Sashe 14
Gubar Rayuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
___________________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*
__________
_________
__________
_________
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_
<><><
><><><>
<><><>
<><><><>
<><><><><>
<><>
Page 25 & 26
Duk da Kalisa ba ta ce komai ba amma tabbas zuciyar ta babu dadi tun d'azu take kuka , anata rarrashinta amma ta kasa iya dena kuka .
A washe gari bayan sun sayar da gidan , dactor Aisha take tabbatar musu dole Kalisa a fitar da ita domin da tun da fari a matakin ciwon na farko an san abinyi shi ne za a mata aikin anan.
Haka dai basu ji dadi ba , amma gwarin gwiwar da suke samu Kalisa zata samu lafiya ,
Duk yau wani farin ciki suke yi domin zuwa gobe Kalisa za a fitar da ita India
wajejen yamma kuwa sai ga Baba Garba , aiko nan ya yi ta musu fad'a a kan rashin sanar dashi da wuri .
Jibril magana d babarshi a kan Sahid
Bayan magariba ta dauko kai Baba anje da farin cikinta ta ce "Nabila ta shi ki tafi gida ki shiryawa muku duk kayan da zaku bukata domin kinsan jirgi ba ya jira ."
Nabila ta ce "To baba bari naje gidan , su ka yi sallama tafi.
Yau dai a 'kallah duk sun sami farin ciki , domin yadda suka saki fuskokinsu abin farin ciki ne , sai dai ma mutuwar mlm Aminu ce duk wani bacin ran.
10:02 na dare
Baba anje ta fad'a a ranta " Nabila dai gida zata kwana ke nan , to Allah ya sa ta zo da wuri , ai Jafar ma na gidan shi da Garba ."
Jafar ma yana komawa gida babu wata-wata ya kwanta domin ya matukar gajiya .
Washe gari da safe
Laila ta samu lafiya har barrister Adam ya sama mata makaranta ta ci gaba , haka ta ci gaba da Rayuwar ta cikin aminci da kaunar iyayenta .
A 'bangaren Uncle Yahaya kuwa shiri yake zai koma Lagos wajen Fa'iza, domin ya sanar da ita halin da yake ciki , hakan ya sa ta turo masa kud'i domin ya koma kusa da ita , tun da dai yanzu ba kowa yake dashi ba .
Aiko yau din nan zan tafi lagos
"Karfe nawa jirgin zai ta shi." ? Baba ta tambaya
"11."
Jafar ya bata amsa a gajarce
"To amma Nabila ina ta shiga ne , ko abinci take yi ne , tun jiya ban zata zata kwana a gida ba sai ga shi ta kwana kuma har karfe 9 shiru."
Baba anje ke nan
Jafar ya ce "Ai na yi zaton ma anan ta kwana domin jiya banganta ba ."
Darammm a zuciyar Kalisa da Baba anje
Kowa shiru ya yi yana sake-sake cikin ranshi , Jafar ya ciro wayarsa a aljihu ya ya nufi numbar Nabila domin kira,
wayar ko shiga ba tai ba balle ya sa ran jinta
Jin sallama duk ya sa hankalinsu ya koma kofar shigowa
"Assalamu alaikum".
Suka amsa sallamar tare da wani yanayi a cikin furkarsu
Baba garba ne ya shigo , shi ma yadda ya gansu ne ya sashi tambaya
" Ya haka , ko lafiya na ganku haka."? Ya karasa maganar ya na zuzzura musu idanu,
"Nabila ce ba a ganta ba."
Jafar ya ba shi amsa
"Subhanallahi kamar ya kuma Jafar."?
Tun kafin Baba Garba ya yi magana , Umar ya shigo yana tambaya
Duk shiru sukai kawai suna jin abin a ransu,
" Bata kwana a gidan ba ne ko ya". ?
Baba Garba ya yi maganar yayin da ya katse musu sake -saken su."
A wannan karon ma dai Jafar ne ya fara magana "Ni wallahi ban sani ba , jiya na gaji hakan ya sa ina shiga gida na kwanta."
