Sashe 26
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Editing
________________________________________
Page 45 & 46
Malam na lado ya kalli matarshi tare da cewa , "Ubangiji Allah shi ne mai rayawa da kashewa haka ya kaddarowa Maryam rayuwarta , ke ma ina baki shawara ki fawwalawa Allah komai, domin ni na bar shi da Allah, a ranar gobe su tsaya da Maryam su yi Shari'a dan haka babu abin da zan yi a kai wannan shari'ar sai a lahira ."
Ta fashe da kuka tana cewa, "Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un Allah ya jikan ki Maryam."
Malam ya yi ajiyar zuciya.
Bayan alkali ya yi rubutu ya ci gaba da sauraran lauyoyi duk kan shaidun lauyansu Umar sun gamsar da kotu , sannan Sahid ya gabatar da wannan kadarori
Daga bisani ne alkali ya du'kufa yana rubutu ,
Yayin da kotu ta yi shiru , lauyoyi suna tattaunawa kowa yana jiran hukuncin da kotu zata yankewa Sahid
Bayan alkali ya gama rubutu ya d'ago ya fara gabatar da hukunci ..........
Ana fitowa daga kotu Nabila ta fara kiran wayar Umar, domin tana son sanar dashi irin nasarar da suka samu a kotu amma bai dauki kiran ba
Haka suka tafi gida suna ta murna da farin ciki ,har da su baba Garba wanda bayan sun koma gida ya wuce 'kauye cikin farin ciki .
Bayan wani lokaci ne Umar ya biyo kiran Nabila, nan suke sanar dashi irin nasarar da akai .
Ya yi matukar farin ciki sosai da sosai
"Mama Allah ya sa mu dace Allah ya jikan baban mu , kin ga ita gaskiya ba ta 'ya'ya yanzu ga shi Sahid ya rasa komai sai gidan bursun aka tura shi."
Jibril ya karasa maganar yana kallon mahaifiyarshi
Mahaifiyarshi ta yi ajiyar zuciya tana cewa, "Farin ciki na kawai yaran nan an mayar musu da dukiyarsu, shi kuma da aka tura shi kurkuku Allah ya shirye shi , Allah ya sa mu dace."
Jibril ya ce ,"Amen mama."
Su Garzali ne zaune suna karatu , Musa ya fado kansu cikin gudu yana haki
Allaro ne cikin fargaba ya tambaya, "Mene ya ke faruwa jikin malam d'in ne."?
Musa cikin wata murya kamar yana barbara ya ce ," Ku taso muje ga wanda ya sanadin mutuwar aunty Maryam can na ganshi a bayan layi."
Garzali ya ce ,"To mene zami masa kada malam ya sani fa.'
Musa ya ce ,"Babu yadda za ai ya sani kawai ku taho."
Suka shiga suka d'e'bo sanduna suka fita da gudu
Sauran almajiran 'kolawa suna kallon su .
Da gudu suka nufi inda Harun ya ke yana tare da motar shi a kofar wani gida
kafin ya an kara ya fara jin saukar duka ta ko'ina, ya fara ihu , dukanshi suke dauu dauu dass dasss har ya kai kasa ba su dena dukanshi ba har suka fara fasa masa jiki , ganin ya kai kasa ba ya motsi
Musa ya ce ,"Ku taho mu tafi mu bar maye anan."
Garzali ya d'aga sanda ya makawa gilass din motar na baya sannan ya sake 'kwalawa Harun sanda suka gudu.
Buja-buja suka koma gida alamun su duk mara sa gaskiya
"To idan ya mutu fa .Ya zami mun kashe rai."
Allaro ya yi maganar yana kallon su
Musa ya ce ,"Wallahi ba zai mutu ba , amma wata kila ya karye."
suka kwashe da dariya Musa ya ce ,"Tsoron da nake kada malam ya samu labari."
"Ba ta yadda za ai ya samu." Cewar Allaro
Mutanen anguwa ne suka taimaki Harun suka kaishi asubiti
bayan ya samu kanshi ya kira wani abokin shi Jamilu
"Yanzu wane ya maka wannan abin da Allah Harun."
Harun cikin zafin ciwo ya ce ,"To Allah ne masani ai domin wallahi ta baya naji an rufe ni da duka ban san komai ba banga kowa ba."
Jamilu ya ce ,"Wallahi dukan mutuwa su kai maka dubi kunne ka amma Likita ya ce ba matsala koh."?
Harun ya yi ajiyar zuciya tare da cewa ,"wallahi matukar ciwo wannan kunnen yake min , ni bama wannan ba so na ke na koma gida yau ."
