Sashe 23
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Editing
_________________________________________
Page 39 & 40
Jafar ya kalli kanwar tashi yana cewa," nima haka Nabila, tun jiya da daddare ma kuwa."
Baba anje ta ce ,"Tofa! Ikon Allah, Allah ya sa alheri ne yake tunkaro mu."
Kafin su kai ga cewa Amin suka Umar kamar an wantsiloshi ya shigo yana haki idanunsa sun yi jajir , ga dukkan alamu akwai damuwa.
Duk tashi tsaye su kai kafin kowa ya ce komai yana ta sake saken abin da ya shigar da Umar wannan hali .
"Tantancewar sojin da akai babu shi ne ? Amma hakan ba zai tada hankalin Umar ba ." Jafar yake fada cikin zuciyar shi .
"Bai zo ba."??? Umar ya yi musu tambayar cikin tsananin jiran amsa .
Kallon juna suka yi alamun samm basu gane mene yake nufi ba .
Jafar ya karasa kusa dashi da cewa ," Kwantar da hankalin ka Umar, mene yake faruwa ne ."
Daga can wajen gidan kuwa wani saurayi ne mai jiki wanda ya ginu ya wadatu da farar fata, ya nufo gidan yana d'ingisawa , yayin da yake tafiya cikin isa yana tattare farar jallabiyar dake jikinshi .
"Sahid nake magana akai domin ya dawo Nigeria a daren jiya , kuma duk inda yake zanje na nemo shi." Umar ya fada tare da matukar nuna kiyayyar Sahid a zahiri
Duk wani tashin hankali suka ji ya sake bugar musu zuciya da kiran sunan maci amanarsu
"Assalamu alaikum."
Sautin sallamar da suka ji ke nan wacce ta daskarar dasu a tsaye
Tabbas yau idanunsu sun ga abin mamaki domin kuwa Sahid ne tsaye a gabansu , yayi wani kyau dashi yayi kiba .
Wasu zafafan hawaye suka zubo wa Nabila masu matukar ciwo
Umar ya kasa cewa komai domin zuciyar shi tana ayyana masa mummunan abu a kan Sahid, hakan ya sa yake 'kokarin sarrafa kanshi
"SAHID".
Jafar ya kira sunan shi
," Na'am Jafar, na sani cewa bani da bakin magana a gabanku , amma ba a son raina komai ya faru ba , na yi tafiya Britannia, jiya da na dawo nake jin labarin mutuwar Kalisa. "
'Kuummmm
Wani wawan duka da Umar ya kai masa , ya fadi ya bige da bango, Umar ya taso shi cikin tsananin takaici ya cigaba da dukanshi .
"Me nai maka ne , haka , mutuwar Kalisa ai haka Allah ya tsaro me ya sa za ka doran laifi."
Cewar Sahid ke nan yayin da Umar yake bibbige shi .
"Jafar ka yi masa magana mana ya dena dukana , ina ciwon kafa."
Jafar ya nufi bayan Umar ya ture Umar ya amshi Sahid.
Yadda Sahid ya ganshi a tsaye ya fara ajiyar zuciya da samun 'yancin da ya yi .
Ba tare da ya ankara Jafar ya kwarfe shi ya fadi ya bugu da bango, ya taso shi ya ma'kure shi kana ya fara magana.
"Burinka ya cika ba , Kalisa ta rasu , kuma ka zaune dukiyarmu."
Gummmm
Ya bugashi jikin wani karfe , sai jini .
"Jafar ku bari karku kashe shi mana , ya jigata sosai." Baba anje ta yi maganar tana kokarin kwace Sahid a hannun Jafar.
Jafar bai san lokacin da ya ture baba anje ba , Allah ya sa bafa fadi ba , ya kalleta cikin takaici da tarin hawayen dake idanunshi , yana cewa.
"Shin baki tuna lokacin da Kalisa take kwance ba ? ko kin manta sanda muka tashi aka yi garkuwa da Nabila, kin mance ranar da Kalisa tai Allah wadai dashi , mu bamu jigata ba ne baba ? ko kuwa bamu ga tashin hankali ba ."
Ya aje maganar cikin wasu zafafan hawaye da suka zubo masa , sannan ya maida kallon shi ga Sahid yana cewa, "Kai azzalumi ne mayaudari ka kashe Kalisa ka kashe mahaifin ka ."
Ya tun kude shi gefe
Sahid yana jiri ya ya tashi ya nemi hanyar fita ya hau mota ya tafi .Kai tsaye masaukinshi ya nufa wato hotel ya gyara jikinsa ya sauya kaya, kana yasha magani.
Kwanciya ya yi da nufin hutawa sai maganar Jafar take fado masa tana masa amsa kuwa .
