka shekarunta bazasu wuce ashirin da biyar ba yanda take wani kalle kalle yasa nima nake kallonta kamar na santa amma na manta inda na santa, ta zauna saman kujera kamar bataso tacemin "Hajiya Amina tana nan kuwa?" kamar nace mata bata nan ganin tambayar rainin hankalin dataimin mutanan dake takaba ina zasu futa wata unguwa, bance mata komaiba na mike na shuga ciki danna kira Mami, tare muka futo da Mami da Ummi jin danai Mami tace "A lale da zuwa Zainaba daman kece?" ɗan shuru tayi kana ta gaida su mamin, jin danai ance Zainaba yasa na gane inda nasanta matar Uncle Fahad ce wacce suka rabu dashi shekaru biyar kenan, Ummi ke tambayar ina "Ameera yammata yanzu nasan ai ta girma" bata bawa Ummi amsaba sai dariya da tayi kawai tana nan har Uncle Fahad da yaya Jabeer suka dawo, ko zama Uncle baiyi ba bayan sun gaisa tai masa gaisuwa ya wuce ɗakinsa, bin bayan sa nayi yana tsaye cikin ɗaki harya fara rage kayan jikinsa yarage daga shi sai dogon wandon shadda sai farar singileti yana kokarin cire dogon wandon ni kuma nayi sallama na shuga kai tsaye, jin sallamata yasa ya juyo yana kallona yaɗan ɓata rai yana cewa "Banace ki daina shugomin ɗaki kai tsaye haka ba, kina fara neman izini tukunna" nidai bance masa komaiba na zauna gefan gado ina cewa "Uncle wai maiyasa bazaka maida Zainaba ɗakintaba kodan Ameera ma dake tsakaninku" ɓata rai yayi yana kallona ya ce "Kintaɓa ganin inda mutum yazauna da makiyinsa" turo baki gaba nayi ina cewa "Tayaya masoyi zai koma makiyi baka sonta daman ka aureta harda yara" zama yayi nesa dani kaɗan yadafe kansa yana magana.
"Bantaɓa son Zainaba ba, Mahaifinta wan mahaifi nane shiya ɗauramin aure da ita nazauna da'ita zaman amana, duk da inada wacce zuciyata keso tun tana jaririya amma haka na danne son na zauna da Zainaba da zuciya ɗaya, ashe itada mahaifinta suna da wata manufa akaina, mun haifi yaranmu guda biyu Abdallah shine babba sai mariya damuke kira da Ameera saboda sunan mahaifiyata dataci! acan baya bayan matuwar mahaifina yayan babanmu ya auri innarmu ashe shi da biyu ya aureta saboda ya kwace duk dukiyar da Abbanmu yabar mana nida Mami, Innarmu ta gano haka saita gudu garinsu ta damkawa mahaifinta duk kanin takardun kadarorinmu sannan ta dawo gane ba komai a wajanta da baba yayi yasa ya rinka wulakanta ta har Allah ya amshi ranta!😰 bayan rasuwarta kakanmu yabamu duk wasu takardunmu Mami ta adana mana, wata rana bayan aurena da Zainaba na dawo daga hospital ranar agajiye na dawo gajiya tasa bana kojin yunwa, ina zama takawomin abinci nace mata banajin yunwa ta ajjiye sai zuwa anjima zanci, bata ɗauke abincinba ta shuga ɗakinta, dai dai sannan Ameera da Abdallah suka dawo daga school, Abdul daman bayada juriyar yunwa yaro ɗan shekara goma jakarsa kawai ya ajje yacemin Uncle Abinci zanci nazuba masa abincin da Zainaba ta kawomin lomarsa uku yafara dafe ciki yana murkususu kafin wani lokaci kumfa tafara futa daga bakinsa ihun yaron yasa Zainaba futowa daga ɗaki ganin halinda Abdallah ke ciki yasa ta kwala ihu tana kallona Fahad abincin dana kawo maka kabasa banbi ta kanta ba na ɗauki Abdul da abincin zuwa Asibitinmu kafin najema rai yayi halinsa Abdul ya rasu😰na bincika abincin saina gano guba a ka saka, bayan ankai Abdul gidanmu na gaskiyya na tsare Zainaba da tambaya anan take gayamin Babanta be yakawo guba yace tazubamin a abinci naci na mutu dansu gaje duk dukiyar da Abbanmu yabar min ni kuma jin haka yasa na saketa saki uku kar naje wataran cikin dare da burma min wuka ta kasheni" Shuru nayi kawai ina bin Uncle da kallo tabbas nasan lokacin da Abdul ya rasu amma banzance ga dalilin rasuwarsa ba" jiki sanyaye na bar ɗakin nasa na koma nawa ɗakin na kwanta lamo ina tunanin lamarin duniyar nan
