Sashe 13
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Kalisa ta kira Umar kusa da ita cikin kasa da murya ta ce "Ina matukar kaunar ka."
Koda yaji hakan sai ya ja da baya cikin tausayi da wasu hawaye a cikin idanunsa
Sannan ya dago ya kalleta ya ce "Ni ma ina kaunar ki Kalisa zaki samu lafiya in sha Allah."
Baba anje ta ce "Allah kai ne abin godiya, ka bawa Kalisa lafiya."
Nabila ta amsa da "Amenn." tare da sake cewa "A gaskiya ya kamata a sanar da baba Garba duk ba su san abin dake faruwa ba."
Baba anje ta ce "Gaskiya ne za a sanar dasu."
Sallama da aka yi ne ya sa duk hankulansu ya koma kan kofar
Mahaifan Sahid ne suka shigo
nan aka basu wajen zama zamansu ke nan Kalisa ta fara shure- shure
hakan ya tayar da hankalin kowa saida aka kira dactor Aisha
bayan ta zo ta mata abin da ya dace har ta samu bacci .
Cikin tashin hankali malam Aminu yake tambayar dactor "Yarinya meke damunta haka."
"Baba tana dauke da mummunan ciwo a cikinta, kuma kullum tsanani yake karawa , sannan da fari kasar waje za a kaita , amma a halin yanzu an sami asubitin da za mata aikin , kud'in ne ba su samu ba , kuma ni gaskiya babu abin da zan iya mata kawai aiki take bukata , sannan a gwajin da mukai dalilin accident din nan karfen da ya tsagata ta sami cancer., Amma in sha Allah da zarar an mata aiki komai mai wucewa ne ."
Bayan ta gama ta musu sallama ta fita
Malam Aminu ya ce "In sha Allah."
Umar ya yi ajiyar zuciya yana cewa da Jafar "Mu je a nemi dillalai wannan ba abin zama ba ne Jafar."
Jafar ya ce "To yaya Umar."
Ya tashi cikin kasala da matukar damuwar da yake ciki .
Kafin su kai ga hanyar fita wani saurayi ya shigo cikin d'akin tare da sallama, nan take malam Aminu ya shaida shi ya caf ki sunan shi
"Sani."
Saurayin ya amsa tare da gashshe shi , sannan ya kalli Jafar yana cewa "Don Allah ka yi hakuri tun shekaran jiya MD Sahid ya bani sako a company amma ban kawo ba na mance ."
Ya Ka rasa maganar yana ciro wata takarda da aka sata a gidan sirri ya ba shi .
Ya musu sallama ya fita, kowa mamaki ne ya rufe shi har Kalisa da ba komai take iya ganewa ba.
Bayan ya bud'e takardar ya karanta a zuciyar shi , bayan ya gama ya yi shiru , yayin da ya barsu cikin tashin hankali dalili kuwa sun ga tashin hankali a tare dashi .
Mahaifiyar Sahid ce ta bude baki tana cewa dashi "Yaro mene a ciki me ya aiko haka."
Jafar ya kalli Kalisa cikin tsananin tashin hankali
Yadda Umar abin ya yi masa ciwo kawai ya karbi takardar ya fara karantawa shima a zuciyar sa
Bayan ya gama irin yanayin da ya shiga har yafi na Jafar
"Haba dan Allah wai mene wannan yaron ya rubuto kun yi mana shiru." Cewar mahaifiyar Sahid
Baba anje ta karbi takardar ta bawa Nabila.
"Nabila dan Allah karanta mana sun bar mu a duhu." Baba ta yi maganar cikin damuwa
Idanunta fal da hawaye ta karbi takardar cikin rawar jiki
muryarta na rawa ta fara da cewa "Assalamu alaikum.
Kalisa ku yi hakuri amma a halin yanzu babu wani kud'i da zaku samu duk da naku ne , ba zan baku komai ba balle ku fita kasar waje, a halin yanzu nayi biza ina birt
niya kuma ina da hakki cikin dukiyar Alaji Idris don haka na tafi na ci nawa .Sai wata rana."
Cikin mummunan yanayi Nabila ta aje karatun tare da tashin hankali
"Na yi asarar haihuwa , Sahid mutumin banza ne wallahi, Allah wadaran ka." Mahaifinsa ya yi maganar cikin kuka
lokaci guda kuma ya fad'i kasa
Hankalin matarshi ya tashi , hakan ya sa duk su Umar suka yo kanshi , da gudu Nabila ta fita kiran likita tana zuwa wajen doctor Aisha ta turo wasu nurse zuwa wajen shi .
Bayan sun kanshi daki cikin hanzari ita ma dactor ta shigo dakin domin taimakon gaggawa .
Zuuuu duk suka fita Nabila da Kalisa aka bari a dakin .