"Kuma ba ta makota."? Baba anje ta jefawa Jafar tambaya
Jafar cikin takaicin yadda kowa shi yake tuhuma ya fara cewa " Ba mu tabbatar ba kawai mu fita mu duba." Ya karasa maganar tare da fita bai jira kowa ba .
A jiyar zuciya Kalisa tai , ba tare da ta ce komai ba
amma kana iya hangar tashin hankalinta a furkarta .
Bayan Uncle Yahaya ya sauka a legos, yabi wannan adireshi na Fa'iza ,wato inda gidanta yake , babu jan lokaci ya sami gidan
"Assalamu alaikum."
Uncle Yahaya ya yi sallamar a gidan Fa'iza tare da takatsan-tsan din kamar ba gidan ba ne , ba tare da ya kuma sallama ba ya ringa duban gidan yana lekawa
Jin muryarta ne ya tabbatar masa tabbas ya zo gidan masoyiya
"Haba baby, ni daya ce fa a gidan , daga ni sai kai , sannu da zuwa."
Ta karasa maganar yayin data aje buta tare da jan bandakin data fito .
Ajiyar zuciyar farin ciki ya yi yana gyarawa jakar kafadarsa zama yana cewa "Ga kyakykyawata farin cikina yau a gabana."
Wani irin kallo Fa'iza tai masa tare da kashe ido , lokaci guda kuma tana kai hannu tana karbar jakar tashi."
Suka nufi daki suna shiga dakin wayarta ta fara ruri , tabbas tasan Abdul ne , hakan ya sa bata bi ta kanta ba ,
shi ma Yahaya ko tayin daukar kiran bai mata ba , domin ga dukkan alamu bai ma jiba , saboda wani shegen kallo da yake binta dashi .
To ga dai Uncle Yahaya a lagos
Ko ta ina zai fara , kuma ya zai rayu
Ga kuma bangaren Kalisa, har yanzu babu labarin Nabila, da Sahid, ga ciwonta kullum abin tafiya yake , ko Kalisa zata sami lafiya?
Ga kuma bangaren Zainab da Mahmud, ga mutumin ku Harun .
Tofa duk ba za mu ji yadda abin zai kasance ba ,sai mun had'u a
A tare da ni Fatima Abdallaah kano
Wato Auta ga marubuta
Mu had'u a kashi na biyu karku mance fa
Share and comment..................................
Gubar Rayuwata
By
Fatima Abdallaah kano
. (Autar marubuta)
______________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*
__________
_________
__________
_________
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_
<><><
><><><>
<><><>
<><><><>
<><><><><>
<><>
Page 27 & 28
Duk hankalinsu ya gama tashi matukar gaske, har magariba ta yi amma babu labarin Nabila , da tananan sun tabbatar yanzu Kalisa tana India, amma duk inda ya dace a duba kuma a tambaya an yi , sai dai babu wani cigaba.
Allah ya kawo sauki da mafita , haka rayuwar take, kowa da kalar tashi kaddarar.
Washe gari
Jibril ne zaune kusa da mahaifiyar shi yana rarrashinta , tun da garin Allah ya waye take kuka
Cikin tausayin mahaifiyar tashi Jibril ya ce "Babata dan Allah ki jure wannan jarabawar , wallahi komai mai wucewa ne ."
Cikin rashin gwarin gwiwa ya karasa maganar
Cikin kuka tana face majina tana gogewa da zaninta ta ce "Wallahi Jibril kaninka ya yi asara duniya d lahira , domin ba zan yafe masa, ya je indai duniya ce , wanda ba su zo ba ma jiransu take , sai ta sashi kukan da babu hankicin da zai share masa."
Ta kuma fashewa da kuka
Jibril duk ya kasa cewa komai domin zuciyar shi shi daya yasan zugin da take masa .
Kasar waje
Sahid ne ya fito daga asubitin kashi yana dingishi , guri ya samu ya zauna
iska mai dadin gaske ce ke kai wa tana dawowa , ga duk kan alamu yana jin dadinta fiye da su mazauna kasar
Lokaci guda kuma ya hade rai yana magana shi daya , yayin da ya hango wani gurgu bisa keke ana turashi
" Allah ka raba mu da wannan masifar kawai a yankewa mutum kafarsa ,
wannan asubitin za su min komai ba sai na koma Nigeria ba , Allah sarki babata da na ce ciwo zata daukon magani ,
ni da na koma Nigeria sai na yi aure na haihu da baturiya ,daga nan ma Pakistan zan wuce."
