← Book details In Bani Book 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 69

Sashe 62

In Bani Book 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wuraren biyar da rabi suka gama komi tsaf suka fiffito har haraban asibitin Aadil da Baba Suleman suka shiga gaban mota itakuma da big Mum suna baya, Baba Suleman ya kunna motar yaja suka shiga hanya yace "i can't wait to see yanda su Mami da Aabid zasuyi idan suka ganmu" dan dagokai Hamida tayi ta side glass ta kalli fuskar Aadil taga idanunshi a lumshe suke kaman mai bacci, kuka ne sosai taji yazo mata, she's so longing for his talk, so kawai take yamata magana amma ya share ta, da kyar ta daure ta hana kanta kukan dan bamata da karfin yin kukan tanata kallon garin dasuke dan daga gani tasan ba Nigeria bane dan larabawa take ta gani tako ina, tafiyan kusan 20min sukayi taga Baba Suleman yay parking agaban wani babban gida yace "muna shiga da mota zasu gane kuzo muje" fitowa yayi hakan yasa Aadil yabude kofa shima yafito yakosa yaga Mami da dan uwanshi, big Mum ma tafito ta taimakama Hamida itama tafito, Baba Suleman yabude gate suka shiga har gaban babban flat dinsu Baba, Suleman ne yajuyo yana zare ido hadaura yatsarahi akan lips dinshi ya kallesu, hanun Aadil yakama ya daura akan na Hamida da sauri Aadil ya yatsine fuska tareda janye hanunshi da sauri yana kallon Baba Suleman irin me haka, ahankali Hamida ta kallai yanda yake yatsine fuska, cikin rage murya batare da yalura damai yafaru ba Baba Suleman yace "kariketa karta fadi kaga batada karfi nida Aisha ne zamu fara shiga ciki kafin ku kubiyomu abaya" yay maganan yana kara daura hanun Aadil akan na Hamida ahankali Hamida ta saukar da kanta kasa dan tana gabda sakin kuka, Baba Suleman da Big Mum suka juya suka bude kofa suka shiga ciki atare, wani irin gajeren wahalallen tsaki Aadil yaja ya saki hanunta da sauri hakan yasa tai baya zata fadi atsorace taidan kara tadafe bango ahankali tana maida ajiyan zuciya, ko kallonta baiyiba yasa hannu yabude kofa ya shiga dakin idanunshi suka hadu dana Mami da Aabid yadebo rice a spoon yana kokarin kaimata baki danko kadan bata iyacin abinci sai an tursasata tarame sosai bana wasaba, Baba Suleman da Big
Mum tsaye agefe suna murmushi sosai suna kallonsu sunyi folding hand akirji, atare Mami da Aabid suka mike tsaye suna kallon Aadil din, wani irin cute adorable smile Aadil yayi yace "Mami na" ya kalli Aabid yace "rascal" sakin plate din abincin Aabid yayi akasa jikinshi yadau wani irin rawa bakinshi har rawa yake yana kallon Aadil din yace "d...Dil"
Durkushewa Mami tayi tana kuka kuka kaman zata mutu ganin yanda gini ya ruguzo kan Abie, Baffa duk shine mai dan kwari a cikinsu ya kalli su Suleman da muryanshi data dishashe yace "ku wuce kukai yaran nan asibiti we will take care of the rest anan" juyawa duk sukayi Aabid da kyar ya iya daga kafarshi yay hanyar gate dan motarshi na waje har wani jiri jiri yake gani, bude motar yayi ya kwantar da ita abaya yamaida kofar yarufe ya shiga gaba ya tada motar, su suleman ma suka shiga tasu motar bayan sun kwantar da Aadil abaya sukaja motar sukabar anguwan sukai wani babban private hospital dasu inda da gudu Nurses and Dr suka karbesu sukai placing dinsu on admission, Baba Suleman ne yace "VIP room mukeso asasu" nan aka kwantar dasu awani hadadden daki mai gado biyu Dr suka taru akansu ana kokarin saving their lives, ahankali Aabid yatashi daga jikin kofan inda yake leka yanda Dr's ke battling suna kokarin cetosu ya zauna akan one of the kujera dake corridor da dakinsu yake ya saukar da kanshi kasa yadafe kanshi zuciyarshi na bugawa yanamai zafi, yanamai daci sanan yanamai yaji, for the first time a history din life dinshi yaji ya tsani life dinshi, ya tsani his life he hates who he is, yanzu dama cikin kudin jini Abie ya rainesu?

Yasasu makaranta har ya karanci business administration, da blood money ya rayu daman?

Thank God yanada aikin kanshi, yanada kampanin kanshi dayay establishing bayan yagama masters dinshi but dudda hakan d thought of yarasu yaci yasha yay karatu da blood money yakasa fita daga ranshi.

"Astagafurullah" yafada sounding weak, he promised kanshi daidai da riga daya tak wanda Abie yasaimai shida Brother shi saiya cire ya kona ya zubar, komi na Abie daya saima shida Aadil saiya kona tass.

Dafashi da akayi yasa ya dago kanshi da kyar idanunshi sunyi jajir, Baba Suleman ne ya zauna kusa dashi yana kallonshi cikeda tausayawa yasan this is hard dole abin ya daki zuciyar Aabid da karfi.