Kanol ya kalli Mami yana murmushi "Kuyi hakuri banjin wannan ciwon nawa na tashi ne! kuyafemin ga amanar yarana nan na damka a hannunku kuci gaba da basu ingartacciyar tarbiya kamar wacce muke basu ina raye, dan Allah kada kubari wani ruɗe na duniya yasa ku raba kanku kuci gaba da haɗe kanku kamar yanda kuke ayanzu, sannan Su'ad na bawa Fahad ya aureta ko bayan raina kuka canza ban yafe ba! da sauri Mami ta kalli Kanol "Abban Su'ad yazakace haka su yaran sukace maka suna son junansu shakuwa ce kawai fa a tsakaninsu ba soyayya, inma shi Fahad sonta yake to ita Su'ad tanada wanda ta..."Umarni na bayar lallene acikan burina ko bayan raina! "Kanol dan Allah kayi shuru cuta fa ba mutuwa bace, kabari inkaji sauki saimu tattauna" murmushi kawai yayi yana kallon Ummi data kasa magana hawaye kawai take, Kanol ya lumshe idanu yana faɗin "La'ilaha illallah muhammadan rasulillah" azabure Ummi ta ɗago tana kallonsa ganin yanda hannunsa dake cikin nata yasaki, wata kara tasaki haɗeda salati itama nan ta zube, dai dai shugowar Fahad daya dawo daga gida dan ganin yaya jikin Daddyn turus yayi ya tsaya bakin kofar ɗakin yama kasa shugowa, Mami ke salati tana girgiza Ummi datake zaton itama mutuwar tayi, "Fahad ka tsaya anan karaso ciki ka bata taimakon gaggawa Daddy yau Allah ya amshi abinsa, hasbinallahu wani'imal wakil" azabure fahad yashugo ɗakin yasoma tattaɓa Daddyn saida ya tabbata rai yayi halinsa kana yasa Mami ta ɗora Ummi saman gadon dake kusa dana Daddy yasoma bata taimakon gaggawa, a firgice ta farka dai dai shugowar Fatima da sai sannan taji Daddy bayada lafiya, ganin mutum lulluɓe da farin yadi yasa Fatiman ta buɗe yanayin dataga Daddy yatabbatar mata baya lumfashi luuu tayi baya zata faɗi mijinta ya rukota ta faɗa jikinsa tana fashewa da kuka, Fahad da kwamishina su suka jajirce kan gawar Kanol aka gama haɗasa suka ɗaukesa zuwa gida dan masa sallah akaisa makwancinmu na gaskiyya😰
*Su'ad*
Sauri sauri nake na kammala fatan dankalin da Daddy yace nayi masa ko wanka banyi ba haka kurum duk nakejin jikina yai wani irin sanyi, na zuba dankalin kenan naji wata faɗuwar gaba tareda kara haɗida salati kamar muryar Yaya Shareef nakeji shiyasa na futo daga kicin ɗin da sauri kamar zan faɗi na nufi compound na gidan inda nake jiyo hayaniya, nima salati na saki ina kamewa awaje ɗaya saboda abinda idanuna suka ganemin, wata irin girgiza nayi sai gani gaban motar na rirrike Uncle Fahad ina kuka kamar raina zai futa, Rukoni yayi sosai yana goge hawayan fuskarsa yama kasa cewa komai, hannuna yaja muka shuge cikin gidan ɗakinsa yakaini ya zaunar dani gefan gado shima ya zauna har sannan hawaye ke zuba daga cikin idanunsa yabuɗe baki zaiyi magana kawai yafashe da kuka, sosai yake kuka yanda yake kukan zakasan mutuwar ta taɓa masa zuciya, cikin kuka yake lallashina "Muyi hakuri! bamuda yanda zamuyi inama wani yana fansar wani dana mutu Daddy ya rayu, tabbas munyi babban rashi Su'ad dabazamu samu madadinsa ba" mikewa yayi ganin yanda na haɗe jikina waje ɗaya ina kuka dukkan ilahirin jikina karkarwa yake allura yake shirin yimin na ɗago ina kallonsa "Uncle mai zakamin allurar barci please dan Allah karkamin kabarni naga Daddy na nai masa kallon karshe nai masa addu'a", ajje alluran yayi muka futa falo tuni mutane sun fara taruwa, kasancewar juma'a ce ana idar da sallah a masallacin unguwarmu aka sallaci gawar Daddy munaji muna gani badan ranmu naso ba aka kai Daddy makoncinsa, mutuwar Daddy gaba ɗaya ta canzar rayuwata nazama wata slent sam ba rigimar nan dana saba bana komai sai karatun kur'ani dan tuni Mami ta takamin burki da yawan kukan danake, tace ba abinda zai amfanarwa Daddy saima azaba da zanja masa, Fu'ad yazo tun randa akayi matuwar dashi aka sallaci Daddy, yan uwansa ma sunzo sosai harda Umma da mai martaba, Abbi ɗinsa ne baya nan a waya yamin ta'aziya nai mamaki sosai yanda yan uwansa suka san dani, hatta babbar y'ar mai martaba Hidaya wacce ke auran sarkin garinmu saida tazo mana gaisuwa.
Rasuwar Daddy ta canza rayuwar jama'ar gidanmu baki É—aya kowa yazama ustaz sai ahankali muka saba da rashin Daddy tuni kowa ya koma bakin aikinsa, yaya sharif ya koma kaduna inda yake aiki domin shima soja ne sai yaya Jabeer dake aikin banki nida Yazeed mun koma makaranta ni ina shekara ta biyu shi kuma yana shekarar karshe, duk fanni É—aya muke karanta low.