Ya aje maganar yana kallon ambulance din da suka shigo asubitin.
A d'azu jikin Kalisa ya rikice sosai da sosai , nan hankalinsu ya tashi
sun yi kokarin fitar da ita , amma Kalisa ta ce bazata bar kasar nan ba ba tare da tasan halin da kanwarta ke ciki ba .
Duk da an sanar da 'yan sanda amma har yanzu ba ta sauya zani ba
Fitar kannen Umar ke nan daga asubitin , su biyu mace dana miji
macen tana kuka da wannan yanayi data gansu a ciki. To ya za ai da lamarin ubangiji
Umar ya matukar ramewa sosai , su baba anje ma ba a cewa komai ga su Jafar da Garba , abin dai sai wanda ya gani.
Jingum suka yi duk din su a dakin
wayar Jafar da take ruri ne kawai ya sa ake jin wani sauti
da kasala ya cirota a aljihunsa tare d amsa kiran yana karawa a kunne .
Koda jin wata kakkausar murya ce ke magana hakan ya sa ya tashi tsaye , yayin da duk hankulansu suka dawo wajenshi
Da alamar magana da kai Umar yake tambaya ko lafiya, hakan ya sa Jafar ya sata a sautin da kowa kan iya jin abin da ake cewa
"Na ce kai ne Jafar."
Aka fad'a cikin muryar rashin girmamawa, cikin faduwar gaba Jafar ya amsa da shi ne
Aka ci gaba da magana kamar haka "To wallahi mu harkar mu babu karanta , da zarar mun baka lokaci ba kai amfani da shi ba komai na faruwa, mu ne muka dauke kanwarka , kud'in fansa muke so , idan kuma ka shigo da 'yan sanda cikin kasuwancin mu to ku shirya jana'izarta."
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)
___________________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*
__________
_________
__________
_________
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_
<><><
><><><>
<><><>
<><><><>
<><><><><>
<><>
Page 25 & 26
Duk da Kalisa ba ta ce komai ba amma tabbas zuciyar ta babu dadi tun d'azu take kuka , anata rarrashinta amma ta kasa iya dena kuka .
A washe gari bayan sun sayar da gidan , dactor Aisha take tabbatar musu dole Kalisa a fitar da ita domin da tun da fari a matakin ciwon na farko an san abinyi shi ne za a mata aikin anan.
Haka dai basu ji dadi ba , amma gwarin gwiwar da suke samu Kalisa zata samu lafiya ,
Duk yau wani farin ciki suke yi domin zuwa gobe Kalisa za a fitar da ita India
wajejen yamma kuwa sai ga Baba Garba , aiko nan ya yi ta musu fad'a a kan rashin sanar dashi da wuri .
Jibril magana d babarshi a kan Sahid
Bayan magariba ta dauko kai Baba anje da farin cikinta ta ce "Nabila ta shi ki tafi gida ki shiryawa muku duk kayan da zaku bukata domin kinsan jirgi ba ya jira ."
Nabila ta ce "To baba bari naje gidan , su ka yi sallama tafi.
Yau dai a 'kallah duk sun sami farin ciki , domin yadda suka saki fuskokinsu abin farin ciki ne , sai dai ma mutuwar mlm Aminu ce duk wani bacin ran.
10:02 na dare
Baba anje ta fad'a a ranta " Nabila dai gida zata kwana ke nan , to Allah ya sa ta zo da wuri , ai Jafar ma na gidan shi da Garba ."
Jafar ma yana komawa gida babu wata-wata ya kwanta domin ya matukar gajiya .
Washe gari da safe
Laila ta samu lafiya har barrister Adam ya sama mata makaranta ta ci gaba , haka ta ci gaba da Rayuwar ta cikin aminci da kaunar iyayenta .