Lamarin yana dukansu , a can daga waje kuwa mahaifiyar Sahid kuka take tana cewa, "Wallahi shi ke nan malam mutuwa zai , zuciyar shi ta buga , yaron nan duk irin hidimar da Alaji Idris ya mana bai gani ba , Allah wadaranka Sahid, ka yi asara ka kashe mahaifin ka , wallahi ba zan yafe maka ba."
Baba anje ce ta fara bata hakuri cikin rarrashi "Ki yi hakuri , ba mutuwa zai ba , babu abin da zai same shi ."
Ta fusge jikinta a jikin baba anje tana cewa "Ni nasan halin malam wallahi, shi ke nan malam sai mun taho." Tana gigicewa da kuka
Ran Umar da Jafar duk ba dadi , Allah ne yasan ciwon dake ransu .
Dactor Aisha tana nuna kwarewa , yayin da tai saurin masa abin da yake bukata hakan ya tabbatar mata yana da rai .
Yayin da daya a cikin nurse din ke shiran sa masa ruwa ne , ya fara fisge fisge sai aman jini.
Nan doctor Aisha ta dawo kanshi .
Anan waje kuka kawai matarshi take , cikin kukan ta kira yayan Sahid take fad'a masa malam Aminu ya mutu, cikin tashin hankali ya fanno asubitin.
Zama ta yi dirshen tana ta kukanta , har baba ta gaji da rarrashi .
Sannan sai doctor Aisha ta fito tare da nurse din .
"Ba sai kin fad'a mini ba nasan ya mutu
jeki abin ki." Matarshi ta yi maganar cikin kuka
"Likita ya ake ciki ya jikin nashi ."?
Jafar ya tambaya yayin dasu baba duk suke jiran amsa
likita Aisha ta fara magana" Ku yi hakuri Jafar , mun yi iya yin mu dan cetar ransa , amma Allah ya amshi abinsa."
Dauuuuu suka ji zuciyoyinsu na wani dukan dubu dubu na tsantsar tashin hankali.
Aisha suka wuce suka basu guri .
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un.Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un. Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un"
Baba anje ta fada cikin tashin hankali, su Umar duk sun kasa cewa komai
Ba a dade ba danta Jibrin ya karaso asubitin, shi ma , aiko su Jafar cikin wannan tashin hankali suka bisu kauye har saida aka shiryashi aka sallace shi sannan da aka kaishi suka dawo wajen dare.
Allah ya sa mu dace
Share and comment..........................,..
Gubar Rayuwata
Koda yaji hakan sai ya ja da baya cikin tausayi da wasu hawaye a cikin idanunsa
Sannan ya dago ya kalleta ya ce "Ni ma ina kaunar ki Kalisa zaki samu lafiya in sha Allah."
Baba anje ta ce "Allah kai ne abin godiya, ka bawa Kalisa lafiya."
Nabila ta amsa da "Amenn." tare da sake cewa "A gaskiya ya kamata a sanar da baba Garba duk ba su san abin dake faruwa ba."
Baba anje ta ce "Gaskiya ne za a sanar dasu."
Sallama da aka yi ne ya sa duk hankulansu ya koma kan kofar
Mahaifan Sahid ne suka shigo
nan aka basu wajen zama zamansu ke nan Kalisa ta fara shure- shure
hakan ya tayar da hankalin kowa saida aka kira dactor Aisha
bayan ta zo ta mata abin da ya dace har ta samu bacci .
Cikin tashin hankali malam Aminu yake tambayar dactor "Yarinya meke damunta haka."
"Baba tana dauke da mummunan ciwo a cikinta, kuma kullum tsanani yake karawa , sannan da fari kasar waje za a kaita , amma a halin yanzu an sami asubitin da za mata aikin , kud'in ne ba su samu ba , kuma ni gaskiya babu abin da zan iya mata kawai aiki take bukata , sannan a gwajin da mukai dalilin accident din nan karfen da ya tsagata ta sami cancer., Amma in sha Allah da zarar an mata aiki komai mai wucewa ne ."
Bayan ta gama ta musu sallama ta fita
Malam Aminu ya ce "In sha Allah."
Umar ya yi ajiyar zuciya yana cewa da Jafar "Mu je a nemi dillalai wannan ba abin zama ba ne Jafar."
Jafar ya ce "To yaya Umar."
Ya tashi cikin kasala da matukar damuwar da yake ciki .
Kafin su kai ga hanyar fita wani saurayi ya shigo cikin d'akin tare da sallama, nan take malam Aminu ya shaida shi ya caf ki sunan shi
"Sani."
Saurayin ya amsa tare da gashshe shi , sannan ya kalli Jafar yana cewa "Don Allah ka yi hakuri tun shekaran jiya MD Sahid ya bani sako a company amma ban kawo ba na mance ."
