← Book details Gargadan So Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 123

Sashe 9

Gargadan So Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

EPISODE Daki ne kwara daya yanada girma ga window da akasa curtains mai kyau pink dakeda zanen flower dayawa, katifa ne number one mai tudu akasa shima an shimfidamai pink bedsheet yayi kyau sosai, ga dan table data jera Kayan shafa da kwalliya gwanin ban sha’awa dasu turaruka da stool na zama awajen, sai kuma dan wardrobe mai 2 rack wanda daga gani kayanta ne aciki sai kuma gefe daya da keken dinki ne mai bala’in kyau ga basket a gefen keken dinkin wanda da alamu abubuwan dinki ne aciki, tsakiyan dakin akwai carpet mai laushi bakin gado, Hawwa tawuce dasauri tazauna tana kokarin danne hawayenta itakuma Ni’ima ta tsaya jawo net na kofan tasa sakata tana sauke labule sannan tajuyo ta taho bakin gadon da sauri tazauna kusada Hawwa dake bude jakanta tana kokarin ciro wayanta tana kallonta, ahankali takai hannunta zata tabata sai kawai Hawwa ta rungumeta da sauri tareda fashewa da kuka, wani irin tsinkewa zuciyan Ni’ima yayi sabida da wuya Hawwa ke kuka, it’s being years bataga kukan Hawwa ba, tariga takoyama kanta dauriya dan taga rayuwa, banda haka duk duniya ita kadai ke ganin kukan Hawwa wanda idan tayishi kasan ta tara abu dayawa aranta ne, cikeda damuwa Ni’ima tai patting back dinta tace “wlh Hawwa idan kina kuka sani kike inaji kaman tawa takare aduniya cus you are the strongest woman dana sani aduniya, please kidena minding maganganun Baba inda sabo yaci ace kin saba, wlh harda tsufa ke damunshi cus make it make sense for me idan kika barsu haka wazai iya ciyarwa agidan nan? Dagashi har matar nasa da yaransa wazai ciyar dasu? Ba aikin dayake zagi kullum ke ciyar dasu ba? Kece cinsu, shansu, suturansu, da kudinki aka aurar da yaransa hudu, kene school din Aminu, kene school din Maryama, still kece magungunan sa, I’m sorry to say baida aiki sai zaman kofar gida baya taba fahimtanki, an gayamai kene kika hana kanki aure? Ni wlh iyayen dake takurama yaransu kan zancen aure na bani mamaki aduniya bayan sune yakamata su dinga bawa yaran nasu karfin guiwa suna gayamusu cewa aure lokaci ne, suna nuna musu su yarda da kaddaransu, duk sanda auren yazo za’ayi saidai su tasa yaran agaba suna kyaransu, ana gayama yara bakaken magana, ana gwanzaban su da addabansu da aure, so yake kije titi ki kama hannu kowani d’a namiji kika gani kikawoshi gidan nan ya aureki? Bakida samari so yake kije kijawo wani karfi da yaji yazo ya aureki? Maza nawa sukazo gidan nan neman aurenki dazaran an tsaida magana su gudu so yake kije ki damkosu karfi da yaji suzo su aureki? Kidnapping na maza yakeso ki fara? Besides duka duka you’re 29 why is he rushing you when bawai kinkai 50yrs baki auren bane? Wlh banso na amsa Baba ne I know it will look disrespectful saisa kikaga natashi najaki munbar masa wajen but I can’t take it idan yana miki irin maganganun nan, when he should be thanking God Allah yabashi diya nutsassiya, kamila, educated and smart dake aiki da ake biyanta da kyau ta rike masa gida tasa yaransa a school, haba, menene aure? Aure lokaci ne, kuma inaji ajikina wani jinkirin alkhairi ne, don’t worry everything is going to be okay I’m here for you no matter what and yarana yaranki ne so kinada yara kinji yadena cewa bakida yara you actually have Yasmeen and Yaseer yaran Hawwa ne” tai maganan tana ciro Hawwa daga jikinta data fito ahankali idanunta sunyi jaa kaman ba Hawwa ba tana gyadama Ni’ima kai gwanin ban tausayi tace “da Mamana na raye she would’ve helped me nai aure, Ni’ima nima nagaji” Ni’ima ta daure cus bataso itama tai kuka takai hannunta tana share mata hawaye, hannun Ni’ima Hawwa tarike ahankali cikin murya mai sanyi gaske tace “Ni’ima I’m tired of everything” ahankali Ni’ima tace “I know you are” ahankali Hawwa tace “I’m tired of yanda mahaifina, the society dana taso ciki and everyone around me suke pressuring dina into getting married, Ni’ima nadamu I don’t know ko inada wani bakin haline maisa naki auruwa? Maisa kona fara soyayya saurayi ke guduwa babu wani kwakkwaran dalili? They always come su bani hope and ran yanzu bamasa zuwa kaman anyi ruwa an dauke, maisa ko an fara maganan aure saisu gudu? Anzo gaban da ko saurayi daya banda shi yanzu, ba tsoho ba yaro ko me faskare baya shinshinata, bani bawa maza sha’awa, my sisters kannina dasuka tazo na kula dasu, na goyasu na chanza musu pampers sunyi aure, all my friends damukai aji daya dasu some nada 5kids ma, what is wrong with me? Ni’ima tell me the truth maisa nakeda bakin jini? Am I not beautiful enough asoni nima a aureni? İnada wani nakasu ne”? Ayanda take maganan kasan she’s seriously hurt maganganun su Baba da kowa ma duk sun sami waje sun zauna a zuciyanta, hannunta Ni’ima takai ta sharemata fuska tace “Hawwa, Best kinga listen to me, bakida bakin jini, there’s nothing wrong with you