Sashe 11
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Timm ya fadi kasa kamar matacce , asubitin cikin gari aka karasa dasu , tare da turasu emergency
Sai ga su Nabila sha'be -sha'be cikin kuka da matukar tashin hankali
suna isa wajen doctor ya fito daga d'akin Umar
da sauri suka tare shi , Jafar ne ya ce "Ya jikin na su likita."?
Baba Anje cikin damuwa ta kallo likita tana sauran amsa
" Ita macen tana ICU room, gaskiya akwai bukatar a yi mata aiki, shi na mijin yana sume , amma nan da anjuma..... "
Likita maganar da yaji a bayansa ne ya sa su duk baba anje saurin juyawa
"Likita ya jikin Kalisa ta." Umar ya fad'a cikin wasu ruwan hawaye dake shirin zubo masa
"Haba malam ka koma ka kwanta , komai zai iya faruwa da kai a wannan yanayi kana bukatar hutu da kulawa."
Dactor ya yi maganar yana kallon Umar
Umar ya karaso gabansu , kawai Nabila ta fashe da kuka ta rungume Jafar
ita ma baba anje duk tausayin Umar ya rufe ta da ganin ciwon dake tare dashi
"Dan Allah yaya Umar ka je ka huta a halin yanzu kaji abin da doctor ya ce ."
Jafar ya yi maganar Nabila kwance a kirjinsa yana rike da hannun Umar.
Umar ya janye hannunshi tare da fara cewa ," Ni bana jin komai Jafar , yanzu kawai Kalisa ce damuwar , domin karku mance akwai bukatar yi mata aiki tun kafin wannan accident din."
Wasu zafafan hawaye suka zubo masa sannan ya ci gaba da cewa ,"Na ga karfe ya huda gwiwar Kalisa, na ji zafi a zuciyata kuma na bayar ta rasu , yanzu kawai lafiya zamu nema mata. "
Baba anje cikin tashin hankali ta ce "Gaskiya ne , innalillahi wa inna'ilaihir raji'un."
Dactor ya ce "Tom gaskiya ciwonta ni bazan iya dubata ba , ku jira kwana biyu likita yana zuwa." Yana gama maganar ya wuce
Ba zato sukaji Umar ya shako sa ,"Kai wanne mara hankali ne , har gobe zamu jira tana cikin wannan yanayin, ina imaninka da tausayinka ka je fa su."?
Likita da ya ji shakar sa ta yi yawa cikin wahala ya fisge ya hankade Umar "Kai mahaukacin ina ne , bari na kira security su fitar da kai." Dactor din ya karasa maganar ya nufi wajen masu gadi
Umar ya ce , "Mu dauki Kalisa mu koma babban asubitin dactor Aisha hakan zai fi."
Nabila ta yi ajiyar zuciya tana kiran sunan Allah .
Mahmud ne ya fito waje yana duban yanayin anguwar yadda tsarinta kullum yake sake burgeshi , duba ga manyan gidaje da sanyin anguwar
hakan ya sa har yau ya kasa komawa gida, har Aminu ya koma , amma shi ba shi da niyya , amma babban dalilin 'kin komawarsa a kan Zainab ne .
Sake bude idanunshi ya yi yana sake kallon abin da ya hango daga gefe ,
kofar gidan wani mutum malam na lado , wanda har almajirai yana dasu
Mahmud ido ya sake zubawa yana kallon ikon Allah
"Mene Harun yake yi anan".
Mahmud ya tambayi kanshi .
Daga bisani lokacin da Harun ya kula da Mahmud ya yi murmushi ya nufo wajensa.
" Malam Mahmud me ake kuma anan." Harun ya tambaya lokacin da ya karaso gaban shi
Mahmud zuciyarshi wata irin tafasa take masa kamar ya kai masa duka, amma ya daure ya kalle shi yana cewa "Mene ka zo yi a wannan anguwar."?
