← Book details In Bani Book 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 69

Sashe 22

In Bani Book 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kiran sallan magriba dakuma wani irin zafi dataji sosai ajikinta yasa ahankali ta bude ido, da sauri takara bude idon ganin inda take iskan magrib na kadawa gari yadan soma duhu kadan dudda da haske, dan nauyin dataji dakuma hanun mutum dataji akan cikinta an rike mata ciki gam, gakuma wani irin hadadden kamshin turare datakeji yana shiga hancinta yasa ta mugun zabura tadan dago, arude tace "you" dan wlh ta manta sunanshi amma dai ta tuna fuskar mutumin nan daya kaita asibiti ranan datana Lagos tagani yana bacci kanshi awuyanta jikinshi da kafafunshi akasa close to her own danhar gogan juna suke, jikinshi zafi sosai bana wasaba yana numfashi ahankali ahankali datake jin saukarshi harta cikin wuyanta, long gashin idanunshi duksun tattare waje daya tsabagen kukan dayasha, ihu tayi ganin takasa janye kafadarta.

"wayyo Allah na" ta ture kanshi daga jikinta kaman zatai kuka, bude idanunshi yayi ahankali cikin bacci dasukai ja sosai sabida zazzabi ya daurasu akanta kirjinshi nawani irin bugawa da sauri da sauri, zaro idanun tayi danji tayi idanunshi sunmata wani iri ajiki da sauri ta ture kanshi daga kafadarta ta matsa baya da sauri tamakale a jikin bango, saura kadan kanshi dake rawa sosai ya buga kasa yatashi ya zauna zuciyarshi namai wani iri sosai yana kallonta ko kyafta ido bayayi, ahankali kaman dan yaro yace "you are awake" samin kanta tayi da gyadamai kai gabanta na faduwa sosai dan yanda yay maganan saida tajishi har kasan zuciyarta, kallonshi takeyi kaman yanda shima kemata wani irin calm cool look da lumstatsun idanunshi, ganin yanda yake yine kanshi narawa sosai kirjinta na bugawa sosai fiyeda na ranan farko ma data fara ganinshi tace "how did you follow me here?" wani irin kallonta yayi da shanyayyun eyes dinshi dayake budesu sosai, da sauri ta kawad da kanta tana murza hanunta danji tayi she's so nervous, ahankali dawata irin murya chan kasa kaman ba na normal Aadil ba yace "am hungry" da sauri ta kalleshi danjin maganan tayi har zuciyarta, tashi tayi da sauri dan wani irin tsoronshi ne taji ya dirar mata arai da sauri tazo zata wuce shi hakan yasa yasaki kuka sosai yana binta da kallo yarike mata hijabi miyau na zuba daga bakinshi yana cizan lips dinshi dat were looking so pinkish and tender, adan tsorace ta kalleshi ganin yanda yake kuka yana kallon fuskarta kaman zai cinyeta yana taune lips dinshi yana girgiza mata kai alamun karta tafi yasa ta sake kawad dakai cike da mamaki aranta, meya sameshi?

Ya akayi ya zama haka? ganin yanda yacigaba da kukan yana goge fuskarshi akafarta yasa tadan juyo ta kalleshi shima ita yake kallo, Ahankali yasa bayan hannu yana goge idanunshi dasukai jajir sundan kumbura ga rigar jikinshi da wandon duksun baci da chabali dahar ya bushe, sake dagowa yayi ya kalleta yana kara rike kafarta hawaye yasake gangarowa daga idanunshi sosai taji zuciyarta yay wani iri dan tsugunnawa tayi agabanshi zatai magana yafada jikinta da sauri ya kankameta yana kuka ahankali babu abinda bayamai ciwo, kanshi ciwo, kafafunshi ciwo, hanunshi ciwo, ga zuciyarshi bayajinta kaman yanda normally yake jinta, yanda yafada jikinta yasa batasan lokacin data zauna dabas a kasan wurin ba ko'ina na jikinta na rawa, fashewa yayi da kuka sosai a wuyanta ya kulle hanunshi abayanta kaman yanda yake rungume Mami, kokarin tura shi take amma takasa ga jikinshi zafi sosai kaman wuta, adan rude tace "to ka sakeni kaga" makemata kafada yayi batare daya gane metake cemai ba, cikin wani irin kuka yace "u want to run and leave me again, that's how you use to do even in my dreams u will come but once I raised d curtain you will run and ask me to find u, I've found you now and I will never let you go" Wani irin tsorone ya shiga jikinta yanda babban namiji yabi ya rungumeta haka ahankali muryanta na rawa sosai tace "please ka sakeni" jin muryanta kaman tana kuka yasa ya saketa ya kalli fuskarta hawayen daya gani yasa ya make mata kafada yakai hanunshi ya share mata hawayen yana turo baki yana wani irin kallon eyes dinta, kallonshi tadanyi kafin murya chan kasa tace "what happen to you why are you like this?" shiru yayi yana wani irin kallonta dayasa taji wani iri da sauri ta dauke kai tace "you are not feeling fine, ur body is hot, stand up and go home" turo baki yayi yanadan lumlumshe ido yace "okay let's go together, you will see Mami, Abie and my Bid, zaki gansu?" yay maganan yana ware mata manyan idanunshi alamun tambaya da sauri ta kalleshi jin yanda yay maganan dan he don't really sound okay to wai meya dawo dashi hakane kodai ba mutumin nan da ya tsinceta a ruwa ya kaita asibiti bane?