"Kai azzalumi ne mayaudari ka kashe Kalisa ka kashe mahaifin ka."
Ya yi ajiyar zuciya ya tashi zaune, ya dauki mukullin motar shi da kafar shi mara lafiya da taji duka ya nufi gidan nasu .
Zuciyoyin su jafar tafasa suke yi matukar gaske, hakan ya sa suka fita domin daukar matakin da ya dace a kan Sahid.
Hauwa ce cikin wani babban falo suna hira da kawarta surayya
Hauwa ta zubawa Surayya idanu tana cewa, "Allah koh , ki ce sabon saurayi kika yi , shi kuma Faruk din fa."
Surayya ta kalli Hauwa tare da jefa mata wata harara tana cewa, "Shi fa soja ne, kuma wallahi ya kwanta mini a rai domin gaye ne Hauwa."
Hauwa ta ta'be baki tare da tashi tsaye tana cewa, "Kin ga ni tafiya zan yi , har akwai wani gaye da zai kuma shiga zuciyar ki bayan Faruk, wallahi kin bani kunya."
Surayya cikin dariya da zolaya ita ma ta ta shi tsaye tana cewa, "Wallahi duk sanda ya zo san had'aku ku gaisa besty ta."
"Mtwss." Hauwa ta ja tsaki tare ta bud'e kofar falon .
Lokacin ne wani farin mutum lukuti mai sanye da farar shadda ya turo kai , ba kowa ba ne kuwa fa ce ambassador.
Nan Hauwa ta gaidashi har yake tambayar mahaifin ta , nan take sanar masa yana gaida shi
shima ambassador ya sake aika masa da sakon gaisuwa.
Haka Hauwa ta dawo gida.........
Anan bangaren su Zainab kuwa
Suna zaune a falo ita da yayan nata Ahmad, laptop ce a gabanshi yana dannawa
Zainab ta ce ,"Yaya Ahmad dan Allah ka yi hakuri ka bawa daddy hakuri, ka amson wayata, wallahi na tuba na canza."
Ahmad ya kalleta ya ta'be baki ya ci gaba da aikinsa
"Haba yayana Ahmad, wallahi na tuba ka kula ni mana , har abada babu ni ba HARUN."
Tsaki Ahmad yaja yana wurga mata harara "Dan Allah ki barni na yi aikina , ki bari ki kuma hankali da kanshi Dady zai baki."
Wayar Ahmad ce ta fara ruri , yana ganin mai kira ya dauka cikin farin ciki.
A yadda Zainab ta ga yayan nata yana waya tasan cewa Mahmud ne .
hakan ya sa yana gama wayar ta titsiye shi da tambaya, "Wa ne Yaya."?
Ahmad cikin farin ciki da washe baki ya ce ," Wallahi Mahmud ne , yana sanar min ya samu aiki a matatar mai ta kasa, abin ya farantan rai ."
Zainab ta yi murmushi tana cewa, "To yaushe zai zo."?
Ahmad ya jefa mata wani kallo yana cewa," To sannu , ke da ganin Mahmud sai Allah, sai dai ke ki shirya kije."
Ya cigaba da aikinshi
Duk atake Zainab ta shiga damuwa .
Bayan ya yi burkin motar shi a kofar gidansu, ya fito da kyer ya shiga cikin gidan .
"Assalamu alaikum."
Sahid ya yi sallamar a cikin gidan , wanda bai ga komai ba sai tabar ma a tsakar gidan , sallama ya sake yi a karo na biyu babu amsa .
Yanayin yadda yaji karshi shi na masa zugi da zafi ya sa ya nufi tabarmar da shirin zama
"Kar ka sake ka zauna mini a gida mugu azzalumi."
Cewar mahaifiyar shi data fito daga daki ,
a lokacin ne shima Jibril ya fito daga wanka .
Tsololo Sahid ya yi da baki yana kallan mahaifiyar shi dajin wannan furuci da ta yi masa
"Ka gaggauta fita a cikin gidan nan Sahid."
Ta kuma fada cikin kunci
Sahid ya daure ya ce ,"Mama da gaske ne baba ya rasu."?
Jibril dai bai ce komai kawai yana sauraransu
"Sahid ni mahaifiyar ka Binta , babu abin da zance maka tsakanina da kai , abu guda dana sani ka ci amana, kuma tana tafe domin cinka , ka je za ka gani."
Tana gama magana ta shige daki , Jibril ma ya shige dakinshi ya sanya kaya ya fita , yana fita ya ci karo da 'yan sanda tare da Umar da Jafar .
Kafin su yi masa tambayar ina Sahid, Sahid ya fito suka sashi a mota suka tafi .
Share and comment...............................
