Sashe 21
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Cikin tashin hankali Uncle yahaya ya zaro idanunsa ya fara magana a yanayin wahala.
"Ya za ai ki barni a nan Fa'iza, ga hadari , ina zan sa kaina , ban zata zaki mini haka ba."
Ajiyar zuciya ta yi sannan ta ce ,"Ka so gaskiya mana Yahaya ina ne zan kai ka , dama kowa yana da kaddarar shi , to ka dauki wannan matsayin abin da ba za ka ta'ba mancewa ba , shi ne Gubar Rayuwarka."
Tana gama magana ta juya da sauri tana kwashe kayanta , sakamakon tsawa da iska da aka fara.
Ba tare da ta ko kalli Yahaya ba tasa kai cikin sauri ta fara tafiya, sakin baki ya yi yana kallonta cikin mamaki ganin cewa da gaske fa tafiya ta yi ta barshi .
Wasu hawaye ne suka zubo masa yayin da ya fara ba za idanu da nufin neman wani ya taimake shi , amma babu wanda ya gani sai wani yaro dake gudu a keke sakamakon yayyafin da aka fara .
"Yanzu ya zan yi , wallahi da nasan abin da zai faru ke nan bazan zo legos ba , basu da mutunci yanzu sai su kone ni a gun nan ." Uncle cikin kuka ya sauke maganar yayin da aka tsuge da ruwan sama .Domin ko ita Fa'iza kafin taje inda zata wannan ruwan ya dake ta , bare Uncle naku dake guri daya.
Yau tun da gari ya waye Maryam take murna da fitar da zasi da Harun , mahaifiyar ta kawai ta sanar wa da wannan labarin , domin ta san malam na lado mahaifinta idan ya ji bazai yadda da wannan shirme ba ,
A tsakanin uwa da 'yah haka sukai maganar su , nan ta ba ta goyon baya tare da umarnin karta jima har Mlm ya tambaye ta.
Doya da kwai take soyawa , daga gefe kuma kana iya hangar wani kunu na gero wanda yasha kayan kamshi.
"Wai Nabila har yanzu ba a gama girki ba yunwa fa nake ji nasan ita ma Baba haka ."
Jafar ya shigo madafa yana wa Nabila maganar cikin mita ,
"Hmmm ." Kawai abin da Nabila ta iya fad'a ke nan
Jafar ba tare da hakan ya dameshi ba ya sake cewa "Kin san dai yau ne Yaya Umar ya ce zai kawo 'kannenshi ko , to ki musu girki dan Allah."
Ta kalleshi tana cewa, "Ban fa mance ba Yaya Jafar."
Ya karaso yana daukar doyar da zummar d'and'anawa.
Bayan Harun ya iso
ba 'ba ta lokaci Maryam ta fita suka tafi
"Ya kamata mu biya ki gaida momy na fa." Harun ya yi maganar yana kallon Maryam
Cikin shagwa'ba Maryam ta kalleshi tana cewa.
Share , like and comment......................
Gubar Rayuwata
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Editing
________________________________________
Page 37 & 38
"Amma gaskiya ba za mu dad'e ba."
Harun wani dad'i yaji ya rufe shi dajin amincewarta , hakan ya sa ya ce ,"Haba sarauniyata yadda ki ke so ai haka za ai besty na." Cikin 'kwarewa da farin ciki ya cigaba da tuki ya nufi gidan da yake kiran gidansu.
Wani gida ne babba suka shiga , Harun yana mata kalamai masu kwantar da zuciya har suka shiga cikin falo.
Maryam dakatawa tai cakk , sakamakon duhun da ta gani a cikin falon , saida Harun ya kunna haske sannan ta ji hankalinta ya kwanta .
"Duk kin wani furgita zauna mana baby bari shaf-shaf na shiga ciki na kira momy."
Harun ya yi maganar yana shige wa ciki.
Nabila kam tasha aiki sosai ta yi girke girke , duk saboda 'kannen Umar da zasu kawo musu ziyara .
Wajen minti biyar Harun ya yi bai fito daga dakin ba ,
Hakan ya sa Maryam ta yi shiru tana sa'ke-sa'ke cikin zuciyar ta
ba ta gama tunanin abin da ya rike su a ciki ba , sai ga Harun ya shigo jikinshi duk a mace ."Mene kuma ya faru."?
Maryam ta yi maganar tare da tashi tsaye
"Ina shiga ciki, na ga momy kwance wallahi hawan jininta ya tashi."
Inji Harun
"Subhanallahi." Maryam ta fad'a
"Amma karki damu , ki shiga ciki ki kula da ita dan Allah, ki kula min da mahaifiyata zan kira likita."
Da sauri Maryam ta fad'a dakin cikin tausayin Harun.
Duhu ta kuma gani cikin dakin , amma ba tare da ta nemi inda glove yake ba , ta nufi gadon wanda tana iya ganin mutum a kudundune a kai.
"Mama , Mama." Tana ta'ba mahaifiyar Harun tana kiran sunanta .
Wani tashin hankali ne ya bigi zuciyar Maryam tare da tsoro , sakamakon yadda taji tulin kayan Harun ne a kan gadon ba wai mahaifiyar shi ba ce .
Da firgici ta tashi tana shirin fitowa taji an rike ta.
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un." Maryam ta fad'a sa'ilin da take da tabbacin Harun ne a gabanta
Dauuuuuu ya kunna glove din dakin yayin da yake rike da hannunta yana dariya.
A yadda mamaki ya kasheta ne ya sa ta kasa cewa komai, zuciyar ta tamkar ta fito musamman jin yadda ya fara magana.