Kodai idanunta ne, but ha'a bagashi nanba, wanan ai shine but yaushe yasami tabin kwakwalwa haka yadawo zararre ahankali muryanta na breaking sosai tace "please katashi katafi gidanku you are sick" make mata kafada yayi yana neman fadawa jikinta cikin wani irin yanayi yace "pls don't leave me again" matsawa tayi gefe da sauri ta mike tsaye, shima da sauri yamike tsaye ya dafa bango da sauri jin kanshi kaman zai fadi yasaki kuka sosai yana cizan lips dinshi, da sauri tadan matso kusada shi wani irin mugun tausayi taji yabata ahankali tace "are you fine?" turo mata baki yayi yanaso yakara fadawa jikinta da sauri ta matsa baya kirjinta na bugawa, ahankali cikin kuka yace "am sick".

Ji tayi kaman itama zatai kukan sabida yanda yake kukan yana kallonta har yanzu bai dena kallonta ba, da sauri tai hanyar fita tace "stand up and go home kasha magani is magrib" dan juyowa tayi ta kalleshi ganin har lokacin kuka yake yana binta da kallo, sosai taji zuciyarta yay wani iri, lekawa waje tayi amma bataga kowaba hakan yasa kawai tafice abinta da sauri dan taje gida kafin a fara neman ta amma still taji duktabi tadamu da sauri take tafiya dan takusa gida, tafiya tayi nakusan minti goma sanan ta shigo anguwan su, hannu tasa zata bude gate din gidansu taji an rikemata hijabi amugun tsorace ta juyo ganin shine idanunshi sunyi jajir bamaya iya bude idon sosai da kyau yasa ta juya ta kakkali anguwan su ganin ba mutane awaje yasa arude ta kalleshi tace "na bani, you followed me why?" make mata kafada yayi yace "I will never let you go again" da sauri takara kallon ko'ina tace "na shiga uku, wai menene to zakajamin fitina, sakenmin hijabi" ta fizge hijabin ta kaman zatai kuka dukta rude dan tasan ware haka Abba ke shigowa gida, dan sassautar da murya tayi dan wlh mugun tausayi taji yabata ayanda taganshi sha bakwai dinan gashi zazzabi yake sosai kuma koba komi yataimaka mata shima, gashi ya kafe ta da ido idanunshi cike fal da hawaye har wani irin shining suke, sosai taji wani iri hakan yasa ta kwantar da muryanta kasa sosai kaman meson lallashin yaro tace "you are sick, you are very sick, touch your body" ta daura hanunta akan wuyanta tanamai demonstrating yana kallonta kaman yasami wani irin TV, tace "your body is very hot, u are running temperature, go home kaji" takarashe maganan tana kallonshi kaman yanda yake kallonta bayako kyaftawa ahankali ya lumshe ido kafin yabudesu ahankali yadaurasu akanta, da sauri ta janye nata idon danya mugun cika mata ido sosai, batare data kalleshi ba tace "what do you want?" murya chan kasa yana kallonta yace "water" dan juyowa tayi ta kalleshi sanan tace "okay wait here bari naje na daukoma ruwa kaji sai kasha katafi, lemme bring water for you okay" gyadamata kai yayi yana binta da kallo, da sauri tabude gate dinsu ta shiga gidan, babu kowa a tsakar gidan, gidan shiru kaman ba mutane ciki kasancewar babu wuta da taji hayaniyan su Zainab suna kallo a falon Mama, hanyar sassan Kaka tayi da mugun saurinta ta shiga falon, Kaka bata falon hakan yasa tai hanyar dakinta ta hango hasken fitila a dakin Kaka, murmushi tayi aranta tace hala salla take saisa bata kira sunana ba dan data kirani, dakinta ta shiga ta tumbuke takalmin kafarta ta yarda jakan akan gadon takarasa da sauri inda jakan pure water daya da Kaka ta ijiye mata adakin ta dau guda daya ta juyo danta koma waje ta bashi da saurinta, wani irin cin karo taida mutum abayanta tai wani irin ihu tai baya zata fadi da sauri ya rikemata hannu shima afirgice dan yana tsoron ihu sosai, azabure Kaka data sallame salla tadau fitila tace "innalillahi Hamida incedai lafiya daga shigowan ki kin kurma uban ihu haka" arude Hamida ta kalli kofan dake abude na dakin da sauri ta fizge hanunta tai wurin kofan kafin Kaka ta iso tarufe tasaka sakata, mutum taji yafado ta bayanta dan shima ya tsorata sosai ya riketa, zatai magana Kaka ta karaso wajen ta buga wani irin uban salati.

"innalillahi Ke Hamida!" a mugun firgice ya juyo da Hamidan data kife da kofa ya ya rungumeta jikinshi na rawa sosai ya kalli Hamidan zaiyi magana, arude Hamida da jikinta ke wani irin masifar rawa ta daura yatsarta akan pink lips dinshi ta girgiza mai kai, ya ware manyan idanunshi yana kallonta, arude Kaka ta buga kofan.

"ke Hamida menene?

Meya sameki?

Budemin kofan nagani?

Ko cinnaka ne?
Chapter 22 · 0% Book details