Gubar Rayuwata
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
_________________________________________
Page 39 & 40
Jafar ya kalli kanwar tashi yana cewa," nima haka Nabila, tun jiya da daddare ma kuwa."
Baba anje ta ce ,"Tofa! Ikon Allah, Allah ya sa alheri ne yake tunkaro mu."
Kafin su kai ga cewa Amin suka Umar kamar an wantsiloshi ya shigo yana haki idanunsa sun yi jajir , ga dukkan alamu akwai damuwa.
Duk tashi tsaye su kai kafin kowa ya ce komai yana ta sake saken abin da ya shigar da Umar wannan hali .
"Tantancewar sojin da akai babu shi ne ? Amma hakan ba zai tada hankalin Umar ba ." Jafar yake fada cikin zuciyar shi .
"Bai zo ba."??? Umar ya yi musu tambayar cikin tsananin jiran amsa .
Kallon juna suka yi alamun samm basu gane mene yake nufi ba .
Jafar ya karasa kusa dashi da cewa ," Kwantar da hankalin ka Umar, mene yake faruwa ne ."
Daga can wajen gidan kuwa wani saurayi ne mai jiki wanda ya ginu ya wadatu da farar fata, ya nufo gidan yana d'ingisawa , yayin da yake tafiya cikin isa yana tattare farar jallabiyar dake jikinshi .
"Sahid nake magana akai domin ya dawo Nigeria a daren jiya , kuma duk inda yake zanje na nemo shi." Umar ya fada tare da matukar nuna kiyayyar Sahid a zahiri
Duk wani tashin hankali suka ji ya sake bugar musu zuciya da kiran sunan maci amanarsu
"Assalamu alaikum."
Sautin sallamar da suka ji ke nan wacce ta daskarar dasu a tsaye
Tabbas yau idanunsu sun ga abin mamaki domin kuwa Sahid ne tsaye a gabansu , yayi wani kyau dashi yayi kiba .
Wasu zafafan hawaye suka zubo wa Nabila masu matukar ciwo
Umar ya kasa cewa komai domin zuciyar shi tana ayyana masa mummunan abu a kan Sahid, hakan ya sa yake 'kokarin sarrafa kanshi
"SAHID".
Jafar ya kira sunan shi
," Na'am Jafar, na sani cewa bani da bakin magana a gabanku , amma ba a son raina komai ya faru ba , na yi tafiya Britannia, jiya da na dawo nake jin labarin mutuwar Kalisa. "
'Kuummmm
Wani wawan duka da Umar ya kai masa , ya fadi ya bige da bango, Umar ya taso shi cikin tsananin takaici ya cigaba da dukanshi .
"Me nai maka ne , haka , mutuwar Kalisa ai haka Allah ya tsaro me ya sa za ka doran laifi."
Cewar Sahid ke nan yayin da Umar yake bibbige shi .
"Jafar ka yi masa magana mana ya dena dukana , ina ciwon kafa."
Jafar ya nufi bayan Umar ya ture Umar ya amshi Sahid.
Yadda Sahid ya ganshi a tsaye ya fara ajiyar zuciya da samun 'yancin da ya yi .
Ba tare da ya ankara Jafar ya kwarfe shi ya fadi ya bugu da bango, ya taso shi ya ma'kure shi kana ya fara magana.
"Burinka ya cika ba , Kalisa ta rasu , kuma ka zaune dukiyarmu."
Gummmm
Ya bugashi jikin wani karfe , sai jini .
"Jafar ku bari karku kashe shi mana , ya jigata sosai." Baba anje ta yi maganar tana kokarin kwace Sahid a hannun Jafar.
Jafar bai san lokacin da ya ture baba anje ba , Allah ya sa bafa fadi ba , ya kalleta cikin takaici da tarin hawayen dake idanunshi , yana cewa.
"Shin baki tuna lokacin da Kalisa take kwance ba ? ko kin manta sanda muka tashi aka yi garkuwa da Nabila, kin mance ranar da Kalisa tai Allah wadai dashi , mu bamu jigata ba ne baba ? ko kuwa bamu ga tashin hankali ba ."
Ya aje maganar cikin wasu zafafan hawaye da suka zubo masa , sannan ya maida kallon shi ga Sahid yana cewa, "Kai azzalumi ne mayaudari ka kashe Kalisa ka kashe mahaifin ka ."
Ya tun kude shi gefe
Sahid yana jiri ya ya tashi ya nemi hanyar fita ya hau mota ya tafi .Kai tsaye masaukinshi ya nufa wato hotel ya gyara jikinsa ya sauya kaya, kana yasha magani.
Kwanciya ya yi da nufin hutawa sai maganar Jafar take fado masa tana masa amsa kuwa .