"Ya za ai ki barni a nan Fa'iza, ga hadari , ina zan sa kaina , ban zata zaki mini haka ba."
Ajiyar zuciya ta yi sannan ta ce ,"Ka so gaskiya mana Yahaya ina ne zan kai ka , dama kowa yana da kaddarar shi , to ka dauki wannan matsayin abin da ba za ka ta'ba mancewa ba , shi ne Gubar Rayuwarka."
Tana gama magana ta juya da sauri tana kwashe kayanta , sakamakon tsawa da iska da aka fara.
Ba tare da ta ko kalli Yahaya ba tasa kai cikin sauri ta fara tafiya, sakin baki ya yi yana kallonta cikin mamaki ganin cewa da gaske fa tafiya ta yi ta barshi .
Wasu hawaye ne suka zubo masa yayin da ya fara ba za idanu da nufin neman wani ya taimake shi , amma babu wanda ya gani sai wani yaro dake gudu a keke sakamakon yayyafin da aka fara .
"Yanzu ya zan yi , wallahi da nasan abin da zai faru ke nan bazan zo legos ba , basu da mutunci yanzu sai su kone ni a gun nan ." Uncle cikin kuka ya sauke maganar yayin da aka tsuge da ruwan sama .Domin ko ita Fa'iza kafin taje inda zata wannan ruwan ya dake ta , bare Uncle naku dake guri daya.
Yau tun da gari ya waye Maryam take murna da fitar da zasi da Harun , mahaifiyar ta kawai ta sanar wa da wannan labarin , domin ta san malam na lado mahaifinta idan ya ji bazai yadda da wannan shirme ba ,
A tsakanin uwa da 'yah haka sukai maganar su , nan ta ba ta goyon baya tare da umarnin karta jima har Mlm ya tambaye ta.
Doya da kwai take soyawa , daga gefe kuma kana iya hangar wani kunu na gero wanda yasha kayan kamshi.
"Wai Nabila har yanzu ba a gama girki ba yunwa fa nake ji nasan ita ma Baba haka ."
Jafar ya shigo madafa yana wa Nabila maganar cikin mita ,
"Hmmm ." Kawai abin da Nabila ta iya fad'a ke nan
Jafar ba tare da hakan ya dameshi ba ya sake cewa "Kin san dai yau ne Yaya Umar ya ce zai kawo 'kannenshi ko , to ki musu girki dan Allah."
Ta kalleshi tana cewa, "Ban fa mance ba Yaya Jafar."
Ya karaso yana daukar doyar da zummar d'and'anawa.
Bayan Harun ya iso
ba 'ba ta lokaci Maryam ta fita suka tafi
"Ya kamata mu biya ki gaida momy na fa." Harun ya yi maganar yana kallon Maryam
Cikin shagwa'ba Maryam ta kalleshi tana cewa.
Share , like and comment......................
Gubar Rayuwata
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Editing
________________________________________
Page 37 & 38
"Amma gaskiya ba za mu dad'e ba."
Harun wani dad'i yaji ya rufe shi dajin amincewarta , hakan ya sa ya ce ,"Haba sarauniyata yadda ki ke so ai haka za ai besty na." Cikin 'kwarewa da farin ciki ya cigaba da tuki ya nufi gidan da yake kiran gidansu.
Wani gida ne babba suka shiga , Harun yana mata kalamai masu kwantar da zuciya har suka shiga cikin falo.
Maryam dakatawa tai cakk , sakamakon duhun da ta gani a cikin falon , saida Harun ya kunna haske sannan ta ji hankalinta ya kwanta .
"Duk kin wani furgita zauna mana baby bari shaf-shaf na shiga ciki na kira momy."
Harun ya yi maganar yana shige wa ciki.
Nabila kam tasha aiki sosai ta yi girke girke , duk saboda 'kannen Umar da zasu kawo musu ziyara .
Wajen minti biyar Harun ya yi bai fito daga dakin ba ,
Hakan ya sa Maryam ta yi shiru tana sa'ke-sa'ke cikin zuciyar ta
ba ta gama tunanin abin da ya rike su a ciki ba , sai ga Harun ya shigo jikinshi duk a mace ."Mene kuma ya faru."?
Maryam ta yi maganar tare da tashi tsaye
"Ina shiga ciki, na ga momy kwance wallahi hawan jininta ya tashi."
Inji Harun
"Subhanallahi." Maryam ta fad'a
"Amma karki damu , ki shiga ciki ki kula da ita dan Allah, ki kula min da mahaifiyata zan kira likita."
Da sauri Maryam ta fad'a dakin cikin tausayin Harun.
Duhu ta kuma gani cikin dakin , amma ba tare da ta nemi inda glove yake ba , ta nufi gadon wanda tana iya ganin mutum a kudundune a kai.
"Mama , Mama." Tana ta'ba mahaifiyar Harun tana kiran sunanta .
Wani tashin hankali ne ya bigi zuciyar Maryam tare da tsoro , sakamakon yadda taji tulin kayan Harun ne a kan gadon ba wai mahaifiyar shi ba ce .
Da firgici ta tashi tana shirin fitowa taji an rike ta.
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un." Maryam ta fad'a sa'ilin da take da tabbacin Harun ne a gabanta
Dauuuuuu ya kunna glove din dakin yayin da yake rike da hannunta yana dariya.
A yadda mamaki ya kasheta ne ya sa ta kasa cewa komai, zuciyar ta tamkar ta fito musamman jin yadda ya fara magana.