Murya chan kasa mai cike da calmness nason kwantar ma da yaro hankali yace "let it out Boy, let it out Hussain, Men cry too, am here for you, am here for you kaji" fadawa jikin Baba Suleman Aadil yayi yace "Uncle m...my....my father is is a ri...ritualist, he did all this thing to my brother, Uncle Abie, he feed us da bloodmoney, he cloth us da blood money, he did everything mana da kudin jini, Abie killed and ruin my brother's 30yrs of life, Abie yakashe mini kannai n...." zaiyi magana Baba Suleman ya taushemai baki yana sharemai hawayen daya dake zuba nonstop yace "is okay, is okay Aabid, kaddara ce haka Allah yariga ya tsara rayuwan dan uwanka Aadil, ahaka Allah yariga yarubuta zaiyi shekaru talatin a duniya batare da yasan waye shiba, koda Abie baiyi komiba one way or the other saikaga something happen dazaisa yay rayuwanshi ahaka, now lets all hope for the best, muyi creating new beginning and new memories and let's all forget d past okay, think of your Mum and think abinda take going through yanzu haka, wahala da dawainiyan Aadil tun yana jariri datasha kullum suna hanyan asibiti, sanan ga barin ciki har sau uku yaya kake tunanin takeji yanzu datasan dalilin?

Ga kuma dan uwanka a asibiti shida matarshi yaya kake tunani takeji?

Let's pray murokan ma Abie gafara daga Allah kaddara ce, dama annabi yafada aciki hadisi cewa kowace alumma nada fitinarta yace fitinar alumma ta itace dokiya, kaga arayuwan nan wasu mutane can do anything for money, inhar dai zasu sami kudi they can do anything, arayuwar nan tamu tayau mutum ya kasance mai godiyan Allah, d little da Allah yabaka ka godemai and be contented saikaga Allah will give you more masu albarka, one shouldn't be greedy da mugun son kudi, greediness dason banza can lead you to astray daga hakane zaka fara karban cin hanci which annabi yay hani akai yafadi ahadisi akan Allah ya tsinema mai bayar da cin hanci damai karba, yawan son kudi ma da mutane keso fitina ne, kudi kayane aka dan ranan gobe kiyama saikama Allah bayani akan each and every single kobo daka kashe, how?

Tayaya ka kashe su ta hanya mai kyau ce kota hanyar sabon Allah ne sanan tayaya ka samesu ta hanyar halal ce, ta guminka ne kota hanyar haram, duksai kafadi ma Allah, saisa yakamata kowa kowani musulmi ya yawaita yin addu'a Ya Allah kabani dukiya ta halas, Ya Allah ka sanyama dukiyar Albarka sanan Ya Allah kasa na kashe su ta hanya mai kyau bata hanyar saboba, Allah yasa mudace kawai Aabid, Allah kuma yasa karshen mu tai kyau, Allah kuma ya kashemu muna musulmai sanan Allah ya ganar da dukkan musulmai dakeson kawai suyi kudi kota yayane kotahalin k'ak'a ne, sanan Ya Allah ya shiryi musulmai masu hali irin na Abie wayanda are willing to sacrifice koda mahaifiyar suce dandai kawai suyi kudi su sami abin duniya, wayanda zasu iya zuwa su sadu da gawa dan samin abin duniya, su sami kudi su sami na nunama jama'a ace wai wanan fa babba ne Alhaji ne motoci guda dari gareshi baya sati a nigeria yau yana dubai gobe yana china, Allah yarabamu da dukiyar dazata halaka mu, mu koma ga Allah kawai Aadil, is high time malamai sun tashi a tunatar sukuma tsawatar, kaga shi tunatarwa yana karkato da zuciyan mumini sanan yana kara samai tsoron Allah dakuma gujema kaba'ir, Allah yasa mudace, tashi muje masallaci muyi sallan asuba daganan saimu tafi gida dan akai Abdullahi gidan gaskiya, Allah ya jikanshi ya gafartamai yasa yahuta Allah kuma ya gafartamai kurakuran shi, May Allah forgive all his short comings" ahankali Aabid yace "Ameen" ya share hot hawayen daya zubomai deep down ko Allah yasani yanason mahaifinshi danshi shaida ne akan yanda mahaifinsu ke sonsu, sune komi na Abie amma wat can he do abu daya kawai zaimai shine ya rokamai gafara, yamai addu'a sanan yabude abubuwan sadakatun jariya wanda lada zai dinga kaimai kabari, saida Baba Suleman ya dagashi sanan ya iya tashi ko kadan baida karfi fita sukayi Baba Suleman da Muhammad suka rikeshi alwala sukayi sukai salla sanan suka fito suka shiga mota koda sukakai anguwan su mutane an cika fal tako ina, cikinsu harda baban Hamida da Abban su Ra'is dudda liman da Baffa sunriga sunce babu kyau fadin mummunan halin mamaci boyewa ake, addu'a kawai za'ama Abie saisa kosu baban Hamida ba'a fada musu gaskiyan abinda yafaru ba, banda limaman nan guda uku dasu babu wanda yasan zancen, ancedai wuta ce takama shine ginin ya zubo yafado kan Abie, sanan sukace musu antafi da Hamida da Aadil asibiti sosai su Aban Hamida sukai addu'a sanan sukai musu jaje aka dauko motar daga gidi aka daga ginin aka tattaro pieces din jikin Abie aka atattare awuri daya, rayuwan fa kenan!

Saisa in this world d best thing to do shine kabi Allah koka samu kyakkyawan karshe, yau ina Abie dakeda kudi ghana masgo manya manya sama da dari na yan dollars?

Ina Abie mai kampanin mota?

Ina Abie maisa hadadden shadda dake kyalli yahau jeep yafita ina yake?

Uban dukiyan daya tara yanzu sun hanashi mutuwa?

Dukiyarshi ta taimakeshi?

Ta amfane shi?
Chapter 62 · 0% Book details