A 'bangaren Uncle Yahaya kuwa shiri yake zai koma Lagos wajen Fa'iza, domin ya sanar da ita halin da yake ciki , hakan ya sa ta turo masa kud'i domin ya koma kusa da ita , tun da dai yanzu ba kowa yake dashi ba .
Aiko yau din nan zan tafi lagos
"Karfe nawa jirgin zai ta shi." ? Baba ta tambaya
"11."
Jafar ya bata amsa a gajarce
"To amma Nabila ina ta shiga ne , ko abinci take yi ne , tun jiya ban zata zata kwana a gida ba sai ga shi ta kwana kuma har karfe 9 shiru."
Baba anje ke nan
Jafar ya ce "Ai na yi zaton ma anan ta kwana domin jiya banganta ba ."
Darammm a zuciyar Kalisa da Baba anje
Kowa shiru ya yi yana sake-sake cikin ranshi , Jafar ya ciro wayarsa a aljihu ya ya nufi numbar Nabila domin kira,
wayar ko shiga ba tai ba balle ya sa ran jinta
Jin sallama duk ya sa hankalinsu ya koma kofar shigowa
"Assalamu alaikum".
Suka amsa sallamar tare da wani yanayi a cikin furkarsu
Baba garba ne ya shigo , shi ma yadda ya gansu ne ya sashi tambaya
" Ya haka , ko lafiya na ganku haka."? Ya karasa maganar ya na zuzzura musu idanu,
"Nabila ce ba a ganta ba."
Jafar ya ba shi amsa
"Subhanallahi kamar ya kuma Jafar."?
Tun kafin Baba Garba ya yi magana , Umar ya shigo yana tambaya
Duk shiru sukai kawai suna jin abin a ransu,
" Bata kwana a gidan ba ne ko ya". ?
Baba Garba ya yi maganar yayin da ya katse musu sake -saken su."
A wannan karon ma dai Jafar ne ya fara magana "Ni wallahi ban sani ba , jiya na gaji hakan ya sa ina shiga gida na kwanta."
"Kuma ba ta makota."? Baba anje ta jefawa Jafar tambaya
Jafar cikin takaicin yadda kowa shi yake tuhuma ya fara cewa " Ba mu tabbatar ba kawai mu fita mu duba." Ya karasa maganar tare da fita bai jira kowa ba .
A jiyar zuciya Kalisa tai , ba tare da ta ce komai ba
amma kana iya hangar tashin hankalinta a furkarta .
Bayan Uncle Yahaya ya sauka a legos, yabi wannan adireshi na Fa'iza ,wato inda gidanta yake , babu jan lokaci ya sami gidan
"Assalamu alaikum."
Uncle Yahaya ya yi sallamar a gidan Fa'iza tare da takatsan-tsan din kamar ba gidan ba ne , ba tare da ya kuma sallama ba ya ringa duban gidan yana lekawa
Jin muryarta ne ya tabbatar masa tabbas ya zo gidan masoyiya
"Haba baby, ni daya ce fa a gidan , daga ni sai kai , sannu da zuwa."
Ta karasa maganar yayin data aje buta tare da jan bandakin data fito .
Ajiyar zuciyar farin ciki ya yi yana gyarawa jakar kafadarsa zama yana cewa "Ga kyakykyawata farin cikina yau a gabana."
Wani irin kallo Fa'iza tai masa tare da kashe ido , lokaci guda kuma tana kai hannu tana karbar jakar tashi."
Suka nufi daki suna shiga dakin wayarta ta fara ruri , tabbas tasan Abdul ne , hakan ya sa bata bi ta kanta ba ,
shi ma Yahaya ko tayin daukar kiran bai mata ba , domin ga dukkan alamu bai ma jiba , saboda wani shegen kallo da yake binta dashi .
To ga dai Uncle Yahaya a lagos
Ko ta ina zai fara , kuma ya zai rayu
Ga kuma bangaren Kalisa, har yanzu babu labarin Nabila, da Sahid, ga ciwonta kullum abin tafiya yake , ko Kalisa zata sami lafiya?
Ga kuma bangaren Zainab da Mahmud, ga mutumin ku Harun .