that I’m sure, it’s just time…okay, trust me it’s just time” sake fashewa da kuka Hawwa tayi she just had enough today from Baba, zuciyanta na mata zafi tace “time? I will be 30 in 2months time, when will the right time comes? Idan nakai 70yrs”? Sheshekan kuka tayi sosai cikin mugun raunin murya tace “Ni’ima inaso nai aure, nima inaso naga inada miji kaman kowace matan aure, nima akillace ni agida, I want to have my own husband someone I can call mine, wanda I will share my soul with, wanda will make sure I eat, I sleep, I’m happy wanda will look after me, someone I can share my happiness and sorrows with, someone that will hold hannuwana idan ina ciwo and watch me get better, Ni’ima I’m a woman too, just because I buried damuwata doesn’t mean banda shi, nagaji da gidan mahaifina I just want to leave naje gidan mijina, I’m so lonely Ni’ima I’m very very and very lonely, inason aure when will that time comes eh????” Ta kankame hannun Ni’ima tana kuka dayasa Ni’ima itama hawaye yafito daga idanunta tana kallon Hawwa bakinta na rawa irin na wanda ke shirin kuka sai kawai ta rungumeta tafara kuka sukahau kuka babu mai lallashin wani, tana kuka Ni’ima tace “life is not fair to you, you are the most beautiful yarinyar dana sani aduniya, the most intelligent, your heart is as pure and ruwan dake burtsatsowa daga cikin dutse, I’m so sorry Hawwa you are going through all this kinji, I’m so sorry don’t ever believe in maganan Baba kan kinyi kwantai bari na gayamiki all those mazan nan da suka gudu wlh sune sukai loosing precious gem, Hawwa you’re special and Allah ya ajiyeka for a special man ne only zaki gani, I will hold your hand, stay with you mujira the right man for my best friend together okay”.EPISODE Ringing da wayan Ni’ima yayi yasa ahankali Hawwa tasaketa tana share fuskanta sannan takai hannunta tana share fuskan Ni’ima tace “tashi kije Baban Yaseer is calling you” batai musu ba ta tashi tace “promise you will not cry again” murmushi Hawwa ta kakalo tamata tace “I won’t, wuce kije bari na shiga wanka nima” gyadamata kai tayi tace “muje tare to daganan saina fita” tashi tayi ta sauka daga gadon tarage kayan jikinta tadauki zani ta daura a kirji tadauki basket na sponge nata da sabulu suka fito tare, a pampo dake compound din ta tara ruwa sannan tawuce bayin tsakar gidan tana mata bye itakuma Ni’ima tawuce waje, sallama sukama Baba suka wuce bayan Baban Yaseer yamai kyautan kudade sai godiya yake, suka shiga mota yaja motan suka wuce kallo daya yamata yamaida kanshi kan tuki yace “why did you cry”? Kallonshi tayi saikuma tai shiru sake kallonta yayi ganin the way she’s worried yasa yamika hannunshi yakama nata yarike yadan matsa yace “wat is it my Baby”? Fashewa tayi da kuka tace “I’ve cracked my brain Sweedy countless times nakasa gane the exact reason Hawwa taki auruwa, babu mai aurenta sai su gudu, yanzu for like 2yrs batada saurayi ko guda daya, I don’t know mesa samarinta ke guduwa, though I know some na neman jikinta itakuma Hawwa will never settle for that kind of love but ai naga that’s a good thing kasan kamila zaka aura, mesa suke guduwa? Just why why whyyy?” Dan sauke ijiyan zuciya yayi yasake dan matsa hannunta ahankali yace “stop crying, Hawwa is a smart woman, I hope next time dazata hadu damai sonta she will make smart choice, come here” yadan karkato yana jawota kiss ya manna mata agoshi yace “stop crying banso yaranmu suganki ahaka, I love you” murmushi tamai tace “I love you too mijina” sakinta yayi ya gyara zamanshi yacigaba da tuki itakuma tadan juya tana kallon waje tace “I wish Hawwa tasami miji as romantic as you are Baban Yaseer” dan kallonta yayi saikuma ya daukekai yacigaba da tuki batare dayace komi ba, chan tace “abinda Baba yake is not nice, sai zaginta yake yana mata maganganu duk yan layi naji sai kace ba yarsa ba, ni wlh ma kaman bayasonta dana sanin haihuwanta yake” dan ijiyan zuciya Baban Yaseer yasauke tareda girgiza matakai hankalinshi nakan tuki yace “ku mata ne bazaku taba gane halin Baba ba” dasauri Ni’ima tace “kana ganin haka Babe?” Gyadamata kai yayi yace “Baba na son Hawwa sosai saisa damuwan nan tamai yawa, kullum lissafinsa da burinsa shine yanda zai aurar da ita, he feels responsible towards Hawwa sama da duka sauran yaran daya haifa sabida yasan ita marainiya ce, batada mahaifiya sauran yaransa na nada mahaifiya, da ace Maman su Aminu tadauki Hawwa as her own dukda abin yazoma Baba da sauki but bata taba accepting Hawwa ba, so shi kadai Hawwa kedashi, kina ganin da mahaifiyarta na nan da yanzu tayi wani abu akan zancen nan, uwa uwace and mothers can do extraordinary things to help yaransu, da tana rana da sai inda karfinta ya kare wajen nemawa yarta miji, part of abinda ke damun Baba also is fear, ya tsufa gashi baida kafa, baison yafadi yamutu bai aurar da Hawwa ba cus yana ganin zata iya zama haka har abada batai auren
Chapter 9 · 0% Book details