Jamilu ya ce ,"Wai Tiga kake magana.Ka bari ka warke mana."
Harun ya ce ,"Ka ga idan zaka kai ni tom idan ba za ka kaini ba saina kira Yahaya duk da ina ta kiran wayarshi a kashe."
"Dan Allah ka bari kaji sauki mana haba Harun ."
Cikin bacin rai Harun ya ce ,"Wato na zauna sai yau a biyo dare a kashe ni koh ? Wallahi yau gida zan koma."
Jamilu ya ce ,"To ai shi ke nan Allah ya kyauta."
Yau dai Mahmud ya shigo kano, Zainab ta matukar farin ciki sosai ya ga kauna da soyayya a zahiri wajen Zainab,
Daga karshe har gidansu Hauwa yaje ya gaida mahaifinta wanda shi lu'utanal da kanshi ya ba shi invitation na bikin Hauwa ya sanar dashi yana gayyatar shi.
Sahid yana can yana fama da rayuwa sai yanzu yasan da cewa tabbas ba shi da gata ya yi matukar shiga tashin hankali yayin da ya lura tabbas hakkin mahaifishi sai ya bishi ,
Ga ciwon kafa da yake matukar fama da ita , a cikin satin ne da likita ya je bursun din aka duba masa ita aka kuma tabbatar cancer ce ta kama kafar tashi.Nan hankalin Sahid ya sake tashi matukar gaske .
___________________________________________
Yau su jafar duk suka shirya
domin tafiya ta ya Umar murna na passing out din da zasi
Nasir da Salma , Nabila, Jafar da Baba anje suka tafi
Soyayyar Nabila da Nasir ta yi matukar nisa sosai
Umar farin ciki kamar ya kashe shi amma yana ganinsu ya fashe da kuka mai matukar gwanin ban tausayi
"Haba Yaya Umar mene haka kuma." Jafar ya yi maganar yayin da ya rungume shi
Umar kuka wiwi tare da hawaye
Duk sai jikinsu ya yi sanyi
Umar cikin kukan ya fara musu magana, "Wallahi tun jiya nake jiran ku Jafar cikin matukar shauki , lokacin dana hango ku Kalisa na gano a tare daku tana ta min murmushi sai da kuka karaso na ga Nabila ce."
Wani tausayi suka ji ya sake rufe su mummunan Nabila data fara kuka .
Salma ta ce ,"Ku yi hakuri dan Allah Yaya , dama aunty Kalisa ai tana tare da kai addu'a kawai zamu cigaba da yi mata. "
Baba anje ta ce ,"Haka ne a dena kukan haka dan Allah domin farin ciki ne ya kawo mu."
"Yi hakuri Nabila, inajin zafi da wannan kukan da kike, ki dena baby dan Allah." Nasir yake yiwa Nabila magana yayin da ba kowa ke jin maganar ba .
Umar ya yi musu iso zuwa ciki , suka sami guri , ana ta gaisawa nan farin ciki ya karu aka ci aka sha cikin farin ciki .
Harun dai ya koma Tiga , nan iyayensa lamarin ya d'aga musu hankali, musamman jin bai samu aikin soja ba, ga kuma abin da ya faru dashi, haka sukai hakuri suka kuma fara nema masa magani , domin kunnenshi ba a cewa komai .
Bayan wani lokaci.
Wani irin kallo Zainab take yiwa Mahmud,
Mahmud ya yi murmushi yana cewa, "Mene kuma Zainab."
Zainab ta ce ,"Yaushe ne auren mu yaya Mahmud. "
Mahmud ya rike baki cikin mamaki yana cewa, "Eh tabbas kanwata ta girma har aure ma take so."
Ta ta'be baki tare shagwa'ba tana cewa, "Ni fa da gaske nake yaya Mahmud."
Mahmud murmushi ya sake yi yana kallonta yana gyara zaman hular dake kanshi yana cewa, "Ni ma Zainab wannan ranar nake jira , domin..."
Bai karasa maganar ba Ahmad ya shigo falon yana cewa, "Tashi mu tafi."
Mahmud ya kalleshi sannan ya tashi tsaye yana kallon Zainab.
"Amma zaka dawo ko."? Zainab ta yi wa Mahmud tambaya
ajiyar zuciya ya yi kana ya ce da ita ," Gaskiya Zainab bazan dawo ba , da zarar an d'aura auren zan wuce ba sai na dawo baya ba."
Zainab ba tare da taji dad'i ba , ba kuma ta so hakan ba ta yi musu sallama suka tafi
Mahmud da Ahmad suka nufi d'aurin auren Hauwa, eh tabbas an yi buduri an yi wasa da kud'i mu dai sai dai muce Allah ya sanya alheri.