Harun ya sheke da dariya har da tafawa , sannan ya ce ," Mahmud ni wallahi ma dariya kake bani , to mene ya dameka dani, sannan kuma kar ka yi zaton na bar Zainab, Wallahi ban bar ta ba , kai ne kamin shamaki da ita , amma wallahi kasa a ranka da zarar na zama soja wallahi sai na kawar da kai dan na samu Zainab, ka rubuta ka aji ye ni Harun ni ne ajalinka. "
Ajiyar zuciya Mahmud ya yi yana cewa, " Mu yi mu gani , kar kai tunanin dan ka 'bata Asma'u na ya zamo ina jin tsoron ka......."
Mahmud bai karasa maganar ba Harun ya dakatar dashi da cewa ,"Zan yi wulakanci idan nasa kaki , wallahi Mahmud sai na wulakantaka, zaka gani."
Ya wuce ya yi tafiyarsa
Ran Mahmud ya matukar baci sosai , gida ya shiga cikin bacin rai , ya shiga cikin lambu ya kasa tsaye ya kasa zaune , kawai maganar Harun ce take masa yawo , cikin ranshi yake sake nanata zancen
"Tabbas Harun azzalumi ne , zai aikata duk abin da yake so, yanzu mene mafita."?
Mahmud ya dafa kanshi da ya farai masa ciwo " To ko dai na shigar dashi kara. "?
Ya tambayi kanshi , tare da bada amsa kuma
" Gaskiya 'a'a wannan ba shawara ba ce ."
Ya tsuguna kamar mai shirin yin kuka , sannan ya tashi tsaye yana kallon sararin sama yana ajiyar zuciya.
Da sauri ya dawo da kanshi kasa tare da rudewa da farin cikin shawarar da ta zo masa,
da sauri ya shiga cikin gidan ya wuce d'akinshi ya dauko wayarshi dake caji ya zauna a bakin gado .
Sannan ya fara danna wayar yana cewa, "Hhh kwananka ya kare Harun." A daidai lokacin yana kiran numbar Hauwa 'yar gidan lu'utanal
Kamar jira take karaf ta dauki kiran "Ya Mahmud manyan gari kwana biyu." Ta yi maganar cikin yaren turanci
Sai ga su Nabila sha'be -sha'be cikin kuka da matukar tashin hankali
suna isa wajen doctor ya fito daga d'akin Umar
da sauri suka tare shi , Jafar ne ya ce "Ya jikin na su likita."?
Baba Anje cikin damuwa ta kallo likita tana sauran amsa
" Ita macen tana ICU room, gaskiya akwai bukatar a yi mata aiki, shi na mijin yana sume , amma nan da anjuma..... "
Likita maganar da yaji a bayansa ne ya sa su duk baba anje saurin juyawa
"Likita ya jikin Kalisa ta." Umar ya fad'a cikin wasu ruwan hawaye dake shirin zubo masa
"Haba malam ka koma ka kwanta , komai zai iya faruwa da kai a wannan yanayi kana bukatar hutu da kulawa."
Dactor ya yi maganar yana kallon Umar
Umar ya karaso gabansu , kawai Nabila ta fashe da kuka ta rungume Jafar
ita ma baba anje duk tausayin Umar ya rufe ta da ganin ciwon dake tare dashi
"Dan Allah yaya Umar ka je ka huta a halin yanzu kaji abin da doctor ya ce ."
Jafar ya yi maganar Nabila kwance a kirjinsa yana rike da hannun Umar.
Umar ya janye hannunshi tare da fara cewa ," Ni bana jin komai Jafar , yanzu kawai Kalisa ce damuwar , domin karku mance akwai bukatar yi mata aiki tun kafin wannan accident din."
Wasu zafafan hawaye suka zubo masa sannan ya ci gaba da cewa ,"Na ga karfe ya huda gwiwar Kalisa, na ji zafi a zuciyata kuma na bayar ta rasu , yanzu kawai lafiya zamu nema mata. "
Baba anje cikin tashin hankali ta ce "Gaskiya ne , innalillahi wa inna'ilaihir raji'un."