"Kai azzalumi ne mayaudari ka kashe Kalisa ka kashe mahaifin ka."
Ya yi ajiyar zuciya ya tashi zaune, ya dauki mukullin motar shi da kafar shi mara lafiya da taji duka ya nufi gidan nasu .
Zuciyoyin su jafar tafasa suke yi matukar gaske, hakan ya sa suka fita domin daukar matakin da ya dace a kan Sahid.
Hauwa ce cikin wani babban falo suna hira da kawarta surayya
Hauwa ta zubawa Surayya idanu tana cewa, "Allah koh , ki ce sabon saurayi kika yi , shi kuma Faruk din fa."
Surayya ta kalli Hauwa tare da jefa mata wata harara tana cewa, "Shi fa soja ne, kuma wallahi ya kwanta mini a rai domin gaye ne Hauwa."
Hauwa ta ta'be baki tare da tashi tsaye tana cewa, "Kin ga ni tafiya zan yi , har akwai wani gaye da zai kuma shiga zuciyar ki bayan Faruk, wallahi kin bani kunya."
Surayya cikin dariya da zolaya ita ma ta ta shi tsaye tana cewa, "Wallahi duk sanda ya zo san had'aku ku gaisa besty ta."
"Mtwss." Hauwa ta ja tsaki tare ta bud'e kofar falon .
Lokacin ne wani farin mutum lukuti mai sanye da farar shadda ya turo kai , ba kowa ba ne kuwa fa ce ambassador.
Nan Hauwa ta gaidashi har yake tambayar mahaifin ta , nan take sanar masa yana gaida shi
shima ambassador ya sake aika masa da sakon gaisuwa.
Haka Hauwa ta dawo gida.........
Anan bangaren su Zainab kuwa
Suna zaune a falo ita da yayan nata Ahmad, laptop ce a gabanshi yana dannawa
Zainab ta ce ,"Yaya Ahmad dan Allah ka yi hakuri ka bawa daddy hakuri, ka amson wayata, wallahi na tuba na canza."
Ahmad ya kalleta ya ta'be baki ya ci gaba da aikinsa
"Haba yayana Ahmad, wallahi na tuba ka kula ni mana , har abada babu ni ba HARUN."
Tsaki Ahmad yaja yana wurga mata harara "Dan Allah ki barni na yi aikina , ki bari ki kuma hankali da kanshi Dady zai baki."
Wayar Ahmad ce ta fara ruri , yana ganin mai kira ya dauka cikin farin ciki.
A yadda Zainab ta ga yayan nata yana waya tasan cewa Mahmud ne .
hakan ya sa yana gama wayar ta titsiye shi da tambaya, "Wa ne Yaya."?
Ahmad cikin farin ciki da washe baki ya ce ," Wallahi Mahmud ne , yana sanar min ya samu aiki a matatar mai ta kasa, abin ya farantan rai ."
Zainab ta yi murmushi tana cewa, "To yaushe zai zo."?
Ahmad ya jefa mata wani kallo yana cewa," To sannu , ke da ganin Mahmud sai Allah, sai dai ke ki shirya kije."
Ya cigaba da aikinshi
Duk atake Zainab ta shiga damuwa .
Bayan ya yi burkin motar shi a kofar gidansu, ya fito da kyer ya shiga cikin gidan .
"Assalamu alaikum."
Sahid ya yi sallamar a cikin gidan , wanda bai ga komai ba sai tabar ma a tsakar gidan , sallama ya sake yi a karo na biyu babu amsa .
Yanayin yadda yaji karshi shi na masa zugi da zafi ya sa ya nufi tabarmar da shirin zama
"Kar ka sake ka zauna mini a gida mugu azzalumi."
Cewar mahaifiyar shi data fito daga daki ,
a lokacin ne shima Jibril ya fito daga wanka .
Tsololo Sahid ya yi da baki yana kallan mahaifiyar shi dajin wannan furuci da ta yi masa
"Ka gaggauta fita a cikin gidan nan Sahid."
Ta kuma fada cikin kunci
Sahid ya daure ya ce ,"Mama da gaske ne baba ya rasu."?
Jibril dai bai ce komai kawai yana sauraransu
"Sahid ni mahaifiyar ka Binta , babu abin da zance maka tsakanina da kai , abu guda dana sani ka ci amana, kuma tana tafe domin cinka , ka je za ka gani."
Tana gama magana ta shige daki , Jibril ma ya shige dakinshi ya sanya kaya ya fita , yana fita ya ci karo da 'yan sanda tare da Umar da Jafar .
Kafin su yi masa tambayar ina Sahid, Sahid ya fito suka sashi a mota suka tafi .
Share and comment...............................
Gubar Rayuwata
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)