Umar ne ya nufo gidan su Jafar sanye da kayan sojoji yana tura kofar gidan ya ci karo da Nabila da Nasir suna hira, Umar ya yi sand'a ya lalla'ba ta bayansu ba tare dasun sani ba .
Share, like and comment......................
Gubar Rayuwata
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Editing
Page 47 & 48
A hankali ya karasa bayan Nasir yayin da yaji yana cewa da Nabila ,"Tun da komai ya yi daidai a gaskiya sai a daura mana aure domin a halin yanzu babu wata..."
Kafin ya 'karasa yaji an tallafe masa 'keya, yana juyowa ya ga Umar
Duk kunya sai ta rufe Nabila musamman jin maganar da Umar ya fara ,"Eh lallai yaron nan wato ka girma harda zance aure , to ai sai ka bari ta gama makaranta, kai ma ka tsaya da kafafunka kafin ka yi maganar aure ko , amma ka ban mamaki Nasiru."
Umar ya karasa maganar yana rike ha'ba
Dariya suka yi a tare yayin da Nasir ya bawa Umar hanya domin ya wuce ciki
Wani mamaki ne ya kama Umar
"Me kake nufi." Ya tambayi Nasir
"Yaya ina ce wucewa zakai ciki."
Dariya Umar ya sa yana sake kaiwa kanin nashi duka yana cewa, "Dallah wuce muje ciki babu wata sauran soyyaya tunda na zo ."
Nabila da gudu tasa kai ta shige ciki , yayin da Umar ya dafa 'kanin nashi suka nufi cikin gidan .
Yauu tunda Harun ya tashi ya kasa gane inda yake masa ciwo , hakan ya sa ya yi 'kokari ya nufi asubiti wajen wani abokinshi Dactor Sa'id
Yana isa asubitin ya nufi office din shi yana bude kofa kuwa ya ganshi zaune yana cike wasu takardu
"Ahhh Aboki Harun kai ne tafe , masha Allah karaso." Cikin farin ciki doctor ya yi maganar
Harun yana zama doctor ya kula da tabbas ba shi da lafiya mussaman ganin Fuskarshi a kunbure ga kuma rama hakan ya sa kafin ma su gaisa ya fara cewa "Kaiiiii Harun sannu , baka da lafiya haka ."?
________________________________________
Page 45 & 46
Malam na lado ya kalli matarshi tare da cewa , "Ubangiji Allah shi ne mai rayawa da kashewa haka ya kaddarowa Maryam rayuwarta , ke ma ina baki shawara ki fawwalawa Allah komai, domin ni na bar shi da Allah, a ranar gobe su tsaya da Maryam su yi Shari'a dan haka babu abin da zan yi a kai wannan shari'ar sai a lahira ."
Ta fashe da kuka tana cewa, "Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un Allah ya jikan ki Maryam."
Malam ya yi ajiyar zuciya.
Bayan alkali ya yi rubutu ya ci gaba da sauraran lauyoyi duk kan shaidun lauyansu Umar sun gamsar da kotu , sannan Sahid ya gabatar da wannan kadarori
Daga bisani ne alkali ya du'kufa yana rubutu ,
Yayin da kotu ta yi shiru , lauyoyi suna tattaunawa kowa yana jiran hukuncin da kotu zata yankewa Sahid
Bayan alkali ya gama rubutu ya d'ago ya fara gabatar da hukunci ..........
Ana fitowa daga kotu Nabila ta fara kiran wayar Umar, domin tana son sanar dashi irin nasarar da suka samu a kotu amma bai dauki kiran ba
Haka suka tafi gida suna ta murna da farin ciki ,har da su baba Garba wanda bayan sun koma gida ya wuce 'kauye cikin farin ciki .
Bayan wani lokaci ne Umar ya biyo kiran Nabila, nan suke sanar dashi irin nasarar da akai .
Ya yi matukar farin ciki sosai da sosai
"Mama Allah ya sa mu dace Allah ya jikan baban mu , kin ga ita gaskiya ba ta 'ya'ya yanzu ga shi Sahid ya rasa komai sai gidan bursun aka tura shi."
Jibril ya karasa maganar yana kallon mahaifiyarshi
Mahaifiyarshi ta yi ajiyar zuciya tana cewa, "Farin ciki na kawai yaran nan an mayar musu da dukiyarsu, shi kuma da aka tura shi kurkuku Allah ya shirye shi , Allah ya sa mu dace."
Jibril ya ce ,"Amen mama."