Dactor ya ce "Tom gaskiya ciwonta ni bazan iya dubata ba , ku jira kwana biyu likita yana zuwa." Yana gama maganar ya wuce
Ba zato sukaji Umar ya shako sa ,"Kai wanne mara hankali ne , har gobe zamu jira tana cikin wannan yanayin, ina imaninka da tausayinka ka je fa su."?
Likita da ya ji shakar sa ta yi yawa cikin wahala ya fisge ya hankade Umar "Kai mahaukacin ina ne , bari na kira security su fitar da kai." Dactor din ya karasa maganar ya nufi wajen masu gadi
Umar ya ce , "Mu dauki Kalisa mu koma babban asubitin dactor Aisha hakan zai fi."
Nabila ta yi ajiyar zuciya tana kiran sunan Allah .
Mahmud ne ya fito waje yana duban yanayin anguwar yadda tsarinta kullum yake sake burgeshi , duba ga manyan gidaje da sanyin anguwar
hakan ya sa har yau ya kasa komawa gida, har Aminu ya koma , amma shi ba shi da niyya , amma babban dalilin 'kin komawarsa a kan Zainab ne .
Sake bude idanunshi ya yi yana sake kallon abin da ya hango daga gefe ,
kofar gidan wani mutum malam na lado , wanda har almajirai yana dasu
Mahmud ido ya sake zubawa yana kallon ikon Allah
"Mene Harun yake yi anan".
Mahmud ya tambayi kanshi .
Daga bisani lokacin da Harun ya kula da Mahmud ya yi murmushi ya nufo wajensa.
" Malam Mahmud me ake kuma anan." Harun ya tambaya lokacin da ya karaso gaban shi
Mahmud zuciyarshi wata irin tafasa take masa kamar ya kai masa duka, amma ya daure ya kalle shi yana cewa "Mene ka zo yi a wannan anguwar."?
Harun ya sheke da dariya har da tafawa , sannan ya ce ," Mahmud ni wallahi ma dariya kake bani , to mene ya dameka dani, sannan kuma kar ka yi zaton na bar Zainab, Wallahi ban bar ta ba , kai ne kamin shamaki da ita , amma wallahi kasa a ranka da zarar na zama soja wallahi sai na kawar da kai dan na samu Zainab, ka rubuta ka aji ye ni Harun ni ne ajalinka. "
Ajiyar zuciya Mahmud ya yi yana cewa, " Mu yi mu gani , kar kai tunanin dan ka 'bata Asma'u na ya zamo ina jin tsoron ka......."
Mahmud bai karasa maganar ba Harun ya dakatar dashi da cewa ,"Zan yi wulakanci idan nasa kaki , wallahi Mahmud sai na wulakantaka, zaka gani."
Ya wuce ya yi tafiyarsa
Ran Mahmud ya matukar baci sosai , gida ya shiga cikin bacin rai , ya shiga cikin lambu ya kasa tsaye ya kasa zaune , kawai maganar Harun ce take masa yawo , cikin ranshi yake sake nanata zancen
"Tabbas Harun azzalumi ne , zai aikata duk abin da yake so, yanzu mene mafita."?
Mahmud ya dafa kanshi da ya farai masa ciwo " To ko dai na shigar dashi kara. "?
Ya tambayi kanshi , tare da bada amsa kuma
" Gaskiya 'a'a wannan ba shawara ba ce ."
Ya tsuguna kamar mai shirin yin kuka , sannan ya tashi tsaye yana kallon sararin sama yana ajiyar zuciya.
Da sauri ya dawo da kanshi kasa tare da rudewa da farin cikin shawarar da ta zo masa,
da sauri ya shiga cikin gidan ya wuce d'akinshi ya dauko wayarshi dake caji ya zauna a bakin gado .
Sannan ya fara danna wayar yana cewa, "Hhh kwananka ya kare Harun." A daidai lokacin yana kiran numbar Hauwa 'yar gidan lu'utanal
Kamar jira take karaf ta dauki kiran "Ya Mahmud manyan gari kwana biyu." Ta yi maganar cikin yaren turanci