← Book details Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 27

Sashe 22

Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

"Kin ga yadda shiri na ya yi koh. Ga ki gare ni yau Maryam zaki ga irin san da nake muki , babu kowa a gidan nan daga ni sai ke yawan."
Ya karasa maganar yana fincike mayafin dake jikinta .
"Inna'ilaihir wa inna'ilaihir raji'un Harun , kaji tsoron Allah, na roke ka karka rabani da mutunci na , dan Allah." Cikin matukar kuka da firgici Maryam ta yi magana.
Dariya ya yi yana cewa ,"Haba Maryam, karki zama yarinya mana , wallahi tun lokacin da nake zuwa wajenki Wannan ranar nake jira , ban samu Zainab ba , domin na so mu shiga irin wannan yanayin da ita ,amma shegen yayan ta Mahmud ya hana."....
"Dan Allah Harun kar ka cutar dani, wallahi bazan jure ba."
Ya tunkud'eta ta fad'a kan gadon , haka har mai faruwa ta faru .
Sannan Harun yaji dadin rayuwar shi .
Bayansu su Umar sun shigo suka zauna a falo nan suka fara hira dasu Jafar da baba anje
Ya yin da Nabila ta fito daga wanka tana shiryawa.
Da siririyar murya kanwar Umar Salma , wacce take kusa da yayanta Nasir ta ce ,"Wai ina Nabilan ne to."?
Jafar ya ce ,"Ta na zuwa yanzu. "
Nabila ta karaso cikin falon sanye da wata doguwar riga abaya , wacce taji ado ga launi mai matukar kyau.
Tun daga 'bullowarta Nasir ya kasa jire idanunshi a kanta , har ta karaso ta zauna
"Ya ya Umar har kun zo."? Nabila ta yi maganar da Umar yayin da kuma ta ke kallon Nasir da Salma
" Kanwata mun iso, yau dai ga salma nan." Ya yi maganar yana nunawa Nabila kanwar shi .
Murmushi Nabila ta yi tana cewa, "Eh yayana ka cika alkawari kuma naji dadi."
Nasir ne ya 'ba ta rai yana kallon Umar da cewa ,"Haba Yaya Umar to ni ba za a gabatar dani ba."
Jin hakan ya sa kowa ya kalleshi suna masa Murmushi.
Umar tsaki ya yi yana cewa, "Nabila wannan matumburin kanina ne sunan shi Nasir."
"Haba Yaya Umar matumburi kuma." Nasir yayi maganar yana kallon shi .
Dariya suka kwashe da ita baki dayansu har da Umar yayin da ya ce ,"Ai Nasir din ne ya cika zance wallahi. "
Nasir ya kalli Nabila yana cewa ,"Baki gabatar mana da kanki ba sister. "
Cikin haushi Umar ya Had'e rai yana cewa, "Kun ji ba , baka ji an ce Nabila sunanta ba ,banan surutu bama kasan mene za ka na tambaya ba."
Dariya suka kuma yi wacce tafi ta d'azu , har ita Nabilan ya yin da Nasir yake kallon yadda dariya take mata kyau.
Sannan ta tashi ta nufi dakin girki domin kawo musu abinci , Nasir harda lekenta .
Lomar farko ta Nasir ya ce ,"Gaskiya Nabila kin iya girki sosai , sai ka ce a Australia. "
Wata harara Umar ya watsa masa tare da cewa ,"Su Australian girki suka iya? dan Allah ka yi hakuri ka yi shiru haba."
Dariya suka sake yi a karo na ba adadi
haka suka gama cin abincin cikin farin ciki da walwala .
Bayan su kammala suka tashi tafiya, nan ne Nasir ya karbi number Nabila sannan suka yi sallama. Sun matukar jin dadin wannan ziyara baki dayansu."
Fa'iza a gidan kawarta ta samu guri , inda ta tabbatar wa da kawarta zuwa gobe zata koma garinsu .
Tana tsakar gida a zaune ta yi tagumi , a lokacin ne wannan kawarta ta ta fito daga daki .
yadda ta ga Fa'iza ta yi tagumi tana kallon taurarin dake sama ya sa
kawarta cewa ,"Haba Fa'iza lafiya , kin zauna a farin wata kuma kina kallon sama ."
Fa'iza ta yi ajiyar zuciya tare da cire hannu daga tagumin da ta yi
"Ki dena damun kanki fa dan Allah." Cewar kawarta
Ajiyar zuciya Fa'iza ta kuma yi tana cewa, "A kwai abin da ban fad'a miki ba kawata, kuma nasan yanzu duk wannan ruwan saman da akai ga dare yana kwance a wajen nan."
"Topha waye ke nan." Cewar kawarta
Fa'iza ta fara bata labarin halin da Uncle yahaya yake ciki da kuma yadda ta baro shi .
"To yanzu ya kike so a yi masa Fa'iza, ki rabu dashi kawai , idan ya mutu Allah ya jikanshi , kema shawara nake baki tun kina da lokaci ki tuba wallahi, domin ya zama izina gare ki ga yadda Yahayan nan ya samu kanshi , ki manta da komai ki koma ga Allah domin shi mai gafara ne , kuma ba damuwarki ba ce idan Yahaya ya mutu , nan zasu sa wuta su kona shi , idan kuma yana raye to rayuwa ce zai gani ya more duk yadda Allah ya yi daidai ne ."
Yanayin zazzakar muryarta ya sa Fa'iza ta gamsu da zancen kawartata .
Fa'iza ta ce ,"Haka ne kawata , in sha Allah bana komawa karuwanci domin gobe ma yobe zan koma, Allah ya yafe mana. "
Kawarta ta ce ,"Yawwa Fa'iza ki je kawai ki kwanta saida safe. " Fa'iza ta shige dakinta ta rufo ta kwanta .
Washe Gari
Hauwa ce zaune tana karyawa a lokacin mahaifin ta lu'utanal ya shigo
"Dady har yau baka samu time ba ni gaskiya yau zanje na ga Surayya."
Kai tsaye Hauwa ta yi maganar
Murmushi ya yi yana cewa, "Ehh gaskiya ne , ban samu lokacin ba kije abinki ki gaida mini da ambassador."
"Thanks dady."
Maryam babu wanda ta sanarwa da abin da ya faru , gashi tana cikin halin rashin lafiya , tun da Harun ya samu abin da yake so bai kuma waiwayarta ba , Allah sarki.
Tuni ya barta har ya samu wata , wacce yake da irin wannan nufi a gunta , amma abun da yake ba shi tsoro yadda babanta yake babban mutum ambassador,
Amma sai ya samu salama da ya yi tunanin ya ta'ba'yar malami ma ya zauna lafiya, bare yaran manya da suke chilling suke shoshalewa tabbas cikin sauki zai samu abin da yake so .
Umar ne bayan ya amsa wata waya da akai kiranshi ya tashi da sauri ya fita , a karshe gudu yasa kamar mai shirin tashi sama , yana sake nanata sakon da aka isar masa cikin wayar .
Jafar da Nabila ne zaune , sai baba anje , bayan sun gama karyawa
"Gaba na fad'uwa yake Yaya Jafar." Nabila ta yi maganar cikin damuwa.
Share and comment...................
Gubar Rayuwata
By

Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
Chapter 22 · 0% Book details