Ya Ka rasa maganar yana ciro wata takarda da aka sata a gidan sirri ya ba shi .
Ya musu sallama ya fita, kowa mamaki ne ya rufe shi har Kalisa da ba komai take iya ganewa ba.
Bayan ya bud'e takardar ya karanta a zuciyar shi , bayan ya gama ya yi shiru , yayin da ya barsu cikin tashin hankali dalili kuwa sun ga tashin hankali a tare dashi .
Mahaifiyar Sahid ce ta bude baki tana cewa dashi "Yaro mene a ciki me ya aiko haka."
Jafar ya kalli Kalisa cikin tsananin tashin hankali
Yadda Umar abin ya yi masa ciwo kawai ya karbi takardar ya fara karantawa shima a zuciyar sa
Bayan ya gama irin yanayin da ya shiga har yafi na Jafar
"Haba dan Allah wai mene wannan yaron ya rubuto kun yi mana shiru." Cewar mahaifiyar Sahid
Baba anje ta karbi takardar ta bawa Nabila.
"Nabila dan Allah karanta mana sun bar mu a duhu." Baba ta yi maganar cikin damuwa
Idanunta fal da hawaye ta karbi takardar cikin rawar jiki
muryarta na rawa ta fara da cewa "Assalamu alaikum.
Kalisa ku yi hakuri amma a halin yanzu babu wani kud'i da zaku samu duk da naku ne , ba zan baku komai ba balle ku fita kasar waje, a halin yanzu nayi biza ina birt
niya kuma ina da hakki cikin dukiyar Alaji Idris don haka na tafi na ci nawa .Sai wata rana."
Cikin mummunan yanayi Nabila ta aje karatun tare da tashin hankali
"Na yi asarar haihuwa , Sahid mutumin banza ne wallahi, Allah wadaran ka." Mahaifinsa ya yi maganar cikin kuka
lokaci guda kuma ya fad'i kasa
Hankalin matarshi ya tashi , hakan ya sa duk su Umar suka yo kanshi , da gudu Nabila ta fita kiran likita tana zuwa wajen doctor Aisha ta turo wasu nurse zuwa wajen shi .
Bayan sun kanshi daki cikin hanzari ita ma dactor ta shigo dakin domin taimakon gaggawa .
Zuuuu duk suka fita Nabila da Kalisa aka bari a dakin .
Lamarin yana dukansu , a can daga waje kuwa mahaifiyar Sahid kuka take tana cewa, "Wallahi shi ke nan malam mutuwa zai , zuciyar shi ta buga , yaron nan duk irin hidimar da Alaji Idris ya mana bai gani ba , Allah wadaranka Sahid, ka yi asara ka kashe mahaifin ka , wallahi ba zan yafe maka ba."
Baba anje ce ta fara bata hakuri cikin rarrashi "Ki yi hakuri , ba mutuwa zai ba , babu abin da zai same shi ."
Ta fusge jikinta a jikin baba anje tana cewa "Ni nasan halin malam wallahi, shi ke nan malam sai mun taho." Tana gigicewa da kuka
Ran Umar da Jafar duk ba dadi , Allah ne yasan ciwon dake ransu .
Dactor Aisha tana nuna kwarewa , yayin da tai saurin masa abin da yake bukata hakan ya tabbatar mata yana da rai .
Yayin da daya a cikin nurse din ke shiran sa masa ruwa ne , ya fara fisge fisge sai aman jini.
Nan doctor Aisha ta dawo kanshi .
Anan waje kuka kawai matarshi take , cikin kukan ta kira yayan Sahid take fad'a masa malam Aminu ya mutu, cikin tashin hankali ya fanno asubitin.
Zama ta yi dirshen tana ta kukanta , har baba ta gaji da rarrashi .
Sannan sai doctor Aisha ta fito tare da nurse din .
"Ba sai kin fad'a mini ba nasan ya mutu
jeki abin ki." Matarshi ta yi maganar cikin kuka
"Likita ya ake ciki ya jikin nashi ."?
Jafar ya tambaya yayin dasu baba duk suke jiran amsa
likita Aisha ta fara magana" Ku yi hakuri Jafar , mun yi iya yin mu dan cetar ransa , amma Allah ya amshi abinsa."
Dauuuuu suka ji zuciyoyinsu na wani dukan dubu dubu na tsantsar tashin hankali.
Aisha suka wuce suka basu guri .
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un.Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un. Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un"
Baba anje ta fada cikin tashin hankali, su Umar duk sun kasa cewa komai
Ba a dade ba danta Jibrin ya karaso asubitin, shi ma , aiko su Jafar cikin wannan tashin hankali suka bisu kauye har saida aka shiryashi aka sallace shi sannan da aka kaishi suka dawo wajen dare.
Allah ya sa mu dace
Share and comment..........................,..
Gubar Rayuwata