Tofa duk ba za mu ji yadda abin zai kasance ba ,sai mun had'u a
A tare da ni Fatima Abdallaah kano
Wato Auta ga marubuta
Mu had'u a kashi na biyu karku mance fa
Share and comment..................................
Gubar Rayuwata
By
Fatima Abdallaah kano
. (Autar marubuta)
______________________________________
*AUTAR MARUBUTA CE*
__________
_________
__________
_________
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_
<><><
><><><>
<><><>
<><><><>
<><><><><>
<><>
Page 27 & 28
Duk hankalinsu ya gama tashi matukar gaske, har magariba ta yi amma babu labarin Nabila , da tananan sun tabbatar yanzu Kalisa tana India, amma duk inda ya dace a duba kuma a tambaya an yi , sai dai babu wani cigaba.
Allah ya kawo sauki da mafita , haka rayuwar take, kowa da kalar tashi kaddarar.
Washe gari
Jibril ne zaune kusa da mahaifiyar shi yana rarrashinta , tun da garin Allah ya waye take kuka
Cikin tausayin mahaifiyar tashi Jibril ya ce "Babata dan Allah ki jure wannan jarabawar , wallahi komai mai wucewa ne ."
Cikin rashin gwarin gwiwa ya karasa maganar
Cikin kuka tana face majina tana gogewa da zaninta ta ce "Wallahi Jibril kaninka ya yi asara duniya d lahira , domin ba zan yafe masa, ya je indai duniya ce , wanda ba su zo ba ma jiransu take , sai ta sashi kukan da babu hankicin da zai share masa."
Ta kuma fashewa da kuka
Jibril duk ya kasa cewa komai domin zuciyar shi shi daya yasan zugin da take masa .
Kasar waje
Sahid ne ya fito daga asubitin kashi yana dingishi , guri ya samu ya zauna
iska mai dadin gaske ce ke kai wa tana dawowa , ga duk kan alamu yana jin dadinta fiye da su mazauna kasar
Lokaci guda kuma ya hade rai yana magana shi daya , yayin da ya hango wani gurgu bisa keke ana turashi
" Allah ka raba mu da wannan masifar kawai a yankewa mutum kafarsa ,
wannan asubitin za su min komai ba sai na koma Nigeria ba , Allah sarki babata da na ce ciwo zata daukon magani ,
ni da na koma Nigeria sai na yi aure na haihu da baturiya ,daga nan ma Pakistan zan wuce."
Ya aje maganar yana kallon ambulance din da suka shigo asubitin.
A d'azu jikin Kalisa ya rikice sosai da sosai , nan hankalinsu ya tashi
sun yi kokarin fitar da ita , amma Kalisa ta ce bazata bar kasar nan ba ba tare da tasan halin da kanwarta ke ciki ba .
Duk da an sanar da 'yan sanda amma har yanzu ba ta sauya zani ba
Fitar kannen Umar ke nan daga asubitin , su biyu mace dana miji
macen tana kuka da wannan yanayi data gansu a ciki. To ya za ai da lamarin ubangiji
Umar ya matukar ramewa sosai , su baba anje ma ba a cewa komai ga su Jafar da Garba , abin dai sai wanda ya gani.
Jingum suka yi duk din su a dakin
wayar Jafar da take ruri ne kawai ya sa ake jin wani sauti
da kasala ya cirota a aljihunsa tare d amsa kiran yana karawa a kunne .
Koda jin wata kakkausar murya ce ke magana hakan ya sa ya tashi tsaye , yayin da duk hankulansu suka dawo wajenshi
Da alamar magana da kai Umar yake tambaya ko lafiya, hakan ya sa Jafar ya sata a sautin da kowa kan iya jin abin da ake cewa
"Na ce kai ne Jafar."
Aka fad'a cikin muryar rashin girmamawa, cikin faduwar gaba Jafar ya amsa da shi ne
Aka ci gaba da magana kamar haka "To wallahi mu harkar mu babu karanta , da zarar mun baka lokaci ba kai amfani da shi ba komai na faruwa, mu ne muka dauke kanwarka , kud'in fansa muke so , idan kuma ka shigo da 'yan sanda cikin kasuwancin mu to ku shirya jana'izarta."