Su Garzali ne zaune suna karatu , Musa ya fado kansu cikin gudu yana haki
Allaro ne cikin fargaba ya tambaya, "Mene ya ke faruwa jikin malam d'in ne."?
Musa cikin wata murya kamar yana barbara ya ce ," Ku taso muje ga wanda ya sanadin mutuwar aunty Maryam can na ganshi a bayan layi."
Garzali ya ce ,"To mene zami masa kada malam ya sani fa.'
Musa ya ce ,"Babu yadda za ai ya sani kawai ku taho."
Suka shiga suka d'e'bo sanduna suka fita da gudu
Sauran almajiran 'kolawa suna kallon su .
Da gudu suka nufi inda Harun ya ke yana tare da motar shi a kofar wani gida
kafin ya an kara ya fara jin saukar duka ta ko'ina, ya fara ihu , dukanshi suke dauu dauu dass dasss har ya kai kasa ba su dena dukanshi ba har suka fara fasa masa jiki , ganin ya kai kasa ba ya motsi
Musa ya ce ,"Ku taho mu tafi mu bar maye anan."
Garzali ya d'aga sanda ya makawa gilass din motar na baya sannan ya sake 'kwalawa Harun sanda suka gudu.
Buja-buja suka koma gida alamun su duk mara sa gaskiya
"To idan ya mutu fa .Ya zami mun kashe rai."
Allaro ya yi maganar yana kallon su
Musa ya ce ,"Wallahi ba zai mutu ba , amma wata kila ya karye."
suka kwashe da dariya Musa ya ce ,"Tsoron da nake kada malam ya samu labari."
"Ba ta yadda za ai ya samu." Cewar Allaro
Mutanen anguwa ne suka taimaki Harun suka kaishi asubiti
bayan ya samu kanshi ya kira wani abokin shi Jamilu
"Yanzu wane ya maka wannan abin da Allah Harun."
Harun cikin zafin ciwo ya ce ,"To Allah ne masani ai domin wallahi ta baya naji an rufe ni da duka ban san komai ba banga kowa ba."
Jamilu ya ce ,"Wallahi dukan mutuwa su kai maka dubi kunne ka amma Likita ya ce ba matsala koh."?
Harun ya yi ajiyar zuciya tare da cewa ,"wallahi matukar ciwo wannan kunnen yake min , ni bama wannan ba so na ke na koma gida yau ."
Jamilu ya ce ,"Wai Tiga kake magana.Ka bari ka warke mana."
Harun ya ce ,"Ka ga idan zaka kai ni tom idan ba za ka kaini ba saina kira Yahaya duk da ina ta kiran wayarshi a kashe."
"Dan Allah ka bari kaji sauki mana haba Harun ."
Cikin bacin rai Harun ya ce ,"Wato na zauna sai yau a biyo dare a kashe ni koh ? Wallahi yau gida zan koma."
Jamilu ya ce ,"To ai shi ke nan Allah ya kyauta."
Yau dai Mahmud ya shigo kano, Zainab ta matukar farin ciki sosai ya ga kauna da soyayya a zahiri wajen Zainab,
Daga karshe har gidansu Hauwa yaje ya gaida mahaifinta wanda shi lu'utanal da kanshi ya ba shi invitation na bikin Hauwa ya sanar dashi yana gayyatar shi.
Sahid yana can yana fama da rayuwa sai yanzu yasan da cewa tabbas ba shi da gata ya yi matukar shiga tashin hankali yayin da ya lura tabbas hakkin mahaifishi sai ya bishi ,
Ga ciwon kafa da yake matukar fama da ita , a cikin satin ne da likita ya je bursun din aka duba masa ita aka kuma tabbatar cancer ce ta kama kafar tashi.Nan hankalin Sahid ya sake tashi matukar gaske .
___________________________________________
Yau su jafar duk suka shirya
domin tafiya ta ya Umar murna na passing out din da zasi
Nasir da Salma , Nabila, Jafar da Baba anje suka tafi
Soyayyar Nabila da Nasir ta yi matukar nisa sosai
Umar farin ciki kamar ya kashe shi amma yana ganinsu ya fashe da kuka mai matukar gwanin ban tausayi
"Haba Yaya Umar mene haka kuma." Jafar ya yi maganar yayin da ya rungume shi
Umar kuka wiwi tare da hawaye
Duk sai jikinsu ya yi sanyi
Umar cikin kukan ya fara musu magana, "Wallahi tun jiya nake jiran ku Jafar cikin matukar shauki , lokacin dana hango ku Kalisa na gano a tare daku tana ta min murmushi sai da kuka karaso na ga Nabila ce."
Wani tausayi suka ji ya sake rufe su mummunan Nabila data fara kuka .