Watan Daddy ɗaya da wani yammaci ina zaune falo na biyu wata mata tayi sallama ta shugo duka shekarunta bazasu wuce ashirin da biyar ba yanda take wani kalle kalle yasa nima nake kallonta kamar na santa amma na manta inda na santa, ta zauna saman kujera kamar bataso tacemin "Hajiya Amina tana nan kuwa?" kamar nace mata bata nan ganin tambayar rainin hankalin dataimin mutanan dake takaba ina zasu futa wata unguwa, bance mata komaiba na mike na shuga ciki danna kira Mami, tare muka futo da Mami da Ummi jin danai Mami tace "A lale da zuwa Zainaba daman kece?" ɗan shuru tayi kana ta gaida su mamin, jin danai ance Zainaba yasa na gane inda nasanta matar Uncle Fahad ce wacce suka rabu dashi shekaru biyar kenan, Ummi ke tambayar ina "Ameera yammata yanzu nasan ai ta girma" bata bawa Ummi amsaba sai dariya da tayi kawai tana nan har Uncle Fahad da yaya Jabeer suka dawo, ko zama Uncle baiyi ba bayan sun gaisa tai masa gaisuwa ya wuce ɗakinsa, bin bayan sa nayi yana tsaye cikin ɗaki harya fara rage kayan jikinsa yarage daga shi sai dogon wandon shadda sai farar singileti yana kokarin cire dogon wandon ni kuma nayi sallama na shuga kai tsaye, jin sallamata yasa ya juyo yana kallona yaɗan ɓata rai yana cewa "Banace ki daina shugomin ɗaki kai tsaye haka ba, kina fara neman izini tukunna" nidai bance masa komaiba na zauna gefan gado ina cewa "Uncle wai maiyasa bazaka maida Zainaba ɗakintaba kodan Ameera ma dake tsakaninku" ɓata rai yayi yana kallona ya ce "Kintaɓa ganin inda mutum yazauna da makiyinsa" turo baki gaba nayi ina cewa "Tayaya masoyi zai koma makiyi baka sonta daman ka aureta harda yara" zama yayi nesa dani kaɗan yadafe kansa yana magana.
"Bantaɓa son Zainaba ba, Mahaifinta wan mahaifi nane shiya ɗauramin aure da ita nazauna da'ita zaman amana, duk da inada wacce zuciyata keso tun tana jaririya amma haka na danne son na zauna da Zainaba da zuciya ɗaya, ashe itada mahaifinta suna da wata manufa akaina, mun haifi yaranmu guda biyu Abdallah shine babba sai mariya damuke kira da Ameera saboda sunan mahaifiyata dataci! acan baya bayan matuwar mahaifina yayan babanmu ya auri innarmu ashe shi da biyu ya aureta saboda ya kwace duk dukiyar da Abbanmu yabar mana nida Mami, Innarmu ta gano haka saita gudu garinsu ta damkawa mahaifinta duk kanin takardun kadarorinmu sannan ta dawo gane ba komai a wajanta da baba yayi yasa ya rinka wulakanta ta har Allah ya amshi ranta!😰 bayan rasuwarta kakanmu yabamu duk wasu takardunmu Mami ta adana mana, wata rana bayan aurena da Zainaba na dawo daga hospital ranar agajiye na dawo gajiya tasa bana kojin yunwa, ina zama takawomin abinci nace mata banajin yunwa ta ajjiye sai zuwa anjima zanci, bata ɗauke abincinba ta shuga ɗakinta, dai dai sannan Ameera da Abdallah suka dawo daga school, Abdul daman bayada juriyar yunwa yaro ɗan shekara goma jakarsa kawai ya ajje yacemin Uncle Abinci zanci nazuba masa abincin da Zainaba ta kawomin lomarsa uku yafara dafe ciki yana murkususu kafin wani lokaci kumfa tafara futa daga bakinsa ihun yaron yasa Zainaba futowa daga ɗaki ganin halinda Abdallah ke ciki yasa ta kwala ihu tana kallona Fahad abincin dana kawo maka kabasa banbi ta kanta ba na ɗauki Abdul da abincin zuwa Asibitinmu kafin najema rai yayi halinsa Abdul ya rasu😰na bincika abincin saina gano guba a ka saka, bayan ankai Abdul gidanmu na gaskiyya na tsare Zainaba da tambaya anan take gayamin Babanta be yakawo guba yace tazubamin a abinci naci na mutu dansu gaje duk dukiyar da Abbanmu yabar min ni kuma jin haka yasa na saketa saki uku kar naje wataran cikin dare da burma min wuka ta kasheni" Shuru nayi kawai ina bin Uncle da kallo tabbas nasan lokacin da Abdul ya rasu amma banzance ga dalilin rasuwarsa ba" jiki sanyaye na bar ɗakin nasa na koma nawa ɗakin na kwanta lamo ina tunanin lamarin duniyar nan