Salma ta ce ,"Ku yi hakuri dan Allah Yaya , dama aunty Kalisa ai tana tare da kai addu'a kawai zamu cigaba da yi mata. "
Baba anje ta ce ,"Haka ne a dena kukan haka dan Allah domin farin ciki ne ya kawo mu."
"Yi hakuri Nabila, inajin zafi da wannan kukan da kike, ki dena baby dan Allah." Nasir yake yiwa Nabila magana yayin da ba kowa ke jin maganar ba .
Umar ya yi musu iso zuwa ciki , suka sami guri , ana ta gaisawa nan farin ciki ya karu aka ci aka sha cikin farin ciki .
Harun dai ya koma Tiga , nan iyayensa lamarin ya d'aga musu hankali, musamman jin bai samu aikin soja ba, ga kuma abin da ya faru dashi, haka sukai hakuri suka kuma fara nema masa magani , domin kunnenshi ba a cewa komai .
Bayan wani lokaci.
Wani irin kallo Zainab take yiwa Mahmud,
Mahmud ya yi murmushi yana cewa, "Mene kuma Zainab."
Zainab ta ce ,"Yaushe ne auren mu yaya Mahmud. "
Mahmud ya rike baki cikin mamaki yana cewa, "Eh tabbas kanwata ta girma har aure ma take so."
Ta ta'be baki tare shagwa'ba tana cewa, "Ni fa da gaske nake yaya Mahmud."
Mahmud murmushi ya sake yi yana kallonta yana gyara zaman hular dake kanshi yana cewa, "Ni ma Zainab wannan ranar nake jira , domin..."
Bai karasa maganar ba Ahmad ya shigo falon yana cewa, "Tashi mu tafi."
Mahmud ya kalleshi sannan ya tashi tsaye yana kallon Zainab.
"Amma zaka dawo ko."? Zainab ta yi wa Mahmud tambaya
ajiyar zuciya ya yi kana ya ce da ita ," Gaskiya Zainab bazan dawo ba , da zarar an d'aura auren zan wuce ba sai na dawo baya ba."
Zainab ba tare da taji dad'i ba , ba kuma ta so hakan ba ta yi musu sallama suka tafi
Mahmud da Ahmad suka nufi d'aurin auren Hauwa, eh tabbas an yi buduri an yi wasa da kud'i mu dai sai dai muce Allah ya sanya alheri.
Umar ne ya nufo gidan su Jafar sanye da kayan sojoji yana tura kofar gidan ya ci karo da Nabila da Nasir suna hira, Umar ya yi sand'a ya lalla'ba ta bayansu ba tare dasun sani ba .
Share, like and comment......................
Gubar Rayuwata
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Editing
Page 47 & 48
A hankali ya karasa bayan Nasir yayin da yaji yana cewa da Nabila ,"Tun da komai ya yi daidai a gaskiya sai a daura mana aure domin a halin yanzu babu wata..."
Kafin ya 'karasa yaji an tallafe masa 'keya, yana juyowa ya ga Umar
Duk kunya sai ta rufe Nabila musamman jin maganar da Umar ya fara ,"Eh lallai yaron nan wato ka girma harda zance aure , to ai sai ka bari ta gama makaranta, kai ma ka tsaya da kafafunka kafin ka yi maganar aure ko , amma ka ban mamaki Nasiru."
Umar ya karasa maganar yana rike ha'ba
Dariya suka yi a tare yayin da Nasir ya bawa Umar hanya domin ya wuce ciki
Wani mamaki ne ya kama Umar
"Me kake nufi." Ya tambayi Nasir
"Yaya ina ce wucewa zakai ciki."
Dariya Umar ya sa yana sake kaiwa kanin nashi duka yana cewa, "Dallah wuce muje ciki babu wata sauran soyyaya tunda na zo ."
Nabila da gudu tasa kai ta shige ciki , yayin da Umar ya dafa 'kanin nashi suka nufi cikin gidan .
Yauu tunda Harun ya tashi ya kasa gane inda yake masa ciwo , hakan ya sa ya yi 'kokari ya nufi asubiti wajen wani abokinshi Dactor Sa'id
Yana isa asubitin ya nufi office din shi yana bude kofa kuwa ya ganshi zaune yana cike wasu takardu
"Ahhh Aboki Harun kai ne tafe , masha Allah karaso." Cikin farin ciki doctor ya yi maganar
Harun yana zama doctor ya kula da tabbas ba shi da lafiya mussaman ganin Fuskarshi a kunbure ga kuma rama hakan ya sa kafin ma su gaisa ya fara cewa "Kaiiiii Harun sannu , baka da lafiya haka ."?